< San Marcos 1 >

1 TUTUJON y ibangelion Jesucristo, Lajin Yuus.
Farkon bishara game da Yesu Kiristi, Ɗan Allah.
2 Jaftaemano esta matugue gui profeta Isaias: Estagüe, guajo tumago y tentagojo gui menan matamo, para ufamauleg y chalanmo gui menamo.
An rubuta a cikin littafin annabi Ishaya cewa, “Zan aika da ɗan aikena yă sha gabanka, wanda zai shirya hanyarka,”
3 Ynagang ni umaagang gui desierto: Fanmauleg y chalan y Señot: natunas y cayejonña.
“muryar mai kira a hamada tana cewa, ‘Ku shirya wa Ubangiji hanya, ku miƙe hanyoyi dominsa.’”
4 Si Juan managpange gui desierto, ya jasetmon y tinagpangen minañotsot para inasiin isao sija.
Ta haka Yohanna ya zo, yana baftisma a yankin hamada, yana kuma wa’azin baftismar tuba don gafarar zunubai.
5 Ya manjanao guiya güiya guato todo y tano Judea, yan todo sija guiya Jerusalem; ya todo sija mantinagpange gui sadog Jordan, ya jaconfesatñaejon y isaoñija.
Dukan ƙauyukan Yahudiya da dukan mutanen Urushalima suka fiffito zuwa wurinsa. Suna furta zunubansu, ya kuwa yi musu baftisma a Kogin Urdun.
6 Ya si Juan minagagon pulon cameyo, yan sinturon cuero gui senturaña; ya y naña, apacha yan miet monte.
Yohanna ya sa tufafin gashin raƙumi, ya kuma yi ɗamara da fata. Abincinsa fāri ne da kuma zumar jeji.
7 Ya mansesetmon, ilegña: Ufato gui tateco uno na masgaeninasiña qui guajo, y coreas y sapatosña, ti digno yo nu jutecon ya jupula.
Wannan kuwa shi ne saƙonsa, “A bayana, wanda ya fi ni iko yana zuwa, ban kuwa isa in sunkuya in kunce igiyar takalmansa ba.
8 Guajo magajet na jutagpange jamyo yan janom; lao güiya infantinagpange ni Espiritu Santo.
Ina muku baftisma da ruwa, amma shi zai yi muku baftisma da Ruhu Mai Tsarki.”
9 Ya susede ayo sija na jaane, na si Jesus mato guine Nasaret Galilea, ya tinagpange as Juan gui Jordan.
A lokacin, Yesu ya zo daga Nazaret na Galili, Yohanna kuwa ya yi masa baftisma a Urdun.
10 Ya enseguidas nae cajulo gui janom, jalie na mababa y langet, ya y Espiritu, calang paluma tumunog gui jiloña,
Da Yesu yana fitowa daga ruwan, sai ya ga sama ya buɗe, Ruhu kuma yana saukowa a kansa kamar kurciya.
11 Ya mato un inagang guine y langet na ilegña: Jago y lajijo ni yajo, iya jago nae gosmagof yo.
Sai murya ta fito daga sama ta ce, “Kai ne Ɗana, wanda nake ƙauna, da kai kuma nake fari ciki ƙwarai.”
12 Ya enseguidas ninafalag y desierto ni Espiritu.
Nan da nan, sai Ruhu ya kai shi cikin hamada,
13 Ya sumaga güije cuarenta na jaane, ya tinienta as Satanas; yan mañisija y manmachaleg na gâgâ sija; ya y angjet sija masetbe güe.
ya kuma kasance a hamada kwana arba’in, Shaiɗan yana gwada shi. Yana tare da namomin jeji, mala’iku kuma suka yi masa hidima.
14 Anae munjayan si Juan mapreso, mato si Jesus guiya Galilea, jasesetmon y ibangelion Yuus.
Bayan da aka sa Yohanna a kurkuku, sai Yesu ya shigo cikin Galili, yana shelar bisharar Allah.
15 Ya ilegña: Y tiempo esta macumple; ya y raenon Yuus esta jijot: fanmañotsot, ya injenggue y ibangelio.
Yana cewa, “Lokaci ya yi. Mulkin Allah ya yi kusa. Ku tuba, ku gaskata bishara!”
