< 路加福音 1 >

1 德敖斐羅鈞座:
Mutane da yawa sun ɗau niyyar rubuta labarin abubuwan da aka cika a cikinmu,
2 關於在我們中間所完的事蹟,己有許多人,依照那些自始親眼見過,並為真道服役的人所傳給我們的,著手編成了記述,
kamar yadda muka karɓe su daga waɗanda tun farko shaidu ne da kuma masu hidimar bishara.
3 我也從頭仔細查訪的一切,遂立意按著次第給你寫出來,
Saboda haka, da yake ni da kaina na binciko kome a hankali daga farko, na ga ya yi kyau in rubuta maka labarin dalla-dalla, ya mafifici Tiyofilus,
4 為使你認清你所講授的道理,正確無誤。
don ka san tabbacin abubuwan da aka koyar da kai.
5 在猶太王黑落德的時候,阿彼雅班中有一位司祭名叫匝加利亞,他的妻子是出於亞郎的後代,名叫依撒伯爾。
A lokacin da Hiridus ne yake sarautar Yahudiya, an yi wani firist mai suna Zakariya, na sashin firistoci gidan Abiya. Matarsa Elizabet ma’yar zuriyar Haruna ce.
6 二人在天主前是義人,都照上主的一切誡命和禮規行事,無可指摘。
Dukansu biyu kuwa masu adalci ne a gaban Allah, suna kuma bin umarnan Ubangiji da farillansa duka da halin rashin zargi.
7 但是,他們沒有孩子,因為依撒伯爾素不生育,兩人又都上了年紀。
Sai dai ba su da’ya’ya, domin Elizabet bakararriya ce; kuma dukansu biyu sun tsufa.
8 正逢匝加利亞輪著他的班次,在天主前盡司祭的職務時,
Wata rana da lokacin aikin firistoci na sashen Zakariya na yin hidima ya kewayo, yana kuma cikin hidimarsa ta firist a gaban Allah,
9 按著司祭的常例,他抽中了籤,得進上主的聖所獻香。
sai aka zaɓe shi ta wurin ƙuri’a, bisa ga al’adar aikin firist, yă shiga haikalin Ubangiji yă ƙone turare.
10 獻香的時候,眾百姓都在在外面祈禱。
Da lokacin ƙone turare ya yi, duk taron masu sujada suna a waje suna addu’a.
11 有一位上主的天使顯現給他。
Sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, tsaye a dama da bagaden turare.
12 匝加利亞一見,驚惶失措,害怕起來;
Da Zakariya ya gan shi sai ya firgita, tsoro kuma ya kama shi.
13 但天使向他說:「匝加利亞,不要害怕! 因為你的祈禱己蒙應允,你的妻子依撒伯爾要給你生一個兒子,你要給他起名叫若翰。
Amma mala’ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya; an ji addu’arka. Matarka Elizabet za tă haifa maka ɗa, za ka kuma ba shi suna Yohanna.
14 你必要喜樂歡躍,許多人也要因他的誕生而喜樂,
Zai zama abin murna da farin ciki a gare ka, mutane da yawa kuwa za su yi murna don haihuwarsa,
15 因為他在上主面將是偉大的,淡酒濃酒他不喝,而且他在母胎中就要充滿聖神;
gama zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba kuwa zai taɓa shan ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba. Zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun haihuwa.
16 他要使許多以色列子民轉向上主,他們的天主;
Shi ne zai juye mutanen Isra’ila da yawa zuwa wurin Ubangiji Allahnsu.
17 他要以厄利亞的精神和能力,在祂在前面先行,為使父的心轉向兒子,使悖逆者轉向義人的心意,並為上主準備一個善良的百姓。」
Zai sha gaban Ubangiji, a ruhu da kuma iko irin na Iliya, domin yă juye zukatan iyaye ga’ya’yansu, marasa biyayya kuma ga zama masu biyayya don yă kintsa mutane su zama shiryayyu domin Ubangiji.”
18 匝加利亞遂向天主說:「我憑什麼能知道這事呢? 因為我已經老了,我的妻子也上了年紀。」
Sai Zakariya ya tambayi mala’ikan ya ce, “Yaya zan tabbatar da wannan? Ga ni tsoho, matana kuma ta kwana biyu.”
