< Isaiah 19 >

1 Egypt kah olrhuh, BOEIPA tah khomai dongah yanghoep la ngol tih Egypt la pawk. A mikhmuh ah Egypt mueirhol rhoek te hlinghlawk tih Egypt rhoek kah a thinko tah a khui ah paci coeng.
Abin da Allah ya faɗa game da Masar, Duba, Ubangiji yana a kan girgije a sukwane yana kuwa zuwa Masar. Gumakan Masar sun firgita a gabansa, zukatan Masarawa sun karai.
2 Egypt te Egypt neh ka et thil vetih hlang long he a manuca khaw, hlang pakhat loh a hui khaw, khopuei neh khopuei khaw, ram pakhat ram pakhat a vathoh thil ni.
“Zan tā da hargitsi tsakanin mutumin Masar da mutumin Masar, ɗan’uwa zai yi gāba da ɗan’uwa maƙwabci ya yi gāba da maƙwabci, birni ya yi gāba da birni, mulki ya yi gāba da mulki.
3 Egypt kah a mueihla tah a khui ah hoep vetih a cilsuep ka hmaang sak ni. Te vaengah te mueirhol taengla, lung aka khueh, rhaitonghma neh hnam taengla a dawt uh bitni.
Masarawa za su karai, zan kuma sa shirye-shiryensu su zama banza; za su nemi shawarar gumaka da kuma ruhohin matattu, za su nemi shawarar mabiya da na masu duba.
4 Egypt te mangkhak boei rhoek kut ah ka det vetih amih te manghai aka tlung loh a ngol thil ni. Caempuei Yahovah Boeipa kah olphong coeng ni.
Zan ba da Masarawa ga ikon azzalumi shugaba, mugun sarki kuma zai yi mulki a kansu,” in ji mai girma, Ubangiji Maɗaukaki.
5 Tuipuei tui khaw kak ni. Tuiva khaw rhaeng vetih haang ni.
Ruwayen kogi za su ƙafe, bakin kogi zai shanye yă kuma bushe.
6 Tuiva te khaw pam vetih bawn ni. Egypt capu sokko te kak vetih carhaek khaw tloih ni.
Wuriyoyi za su yi wari; rafuffukan Masar za su yi ta raguwa har su ƙafe. Iwa da jema za su bushe,
7 Sokko neh sokko hmoi kah sulhing neh sokko mutue boeih khaw rhae ni. Cuhu vetih om voel mahpawh.
haka ma tsire-tsire kusa da Nilu, a bakin kogi. Kowane abin da aka shuka a gefen Nilu zai bushe, iska ta kwashe su ƙaf.
8 Tuihoi rhoek te huei uh vetih sokko ah vaih aka voei, lawk aka thing rhoek khaw boeih nguekcoi uh vetih tui soah tahah uh ni.
Masu kamun kifi za su yi nishi su kuma yi makoki, dukan waɗanda suke jefan ƙugiyoyi a Nilu; waɗanda suke jefan abin kamun kifi a ruwa abin kamun kifin za su zama marasa amfani.
9 Hlamik a yawt neh aka thotat tih, hlabok aka tak rhoek khaw yak uh ni.
Waɗanda suke aiki da kaɗin auduga za su karai, masu yin lilin mai kyau za su fid da zuciya.
10 A rhungsut te tlawt vetih, kutphu la aka saii boeih khaw a hinglu ngat ni.
Masu aikin tufafi ransu zai ɓace, kuma dukan masu samun albashi za su damu.
11 Zoan mangpa rhoek khaw ang uh tangkik coeng tih Pharaoh kah olrhoep hlangcueih rhoek kah cilsuep khaw a dom coeng. Pharaoh te metlamlae, “Kamah tah hlamat kah manghai koca khuiah khaw ka cueih ca,” na ti eh?
Shugabannin Zowan ba kome ba ne, wawaye ke kawai; mashawarta masu hikima na Fir’auna suna ba da shawarwari marasa amfani. Yaya za ka ce wa Fir’auna, “Ni ɗaya ne cikin masu hikima, almajirin sarakuna na dā can”?
12 Nang kah hlangcueih rhoek te maelae me? Nang taengah ha puen uh laeh vetih caemgpuei Yahovah loh Egypt a caai thil te a ming uh laeh mako.
Ina masu hikima suke yanzu? Bari su nuna maka su kuma sanar da abin da Ubangiji Maɗaukaki ya shirya a kan Masar.
13 Zoan mangpa rhoek te nga uh tih Noph mangpa rhoek khaw rhaithi uh thae. Egypt nim te amah koca rhoek te a cong cong ah kho a hmang uh coeng.
Shugabannin Zowan sun zama wawaye, an ruɗe shugabannin Memfis dutsen kan kusurwa na mutanenta su sa Masar ta kauce.