16 Ya mamomocat gui oriyan tasen Galilea, jalie si Simon, yan si Andres chelun Simon, na jayuyute y lagua gui tase, sa sija manpescadot.
Yayinda Yesu yake tafiya a gaɓar Tekun Galili, sai ya ga Siman da ɗan’uwansa Andarawus, suna jefa abin kamun kifi a cikin tafkin, domin su masunta ne.
17 Ya si Jesus ilegña nu sija: Maela dalalagyo, ya junafanpescadot taotao jamyo.
Yesu ya ce, “Ku zo, ku bi ni, ni kuwa zan mai da ku masuntan mutane.”
18 Enseguidas japolo y laguañija ya madalalag güe.
Nan da nan, suka bar abin kamun kifinsu, suka bi shi.
19 Anae malofan talo didide mona, jalie si Santiago, lajin Sebedeo, yan si Juan cheluña, na manestaba locue gui batco na jalememenda y laguañija.
Da ya yi gaba kaɗan, sai ya ga Yaƙub ɗan Zebedi, da ɗan’uwansa Yohanna a cikin jirgin ruwa, suna gyaran abin kamun kifinsu.
20 Ya enseguidas jaagang; ya jadingo si tatanñija as Sebedeo gui batco yan y manmachocho sija, ya madalalag güe.
Ba da ɓata lokaci ba, ya kira su, sai suka bar mahaifinsu Zebedi a cikin jirgin ruwan, tare da’yan haya, suka kuwa bi shi.
21 Ya manjalom Capernaum; ya enseguidas, gui sábado na jaane, jumalom gui sinagoga ya mamanagüe.
Suka tafi Kafarnahum. Da ranar Asabbaci ta kewayo, sai Yesu ya shiga majami’a ya fara koyarwa.
22 Ya sija ninafanmanman ni finanagüeña; sa jafananagüe sija calang uno ni gaeninasiña, ya ti calang y escriba sija.
Mutane suka yi mamakin koyarwarsa, domin ya koyar da su kamar wanda yake da iko, ba kamar malaman dokoki ba.
23 Ya enseguidas guaja güije gui sinagogañija un taotao na guaja áplacha na espiritu, ya güiya umagang,
Nan take, sai wani mutum mai mugun ruhu a majami’arsu, ya ɗaga murya ya ce,
24 Ylegña: Parajafa jam nu jago, Jesus taotao Nasaret? Matojao para unnafanaelayejam? Jutungoja jayejao, jago y Santos guine as Yuus.
“Ina ruwanka da mu, Yesu Banazare? Ka zo ne don ka hallaka mu? Na san wane ne kai, Mai Tsarki nan na Allah!”
25 Ya si Jesus jalalatde ilegña: Pacaca, ya maela juyong guiya güiya.
Yesu ya tsawata masa ya ce, “Yi shiru! Fita daga cikinsa!”
26 Ya anae y áplacha na espiritu tiniteg güe, ya ninaagang gosdangculo na inagang, jumuyong guiya güiya.
Sai mugun ruhun ya jijjiga mutumin da ƙarfi, ya fita daga jikinsa da ihu.
27 Ya todo sija ninafanmanman, pot este manafaesen entre sija, ilegñija: Jafa este? Jafa na nuebo finanagüe este! yan ninasiña jatago y manáplacha na espiritu, ya maosgueja güe?
Dukan mutane suka yi mamaki, suna tambayar juna suna cewa, “Mene ne haka? Tabɗi! Yau ga sabuwar koyarwa kuma da iko! Yana ma ba wa mugayen ruhohi umarni, suna kuma yin masa biyayya.”
28 Enseguidas y famaña manamamta todo gui tano oriyan Galilea.
Labari game da shi ya bazu nan da nan ko’ina a dukan yankin Galili.
29 Ya enseguidas anae jumuyong gui sinagoga, mato gui guima Simon yan si Andres, yan si Santiago yan si Juan.
Da suka bar majami’ar, sai suka tafi gidan su Siman da Andarawus, tare da Yaƙub da Yohanna.
30 Ya y suegran Simon estaba na umaason sa malango yan calentura: ya masangane güe enseguidas nu y palaoan.
Surukar Siman tana kwance da zazzaɓi, sai suka gaya wa Yesu game da ita.