19 天使回答說:「我是站在天主在前面的加俾額爾,奉命來向你說話,報告給你這個喜訊。
Mala’ikan ya ce, “Ni ne Jibra’ilu. Ina tsaya a gaban Allah, an kuma aiko ni in yi maka magana, in kuma faɗa maka wannan labari mai daɗi.
20 看,你必成為啞吧,不能說話,宜到這事成就的那一天,因為你沒有相信我的話;但我的話屆時必要應驗。」
Yanzu za ka zama bebe, ba za ka ƙara iya magana ba sai ranar da wannan magana ta cika, saboda ba ka gaskata da kalmomina waɗanda za su zama gaskiya a daidai lokacinsu ba.”
21 百姓等候匝加利亞,都奇怪他滯留在聖所內。
Ana cikin haka, mutane suna jiran Zakariya, suna kuma mamaki me ya sa ya daɗe haka a cikin haikali.
22 及至他出來後,不能與他們講話,他們這才知道他在聖所中見了異象,他已成了啞吧,只給他們打手勢
Da ya fito, bai iya yin musu magana ba. Sai suka gane, ya ga wahayi ne a haikali, domin ya dinga yin musu alamu, amma ya kāsa yin magana.
23 他供職的日期一滿,就回了家。
Da lokacin hidimarsa ya cika, sai ya koma gida.
24 幾天以後,他的妻子依撒伯爾了孕,自己躲藏了五個月,說:
Bayan wannan, matarsa Elizabet ta yi ciki, ta kuma riƙa ɓuya har wata biyar.
25 「上主在眷顧的日子這樣待了我,除去了我在人間的恥辱。
Sai ta ce, “Ubangiji ne ya yi mini wannan. A waɗannan kwanaki ya nuna tagomashinsa ya kuma kawar mini da kunya a cikin mutane.”
26 到了第六個月,天使加俾額爾奉天主差遺,往加利肋亞一座名叫納匝肋的城去,
A wata na shida, sai Allah ya aiki mala’ika Jibra’ilu zuwa Nazaret, wani gari a Galili,
27 到一位童貞女那裡,她已與達味家族中一個名若瑟的男子訂了婚,童貞女的名叫瑪利亞。
gun wata budurwar da aka yi alkawarin aurenta ga wani mutum mai suna Yusuf daga zuriyar Dawuda. Sunan budurwar Maryamu.
28 天使進去向她說:「萬福! 充滿恩寵者,上主與妳同在! 」[在女人中妳是蒙祝福的。]
Mala’ikan ya je wurinta ya ce, “A gaishe ki, ya ke da kika sami tagomashi ƙwarai! Ubangiji yana tare da ke.”
29 她卻因這話驚惶不安,便思慮這樣的請安有什麼意思。
Maryamu ta damu ƙwarai da kalmominsa, tana tunani wace irin gaisuwa ce haka?
30 天使對她說:「瑪利亞,不要害怕,因為妳在天主在面前獲得了寵幸。
Amma mala’ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.
31 看,妳將懷孕生子,並要給祂起名叫耶穌。
Ga shi za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa, za ki kuma ba shi suna Yesu.
32 祂將是偉大的,並被稱為至高者的兒子,上主天主要把祂祖先達味的御座賜給祂。
Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi gadon sarautar kakansa Dawuda,
33 祂要為王統治雅各伯家,直到永遠;祂的王權沒有終結。」 (aiōn g165)
zai yi mulkin gidan Yaƙub har abada, mulkinsa kuma ba zai taɓa ƙare ba.” (aiōn g165)
34 瑪利亞便向天使說:「這事怎能成就? 因為我不認識男人。」
Maryamu ta tambayi mala’ikan ta ce, “Yaya wannan zai yiwu, da yake ni budurwa ce?”
35 天使答覆她說:「聖神要臨於妳,至高者的能要庇廕妳,因此,那要誕生的聖者,將稱為天主的兒子。
Mala’ikan ya amsa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki, ikon Maɗaukaki kuma zai rufe ke. Saboda haka, Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi Ɗan Allah.
36 且看,妳的親戚依撒伯爾,她雖在老年,卻懷了男胎,本月已六個月了,她原是素稱不生育的
’Yar’uwarki Elizabet ma za tă haifi ɗa a tsufanta, ita da aka ce bakararriya, ga shi tana a watanta na shida.
