< 阿摩司书 1 >

1 当犹大王乌西雅,以色列王约阿施的儿子耶罗波安在位的时候,大地震前二年,提哥亚牧人中的阿摩司得默示论以色列。
Kalmomin Amos, ɗaya daga cikin makiyayan Tekowa, abubuwan da ya gani game da Isra’ila shekaru biyu kafin a yi girgizar ƙasa, a lokacin da Uzziya yake sarkin Yahuda, Yerobowam ɗan Yowash kuma yake sarkin Isra’ila.
2 他说:耶和华必从锡安吼叫, 从耶路撒冷发声; 牧人的草场要悲哀; 迦密的山顶要枯干。
Ya ce, “Ubangiji ya yi ruri daga Sihiyona ya kuma yi tsawa daga Urushalima; wuraren kiwo duk sun bushe, dutsen Karmel kuma ya yi yaushi.”
3 耶和华如此说: 大马士革三番四次地犯罪, 我必不免去她的刑罚; 因为她以打粮食的铁器打过基列。
Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Damaskus, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Domin sun ci zalunci Gileyad zalunci mai tsanani,
4 我却要降火在哈薛的家中, 烧灭便·哈达的宫殿。
zan sa wuta a gidan Hazayel, da za tă ƙona kagarun Ben-Hadad.
5 我必折断大马士革的门闩, 剪除亚文平原的居民和伯·伊甸掌权的。 亚兰人必被掳到吉珥。 这是耶和华说的。
Zan kakkarye ƙofofin Bet-Damaskus; zan hallaka sarkin da yake cikin Kwarin Awen da kuma mai riƙe da sandar mulkin Bet-Eden. Mutanen Aram za su je bauta a ƙasar Kir,” in ji Ubangiji.
6 耶和华如此说: 迦萨三番四次地犯罪, 我必不免去她的刑罚; 因为她掳掠众民交给以东。
Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Gaza, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Don sun kwashe al’umma gaba ɗaya sun sayar wa Edom,
7 我却要降火在迦萨的城内, 烧灭其中的宫殿。
Zan aika da wuta a katangar Gaza ta ƙone duk kagarunta.
8 我必剪除亚实突的居民和亚实基伦掌权的, 也必反手攻击以革伦。 非利士人所余剩的必都灭亡。 这是主耶和华说的。
Zan hallaka sarkin Ashdod da kuma mai riƙe da sandar mulki na Ashkelon. Zan hukunta Ekron, har sai dukan Filistiyawa sun mutu,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
9 耶和华如此说: 泰尔三番四次地犯罪, 我必不免去她的刑罚; 因为她将众民交给以东, 并不记念弟兄的盟约。
Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Taya, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Don sun kwashe al’umma gaba ɗaya sun kai su bauta a Edom, ba su kula da yarjejjeniyar da aka yi ta zama kamar’yan’uwa ba,
10 我却要降火在泰尔的城内, 烧灭其中的宫殿。
zan aika da wuta a Taya, da za tă ƙone kagarunta.”
11 耶和华如此说: 以东三番四次地犯罪, 我必不免去她的刑罚; 因为她拿刀追赶兄弟,毫无怜悯, 发怒撕裂,永怀忿怒。
Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Edom, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta shi ba. Don ya fafari ɗan’uwansa da takobi, babu tausayi, domin ya ci gaba da fusata bai yarda yă huce daga fushinsa ba.
12 我却要降火在提幔, 烧灭波斯拉的宫殿。
Zan aika wuta a Teman da za tă ƙone kagarun Bozra.”
13 耶和华如此说: 亚扪人三番四次地犯罪, 我必不免去他们的刑罚; 因为他们剖开基列的孕妇, 扩张自己的境界。
Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Ammon, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta shi ba. Don ya tsaga cikin matan Gileyad masu juna biyu don kawai yă ƙwace ƙasar.
14 我却要在争战呐喊的日子, 旋风狂暴的时候, 点火在拉巴的城内, 烧灭其中的宫殿。
Zan sa wuta a katangar Rabba da za tă ƙone kagarunta za a yi kururuwa a ranar yaƙi, faɗan kuwa zai yi rugugi kamar hadiri.
15 他们的王和首领必一同被掳去。 这是耶和华说的。
Sarkinta zai je bauta, shi da ma’aikatansa,” in ji Ubangiji.

< 阿摩司书 1 >