< Luk 5 >

1 Hnin touh hnin vah Gennesaret talî teng Jisuh a kangdue navah tamihunaw ni Cathut e lawk thai hanelah Jisuh koevah a tho awh.
Wata rana, Yesu yana tsaye a bakin Tafkin Gennesaret, mutane kuma suna ta matsawa kewaye da shi, domin su ji maganar Allah,
2 Jisuh ni tuirai lah ka kâhat e long kahni touh a hmu. Tangakamankungnaw teh long dawk hoi a kum teh tamlawk a pâsu awh.
sai ya hangi jiragen ruwa biyu a bakin tafkin, waɗanda masu kamun kifi suka bari suna wankin abin kamun kifinsu.
3 Hote longnaw thung dawk e Simon e long thung a kâen teh, long tahruet haw telah atipouh. Hote long dawk a tahung teh, taminaw hah a cangkhai.
Sai ya shiga ɗaya jirgin ruwan da yake na Siman, ya kuma roƙe shi yă tura shi kaɗan daga gaci. Sai ya zauna a jirgin ruwan, ya koyar da mutane daga ciki.
4 A pâbaw hnukkhu vah, tui adungnae koe lah bout tahruet ei, tamlawk kadai nateh tanga heng ei telah Simon koe kâ a poe.
Da ya gama magana, sai ya ce wa Siman, “Ka tuƙa jirgin zuwa inda akwai zurfi, ka saukar da abin kamun kifinka ka kama kifi.”
5 Simon ni hai Bawipa kaimanaw ni karum tuettuet ka heng awh toe. Hatei, buet touh hai ka man awh hoeh. Hatei nang ni kâ na poe e patetlah ka heng han atipouh.
Siman ya amsa ya ce, “Ranka yă daɗe, duk dare mun yi ta fama ba mu kama kome ba, amma tun da ka ce haka, zan saki abin kamun kifin.”
6 A dei e patetlah a heng navah tanga moikapap a kâman teh tamlawk meimei a kâphi.
Da suka yi haka, sai suka kama kifi da yawa, har abin kamun kifinsu suka fara tsintsinkewa.
7 Alouke long dawk kaawm e a huikonaw kabawp hanelah a kaw. Huikonaw a tho awh teh long kahni touh dawk tanga a pâseng awh navah tanga teh yikkawi teh long teh tui dawk meimei a bo.
Sai suka kira abokansu a ɗaya jirgin, su zo su taimake su, suka kuwa zo. Suka cika jiragen biyu da kifi cif, har jiragen suka fara nutsewa.
8 Simon Piter ni a hmu navah, Jisuh e a khok koe a tabo teh, Bawipa kai teh tamikayon doeh, Kai na cettakhai leih atipouh.
Da Siman Bitrus ya ga wannan, sai ya fāɗi a gaban Yesu ya ce, “Rabu da ni, Ubangiji. Ni mai zunubi ne!”
9 Bangkongmaw telah a dei pouh tetpawiteh a man e tanganaw a khet navah a huikonaw Zebedee e capa Jem hoi Jawhan, Simon hoi kaawm e taminaw teh a kângairu awh.
Gama mamaki ya kama shi da abokansa duka, saboda yawan kifin da suka kama.
10 Jisuh ni taket awh hanh, nang teh atu hoi tami kamankung lah na coung sak han telah atipouh.
Yaƙub da Yohanna,’ya’yan Zebedi, abokan aikin Siman su ma suka yi mamaki. Sai Yesu ya ce wa Siman, “Kada ka ji tsoro, daga yanzu za ka riƙa kama mutane ne.”
11 A kongteng lah long a hruek awh hnukkhu, ahnimanaw ni a tawn awh e pueng koung a ceitakhai awh teh a hnuk a kâbang awh.
Sai suka jawo jiragen ruwansu zuwa gaci, suka bar kome da kome, suka bi shi.
12 Bawipa teh kho buet touh dawk ao navah a takbuem lah ka hrikbei e tami buet touh ni a hmu navah a tabo teh, Bawipa na panki pawiteh kai na thoungsak haw atipouh.
Yayinda Yesu yake ɗaya daga cikin garuruwan nan, sai ga wani mutum wanda kuturta ta ci ƙarfinsa. Da ganin Yesu, sai ya fāɗi da fuskarsa a ƙasa, ya roƙe shi ya ce, “Ubangiji, in ka yarda, kana iya ka tsabtacce ni.”
13 Jisuh nihai, kai ni na panki, thoung lawih atipouh. A kut a dâw teh hote tami teh a tek tahma vah tang a dam.
Yesu ya miƙa hannunsa ya taɓa mutumin ya ce, “Na yarda, ka zama da tsabta!” Nan da nan, sai kuturtar ta rabu da shi.