31 Ayo nae mato güe, ya jamantiene canaeña, ya jajatsa julo; ya pinelo ni calentura, ya güiya sumetbe sija.
Sai ya je wajenta, ya kama hannunta, ya ɗaga ta. Zazzaɓin kuwa ya sāke ta, ta kuma yi musu hidima.
32 Ya anae estaba esta pupuenge, anae machom y atdao, maconiigüe todo ni manmañetnot yan y maninanite.
A wannan yamma, bayan fāɗuwar rana, mutane suka kawo wa Yesu dukan marasa lafiya, da masu aljanu.
33 Ya todo y siuda mandaña gui petta.
Duk garin ya taru a ƙofar gidan.
34 Ya janafanjomlo megae ni manestaba manmalango todo clasen chetnot sija; ya jayute juyong megae na anite sija; ya ti japolo nu y anite sija cumuentos sa matungo güe.
Yesu kuwa ya warkar da marasa lafiya da yawa da suke da cututtuka iri-iri. Ya kuma fitar da aljanu da yawa, amma bai yarda aljanun suka yi magana ba, don sun san wane ne shi.
35 Ya y egaan güije, cajulo gostaftaf, jojomjomja trabia, ya jumuyong, ya malag y un lugat desierto, ya manaetae güije.
Da sassafe, tun da sauran duhu, Yesu ya tashi, ya bar gida, ya tafi wani wurin da ba kowa, a can ya yi addu’a.
36 Ya tinatiye güe as Simon, yan y mangachochongña.
Siman da abokansa suka fita nemansa.
37 Ya anae masoda güe, ilegñija nu güiya: Todo umaliligaojao.
Da suka same shi, sai suka ce, “Kowa yana nemanka!”
38 Güiya ilegña nu sija: Nije tafanmalag y otro lugat gui sengsong ni jijot, ya jufansetmon locue güije; sa pot este na matoyo.
Yesu ya amsa ya ce, “Mu je wani wuri dabam, zuwa ƙauyukan da suke kusa, don in yi wa’azi a can ma. Wannan shi ne dalilin zuwana.”
39 Ya jumalom gui sinagogañija todo Galilea, sesetmon ya jayuyute juyong y anite sija.
Sai ya tafi ko’ina a Galili, yana wa’azi a majami’unsu, yana kuma fitar da aljanu.
40 Ya un ategtog mato guiya güiya, tinayuyut güi ya dumimo, ya ilegña: Yaguin malagojao, siña unnagasgasyo.
Wani mutum mai kuturta ya zo wurinsa, ya durƙusa ya roƙe shi ya ce, “In kana so, za ka iya tsabtacce ni.”
41 Ya si Jesus ninamaase ya jaestira y canaeña, ya japacha, ya ilegña: Malagoyo, ungasgas.
Cike da tausayi, sai Yesu ya miƙa hannunsa ya taɓa mutumin ya ce, “Na yarda, ka tsabtacce!”
42 Ya enseguidas y chetnot y ategtog mapos guiya güiya ya gasgas güe.
Nan da nan, sai kuturtar ta rabu da shi, ya kuma warke.
43 Ya jagosencatga, ya jatago na ujanao,
Yesu ya sallame shi nan take, da gargaɗi mai ƙarfi cewa,
44 Ya ilegña nu güiya: Atan ya chamo sumangangane ni jaye jafa; lao sigueja gui jinanaomo ya unfanue y pale nu jago, ya unofrese ni guinasgasmo ni si Moises manago, para testimonioñija.
“Ka lura kada ka gaya wa kowa wannan. Amma ka tafi ka nuna kanka ga firist, ka kuma miƙa hadayun da Musa ya umarta saboda tsarkakewarka, don yă zama shaida gare su.”
45 Lao güiya mapos, ya jatutujon munamatungo, yan janagosmamta y checho; pot este, si Jesus ti siña jumalom matungo nu güiya gui siuda; lao sumasagaja gui sumanjiyong gui lugat desierto sija, ya manmato guiya güiya guinin todo y patte sija.
A maimakon haka, sai ya fita, ya fara magana a sake, yana baza labarin. Saboda haka, Yesu bai ƙara iya shiga cikin gari a fili ba, sai dai ya kasance a wuraren da ba kowa. Duk da haka, mutane suka yi ta zuwa wurinsa daga ko’ina.

< San Marcos 1 >