14 BOEIPA loh a khui ah lungbuei lukil hnaven neh a thoek tih kho a hmang uh coeng. Egypt loh amah khoboe cungkuem dongah khohmang bangla a lok neh rhui uh.
Ubangiji ya sa zuba musu ruhun jiri; suka sa Masar ta yi tangaɗi cikin kome da take yi, kamar yadda mutumin da ya bugu yake tangaɗi cikin amansa.
15 A lu neh a mai khaw, rhophoe neh canghlong khaw Egypt ham bitat aka saii thai te a om moenih.
Babu abin da Masar za tă yi, kai ko wutsiya, reshen dabino ko iwa.
16 Tekah khohnin ah tah Egypt khaw huta bangla om vetih lakueng ni. Te vaengah anih a thueng thil caempuei BOEIPA kah kut thueng hmai ah birhih pueng ni.
A wannan rana Masarawa za su zama kamar mata. Za su yi rawar jiki lokacin da Ubangiji Maɗaukaki ya ɗaga hannu a kansu.
17 Judah khohmuen te Egypt taengah birhihkuihut la om ni. Anih a phoei carhui te khaw a taengah birhih ni. caempuei BOEIPA kah cilsuep loh anih a uen coeng.
Ƙasar Yahuda kuma za kawo fargaba ga Masarawa; kowanne da Yahuda ya ambace zai firgita, saboda abin da Ubangiji Maɗaukaki yake shiri a kansu.
18 Tekah khohnin ah Egypt kho ah Kanaan ol la aka cal khopuei panga om ni. Te vaengah caempuei BOEIPA taengla ol aka caeng khopuei pakhat te tah koengloengnah khopuei a ti ni.
A wannan rana birane biyar a Masar za su yi yaren Kan’ana su kuma miƙa kai cikin yarjejjeniya ga Ubangiji Maɗaukaki. Za a ce da ɗayansu Birnin Hallaka.
19 Tekah khohnin ah Yahovah kah hmueihtuk te Egypt khohmuen kah a laklung ah, a khorhi ah Yahovah kah kaam om ni.
A wannan rana za a kasance da bagade ga Ubangiji a tsakiyar Masar, da kuma ginshiƙin dutse Ubangiji a iyakarta.
20 Egypt khohmuen ah caempuei BOEIPA kah miknoek neh laipai la om ni. Aka nen kah mikhmuh ah BOEIPA taengla a pang uh vaengah amih aka khang tih aka tungaep ham te a tueih pah vetih amih te a huul ni.
Zai zama alama da kuma shaida ga Ubangiji Maɗaukaki a ƙasar Masar. Sa’ad da suka yi kuka ga Ubangiji saboda masu zaluntarsu, zai aiko musu mai ceto da mai kāriya, zai kuma cece su.
21 BOEIPA loh Egypt te a tukkil vetih Egypt loh BOEIPA te a ming uh ni. Te khohnin ah hmueih neh khocang neh tho a thuenguh. Te vaengah BOEIPA taengah olcaeng neh a caeng uh vetih a thuung uh ni.
Saboda haka Ubangiji zai sanar da kansa ga Masarawa, kuma a wannan rana za su yarda da Ubangiji. Za su yi masa sujada da hadayu da hadayun hatsi; za su yi alkawura ga Ubangiji su kuma kiyaye su.
22 BOEIPA loh Egypt te a yawk sak ni. A yawk sak tih a hoeih daengah ni BOEIPA taengla a mael uh eh. Amih a thangthui uh vaengah amih te a hoeih sak ni.
Ubangiji zai bugi Masar da annoba; zai buge su ya kuma warkar da su. Za su juyo wurin Ubangiji, zai amsa roƙonsu ya kuma warkar da su.
23 Te khohnin ah Egypt lamloh Assyria duela longpuei om. Assyria te Egypt la, Egypt khaw Assyria la cet ni. Egypt neh Assyria loh tho a thueng ni.
A wannan rana za a kasance da babban hanya daga Masar zuwa Assuriya. Assuriyawa za su tafi Masar, Masarawa kuma za su tafi Assuriya. Masarawa da Assuriyawa za su yi sujada tare.
24 Te khohnin ah Israel te a pathum la Egypt neh Assyria taengah diklai laklung kah yoethennah neh om van ni.
A wannan rana Isra’ila za tă zama na uku, tare da Masar da Assuriya, abin albarka ga duniya.
25 Anih te caempuei BOEIPA loh a uem vetih, “Ka pilnam Egypt neh ka kut saii Assyria khaw, ka rho Israel khaw a yoethen,” a ti ni.
Ubangiji Maɗaukaki zai albarkace su, yana cewa, “Albarka ta tabbata ga Masar, mutanena, Assuriya aikin hannuna, da kuma Isra’ila gādona.”

< Isaiah 19 >