14 Jisuh ni hete kong api koehai dei hanh lah a atipouh. Vaihmanaw koe cet nateh kâpâtueh, hahoi na damnae hah lawkpanuesaknae lah ao nahan, Mosi e kâ poe e patetlah thuengnae hah poe haw, atipouh.
Sai Yesu ya umarce shi ya ce, “Kada ka gaya wa kowa, amma ka tafi ka nuna kanka ga firist, ka kuma miƙa hadayu da Musa ya umarta, saboda tsarkakewarka ta zama shaida a gare su.”
15 Hatei hote kamthang teh hoe a kamthang dawkvah tamihupui teh a lawk thai hane dawk hai thoseh, patawpanatnae dam han ngai dawk hai thoseh, a kamkhueng awh.
Duk da haka, labarinsa ya ƙara bazuwa sosai, har taron mutane suka dinga zuwa don jinsa, da kuma neman warkarwa daga cututtukansu.
16 Hatei Jisuh teh kahrawngum a cei teh a ratoum.
Amma Yesu sau da yawa, yakan keɓe kansa zuwa wuraren da ba kowa, yă yi addu’a.
17 Hnin touh hnin vah Jisuh ni cangkhainae a tawn navah, Jerusalem kho, Judah ram hoi Galilee ram dawk e kaawm e Farasinaw hoi cakathutkungnaw a tahung awh teh, patawnae dam sak hanelah Cathut e hnotithainae teh Jisuh dawk ao.
Wata rana, da yake cikin koyarwa, waɗansu Farisiyawa da malaman dokoki waɗanda suka zo daga kowane ƙauye a Galili, Yahudiya da Urushalima kuwa suna zaune. Ikon Ubangiji yana nan don yă warkar da masu ciwo.
18 Hatnavah a kutkhok kamkhuen e tami buet touh Jisuh koe a thokhai awh teh, aonae koe phakhai hanelah a panki awh.
Sai ga waɗansu mutane suka kawo wani shanyayye a kan tabarma. Suka yi ƙoƙari su shigar da shi cikin gidan, domin su kwantar da shi a gaban Yesu.
19 Hatei tami muen akawi teh kâen nahane lamthung a pâphawng awh hoeh dawkvah, Jisuh a onae tueng koe lemphu a rake awh teh phailei dawk hoi a pabo awh.
Da suka ga babu hanyar da za su bi saboda taron, sai suka haura rufin, suka saukar da shi a kan tabarmarsa, ta bakin ramin da suka huda a rufin, suka ajiye shi a tsakiyar taron, a gaban Yesu.
20 Jisuh ni hotnaw e a yuemnae a hmu navah, ka kamkhuen e tami hanlah, ka ca na yonnae teh ngaithoum lah o toe atipouh.
Da Yesu ya ga bangaskiyarsu, sai ya ce, “Saurayi, an gafarta maka zunubanka.”
21 Cakathutkungnaw hoi Farasinaw ni hat e tami ni bangkongmaw Cathut pathoenae lawk a dei. Cathut hloilah apimaw yon ka ngaithoum thai telah a lungthung hoi ati awh.
Farisiyawa da malaman dokoki suka fara yin tunani a zukatansu, “Wane ne wannan mutum da yake saɓo haka? Wa zai iya gafarta zunubai, in ba Allah kaɗai ba?”
22 Jisuh ni ahnimae lungthin thung a pouknae a panue dawkvah bangkongmaw telah na pouk awh.
Yesu ya san abin da suke tunani, sai ya yi tambaya ya ce, “Don me kuke tunanin waɗannan abubuwa a zukatanku?
23 Bang lawk maw dei ka yawihnawn, na yon ngaithoum lah ao toe tie maw dei kayawi, thaw nateh cet leih tie maw ka yawihnawn.
Wanne ya fi sauƙi, a ce, ‘An gafarta maka zunubanka,’ ko kuma a ce, ‘Tashi, ka yi tafiya’?
24 Tami Capa teh talai van dawk yon ngaithoum thainae kâ a tawn tie a panue thai awh nahan thaw leih, phailei kalawng nateh, nama im cet leih telah ka kamkhuen e koe a dei pouh.
Amma domin ku san cewa Ɗan Mutum yana da iko a duniya ya gafarta zunubai.” Sai ya ce wa shanyayyen, “Na ce maka, tashi, ɗauki tabarmarka ka tafi gida.”
25 Hote tami ni hai taminaw pueng e hmalah tang a thaw teh, amae phailei a kalawng teh Cathut pholen laihoi ama im vah a cei.
Nan da nan, ya tashi tsaye a gabansu, ya ɗauki tabarmar da yake kwance a kai, ya tafi gida, yana yabon Allah.