37 因為在天主前沒有不能的事。」
Gama ba abin da zai gagari Allah.”
38 瑪利亞說:「看,上主的婢女,願照你的話成就於我吧! 」天使便離開她去了。
Maryamu ta amsa ta ce, “To, ni baiwar Allah ce, bari yă zama mini kamar yadda ka faɗa.” Sai mala’ikan ya tafi abinsa.
39 瑪利亞就在那幾日動身,急速往山區去,到了猶太的一座城。
A lokacin sai Maryamu ta shirya ta gaggauta zuwa wani gari a ƙasar tudu ta Yahudiya,
40 她進了匝加利亞的家,就給依撒伯爾請安。
inda ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Elizabet.
41 依撒伯爾一聽到瑪利亞安,胎兒就在她腹中歡躍。依撒伯爾遂充滿聖神,
Da Elizabet ta ji gaisuwar Maryamu, sai jaririn da yake a cikinta ya yi motsi. Elizabet kuma ta cika da Ruhu Mai Tsarki.
42 大聲呼喊說:「在女人中妳是蒙祝福的,妳的胎兒也是蒙祝福的。
Sai ta ɗaga murya da ƙarfi ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata. Mai albarka ne kuma ɗan da za ki haifa!
43 吾主的母親駕臨我這裡,這是我裡得來的呢?
Me ya sa na sami wannan tagomashi har da mahaifiyar Ubangijina za tă zo wurina?
44 看,妳安的聲音一入我耳,胎兒就在我腹中歡喜跳躍。
Da jin gaisuwarki, sai jaririn da yake cikina ya yi motsi don murna.
45 那信了由上主傳於她的話必要完成的,是有福的。」
Mai albarka ce wadda ta gaskata cewa abin da Ubangiji ya faɗa mata zai cika!”
46 瑪利亞遂說:「我的靈魂頌揚上主,
Sai Maryamu ta ce, “Raina yana ɗaukaka Ubangiji
47 我的心神歡躍於天主,我的救主,
ruhuna kuma yana farin ciki da Allah Mai Cetona,
48 因為祂垂顧了祂婢女的卑微,今後萬世萬都要稱我有福;
gama ya lura da ƙasƙancin baiwarsa. Daga yanzu nan gaba dukan zamanai za su ce da ni mai albarka,
49 因全能者在我身上行了大事,祂的名字是聖的,
gama Mai Iko Duka ya yi mini manyan abubuwa, sunansa labudda Mai Tsarki ne.
50 祂的仁慈世世代代於無窮世,賜於敬畏祂的人。
Jinƙansa ya kai ga masu tsoronsa, daga zamani zuwa zamani.
51 祂伸出了手臂施展大能,驅散那心高氣傲的人。
Ya aikata manyan ayyuka da hannunsa; ya watsar da waɗanda suke masu girman kai a zurfin tunaninsu.
52 祂從高座上推下權勢者,卻舉揚了卑微貧困的人。
Ya saukar da masu mulki daga gadajen sarautarsu amma ya ɗaukaka ƙasƙantattu.
53 祂曾使飢餓者飽饗美物,反使那富有者空手而去。
Ya ƙosar da masu yunwa da kyawawan abubuwa amma ya sallami mawadata hannu wofi.
54 祂曾回憶起自己的仁慈,扶助了祂的僕人以色列,
Ya taimaki bawansa Isra’ila, yana tunawa yă nuna jinƙai
55 正如祂向我們的祖先所說過的思許,施思於亞巴郎和他的子孫,直到永遠。」 (aiōn g165)
ga Ibrahim da zuriyarsa har abada, kamar yadda ya faɗa wa kakanninmu.” (aiōn g165)
56 瑪利亞同依撒作爾住了三個月左右,就回本家去了。
Maryamu ta zauna da Elizabet kusan wata uku sa’an nan ta koma gida.
57 依撒伯爾滿了產期,就生了一個兒子。
Sa’ad da kwanaki suka yi don Elizabet ta haihu, sai ta haifi ɗa.
58 她的鄰居和親戚聽說上主向她大施仁慈,都和她一同歡樂。
Maƙwabtanta da’yan’uwanta suka ji cewa Ubangiji ya nuna mata jinƙai mai yawa, suka kuma taya ta farin ciki.