26 Tami pueng a kângairu awh teh, maimanaw ni kângairunae atu hmu awh toe telah a dei awh teh Cathut a pholen awh.
Kowa ya yi mamaki, ya kuma yabi Allah. Suka cika da tsoro, suna cewa, “Mun ga abubuwan banmamaki yau.”
27 Hathnukkhu hoi Jisuh teh a cei navah tamuk ka cawng e Levih, im dawk ka tahung e a hmu navah ka hnukkâbang atipouh.
Bayan wannan, sai Yesu ya fita, ya ga wani mai karɓar haraji, mai suna Lawi, yana zaune a wurin da ake karɓar haraji. Yesu ya ce masa, “Bi ni.”
28 Hote tami hai a tawn e naw pueng a ceitakhai teh a hnuk a kâbang.
Sai Lawi ya tashi, ya bar kome da kome, ya bi shi.
29 Hot hnukkhu hoi, Levih ni Jisuh hanelah ama im dawk pawi kalenpoung a sak teh, tamuk kacawngnaw hoi alouke a hnukkâbangnaw teh cungtalah bu rei a ca awh.
Sai Lawi ya shirya wa Yesu wani babban liyafa a gidansa. Wani babban taron na masu karɓar haraji, tare da waɗansu suna cin abinci tare da su.
30 Cakathutkungnaw hoi Farasinaw ni bangkongmaw tamuk ka cawng, tami kahawihoehnaw hoi bu rei a canei awh vaw telah a hnukkâbangnaw koe a phuenang awh.
Amma Farisiyawa da malaman dokokin da suke a ƙungiyarsu, suka yi wa almajiransa gunaguni, suna cewa, “Don me kuke ci, kuke sha tare da masu karɓar haraji da masu zunubi?”
31 Jisuh nihai, a tak kadamnaw ni tâsibawi panki hoeh, kadamhoehnaw ni dueng doeh tâsibawi a panki awh.
Yesu ya amsa musu ya ce, “Ai, masu lafiya ba sa bukatar likita, sai dai marasa lafiya.
32 Tamikalannaw kaw hanelah ka tho hoeh, tamikayonnaw pankângai hanelah doeh ka tho atipouh.
Ban zo don in kira masu adalci ba, sai dai masu zunubi zuwa ga tuba.”
33 Tami tangawn ni Jawhan hnukkâbangnaw hoi Farasinaw teh, rawca a hai awh teh pou ratoum awh hoeh maw. Bangkongmaw Bawipa nange na hnukkâbangnaw teh rawca a hai awh hoeh vaw, telah a pacei awh.
Suka ce masa, “Almajiran Yohanna sukan yi azumi da addu’a, haka ma almajiran Farisiyawa, amma naka sai ci da sha.”
34 Jisuh ni yu kalatkung teh a huikonaw hoi cungtalah ao navah rawca ouk a hai boimaw.
Yesu ya amsa ya ce, “Za ku iya sa abokan ango yin azumi yayinda yake tare da su?
35 Hatei yu kalatkung teh a huikonaw hoi kapek teh lanae tueng ka phat han. Hat torei teh, ahnimanaw hai rawca a hai awh van han.
Amma lokaci yana zuwa, da za a ɗauke ango daga gare su. A waɗancan kwanakin ne za su yi azumi.”
36 Bangnuenae lahoi a dei pouh e teh, angki ka pawn e hah lukkarei katha e hoi bo boihoeh. Hottelah bo pawiteh lukkarei katha e ni kapawn e hoehoe a kâphi sak han.
Sai ya faɗa musu wannan misali ya ce, “Ba wanda yakan yage ƙyalle daga sabuwar riga ya yi wa tsohuwar riga faci. In ya yi haka, zai yage sabuwar rigar, kuma facin daga sabuwar ba zai dace da tsohuwar rigar ba.
37 Hot patetvanlah, misurtui katha e hah karuem e phaivuen um dawk hlun boihoeh. Hottelah hlun pawiteh misurtui katha e ni phaivuen um karuem e hah tangpawk sak vaiteh atui hoi a um a rawk han.
Kuma ba wanda yakan zuba sabon ruwan inabi a cikin tsofaffin salkuna. In ya yi haka, sabon ruwan inabi zai farfashe salkunan, ruwan inabin yă zube, salkunan kuma su lalace.
38 Misurtui katha e teh phaivuen um katha dawk hlun pawiteh kahni touh hoi a cuem han.
A’a, sai dai a zuba sabon ruwan inabi a sababbin salkuna.
39 Karuem e misurtui ka net tangcoung e tami teh a katha e misurtui tang net ngai hoeh, a karuem e misurtui hoe atui e a panue dawkvah, telah atipouh.
Kuma ba wanda yakan so shan sabon ruwan inabi bayan ya sha tsohon, don yakan ce, ‘Ai, tsohon ya fi kyau.’”

< Luk 5 >