59 到了第八天,人們來給這孩子行割損禮,並願意照他父親的名字叫他匝加利亞。
A rana ta takwas, sai suka zo don a yi wa yaron kaciya, dā za su sa masa sunan mahaifinsa Zakariya ne,
60 他的母親說:「不,要叫他若翰。」
amma mahaifiyar yaron ta ce, “A’a! Za a ce da shi Yohanna.”
61 他們就向她說:「在妳親戚中沒有叫這個名子的。」
Sai suka ce mata, “Ba wani a cikin danginku mai wannan suna.”
62 他們便給祂的父親打手勢,看願意叫他什麼。
Sai suka yi alamu wa mahaifinsa, don su san sunan da zai su a kira yaron.
63 他要了一塊小板,寫道:「若翰是他的名字。」群人都驚訝起來。
Ya yi alama a kawo masa allo, a gaban kowa sai ya rubuta, “Sunansa Yohanna.” Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.
64 匝加利亞的口和舌頭立時開了,遂開口讚美天主。
Nan da nan bakinsa ya buɗe harshensa kuma ya saku, sai ya fara magana yana yabon Allah.
65 於是,所有的鄰居都滿懷怕情;這一切事就傳遍了全猶太山區,
Maƙwabta duk suka cika da tsoro, mutane kuwa suka yi ta yin magana game da dukan waɗannan abubuwa a ko’ina a cikin ƙasar tudu ta Yahudiya.
66 凡聽見的人都將這事存在人中,說:「這孩子將成為什麼人物啊? 」因為上主的手與他同在。
Duk waɗanda suka ji wannan kuwa sun yi mamaki suna cewa, “To, me yaron nan zai zama?” Gama hannun Ubangiji yana tare da shi.
67 他的父親匝加利亞充滿了聖神,遂預言說:
Mahaifinsa Zakariya ya cika da Ruhu Mai Tsarki sai ya yi annabci ya ce,
68 「上主,以色列的天主應受讚美,因祂眷顧救贖了自己的民族,
“Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin ya zo ya kuma fanshe mutanensa.
69 並在自己的僕人達味家中,為我們興起了大能的救主,
Ya tā mana ƙahon ceto a gidan bawansa Dawuda
70 正如祂藉歷代諸聖先知的口所說過的, (aiōn g165)
(yadda ya yi magana tun tuni ta wurin annabawansa masu tsarki), (aiōn g165)
71 拯救我們脫離敵人和仇恨我們者的手。
cewa zai cece mu daga abokan gābanmu daga kuma hannun dukan waɗanda suke ƙinmu
72 祂向我們的祖先施行仁慈,記憶祂自己的盟約,
don yă nuna jinƙai ga kakanninmu, yă kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
73 就是祂向我們的祖宗亞巴郎所宣述的誓詞,
rantsuwar da ya yi wa mahaifinmu Ibrahim,
74 恩賜我們從敵人手中被救出以後,無恐無懼,
don yă kuɓutar da mu daga hannun abokan gābanmu, yă kuma sa mu iya yin masa hidima babu tsoro,
75 一生一世在祂的在面前,以聖善和正義事奉祂。
cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakinmu.
76 至於你,小孩,你要稱為至高者的先知,因你要走在上主的在面前,為祂預備道路,
“Kai kuma, ɗana, za a ce da kai annabin Maɗaukaki; gama za ka sha gaban Ubangiji don ka shirya masa hanya,
77 為祂的百姓認識救恩,以獲得他們罪惡的寬宥:
don ka sanar da mutanensa ceto, ta wurin gafarar zunubansu,
78 這是出於我們天主的慈懷,使旭日向我們照耀,
saboda jinƙai na Allahnmu mai ƙauna, hasken nan na ceto zai ɓullo mana daga sama,
79 為光照那坐在黑暗和死影中的人,並引我們的腳步,走向和平的道路。」
don yă haskaka a kan waɗanda suke zama cikin duhu, da kuma cikin inuwar mutuwa, don yă bi da ƙafafunmu a hanyar salama.”
80 這小孩漸漸長大,心神堅強。他住在荒野中,直到他在以色列人前出現的日期。
Yaron kuwa ya yi girma ya kuma ƙarfafa a ruhu; ya zauna a hamada sai lokacin da ya fito a fili ga mutanen Isra’ila.

< 路加福音 1 >