< San Lucas 1 >

1 POT y guaja megae y umapolo y canaeñija para ufannaregla y cuentos nu y ayo na güinaja na esta guefmaasegura gui entalo jame,
Mutane da yawa sun ɗau niyyar rubuta labarin abubuwan da aka cika a cikinmu,
2 Jaftaemanoja ninaejam ni guine y tutujoña y testigojam ni y malie, nu y yan y ministrojam y sinangan;
kamar yadda muka karɓe su daga waɗanda tun farko shaidu ne da kuma masu hidimar bishara.
3 Y jinasoco mauleg locue nu guajo, sa juguefegaga sinengcabales todo y güinaja guine y tutujonña, na jutuguie jao pot y inaregla, jago guesmagas na Teofilo;
Saboda haka, da yake ni da kaina na binciko kome a hankali daga farko, na ga ya yi kyau in rubuta maka labarin dalla-dalla, ya mafifici Tiyofilus,
4 Para untungo sija y magajet ayosija mano nae unresibe y finanagüe.
don ka san tabbacin abubuwan da aka koyar da kai.
5 Guaja gui jaanin Herodes, ray guiya Judea, un pale, naanña si Sacharias, y clasen Abias; y asaguaña guinin sija jagan Aaron ya y naaña si Elisabet.
A lokacin da Hiridus ne yake sarautar Yahudiya, an yi wani firist mai suna Zakariya, na sashin firistoci gidan Abiya. Matarsa Elizabet ma’yar zuriyar Haruna ce.
6 Este na dos mauleg gui sanmenan Yuus, jajananao gui todo y lay yan y tinago Señot, ti lalatdiyon.
Dukansu biyu kuwa masu adalci ne a gaban Allah, suna kuma bin umarnan Ubangiji da farillansa duka da halin rashin zargi.
7 Ya taya patgonñija; sa si Elisabet tifáfañago; yan y dos megae jaaniñija.
Sai dai ba su da’ya’ya, domin Elizabet bakararriya ce; kuma dukansu biyu sun tsufa.
8 Ya jumuyong, anae mañeñetbe si Sacharias, gui ofisio y pale gui menan Yuus, gui chechon y clasiña,
Wata rana da lokacin aikin firistoci na sashen Zakariya na yin hidima ya kewayo, yana kuma cikin hidimarsa ta firist a gaban Allah,
9 Jaftaemanoja y costumbren y ofisio y pale, y chechoña na jumalom gui guimayuus ya jasonggue y paopao.
sai aka zaɓe shi ta wurin ƙuri’a, bisa ga al’adar aikin firist, yă shiga haikalin Ubangiji yă ƙone turare.
10 Ya todo y linajyan taotao mangaegue gui sanjiyong manmananaetae gui oran paopao.
Da lokacin ƙone turare ya yi, duk taron masu sujada suna a waje suna addu’a.
11 Ya mato guiya güiya y angjet y Señot, na gaegue gui agapa y attat y paopao.
Sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, tsaye a dama da bagaden turare.
12 Ya inestotba si Sacharias anae jalie, ya mato minaañao gui jiloña.
Da Zakariya ya gan shi sai ya firgita, tsoro kuma ya kama shi.
13 Lao y angjet ilegña nu güiya: Sacharias, chamo maaañao; sa y tinaetaemo este majungog; ya y asaguamo as Elisabet ufañago y patgon laje, ya umafanaan naanña si Juan.
Amma mala’ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya; an ji addu’arka. Matarka Elizabet za tă haifa maka ɗa, za ka kuma ba shi suna Yohanna.
14 Ya uguaja jao minagof yan alegria; ya y megae umagof nu y mafañaguña.
Zai zama abin murna da farin ciki a gare ka, mutane da yawa kuwa za su yi murna don haihuwarsa,
15 Sa udangculo güe gui menan Señot; ya ti uguimen bino ni metgot na guinem ya ubulagüe Espiritu Santo, guinin y tiyan nanaña.
gama zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba kuwa zai taɓa shan ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba. Zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun haihuwa.
16 Ya megae gui famaguon Israel, ujabira nu y Señot, Yuusñija.
Shi ne zai juye mutanen Isra’ila da yawa zuwa wurin Ubangiji Allahnsu.
17 Ya ujanaogüe gui menan y mataña nu y espiritu yan y ninasiñan Elias, para unanalo y corasonñija y mañaena guiya y famaguon, yan y manchátmatago ni y tiningo y manunas; para ufamauleg nu y Señot y taotao, ni y esta fanmauleg para güiya.
Zai sha gaban Ubangiji, a ruhu da kuma iko irin na Iliya, domin yă juye zukatan iyaye ga’ya’yansu, marasa biyayya kuma ga zama masu biyayya don yă kintsa mutane su zama shiryayyu domin Ubangiji.”
18 Ya ilegña si Sacharias nu y angjet: Jaftaemano jutungo este? sa guajo bijoyo ya y asaguajo megae jaaniña.
Sai Zakariya ya tambayi mala’ikan ya ce, “Yaya zan tabbatar da wannan? Ga ni tsoho, matana kuma ta kwana biyu.”
19 Ya manope y angjet ya ilegña nu güiya: Guajo si Gabriel, na gaegue yo tumotojgue gui menan Yuus; ya guajo esta matago na jucuentusejao, ya junaejao ni este mauleg na sinangan.
Mala’ikan ya ce, “Ni ne Jibra’ilu. Ina tsaya a gaban Allah, an kuma aiko ni in yi maka magana, in kuma faɗa maka wannan labari mai daɗi.
20 Ya estagüe, na jago udojao ya ti siña uncuentos, asta y jaane nae este macumple estesija; sa y ti unjongue y sinanganjo, ni umacumple y tiempoña.
Yanzu za ka zama bebe, ba za ka ƙara iya magana ba sai ranar da wannan magana ta cika, saboda ba ka gaskata da kalmomina waɗanda za su zama gaskiya a daidai lokacinsu ba.”
21 Ya y taotao sija manmannanangga as Sacharias, ya ninafanmanman ni y inapmamña gui guimayuus.
Ana cikin haka, mutane suna jiran Zakariya, suna kuma mamaki me ya sa ya daɗe haka a cikin haikali.
22 Ya anae jumuyong, ti siña umadingane sija; ya matungo na manlie un linie gui guimayuus; lao güiya sigue di fumatinas y señatja; ya sumaga udo.
Da ya fito, bai iya yin musu magana ba. Sai suka gane, ya ga wahayi ne a haikali, domin ya dinga yin musu alamu, amma ya kāsa yin magana.
23 Ya anae esta munjayan y jaanin y ministroña, jumanao para y guimaña.
Da lokacin hidimarsa ya cika, sai ya koma gida.
24 Ya despues di ayo sija na jaane mapotgue y asaguaña as Elisabet, ya janana sinco na meses, ya ilegña:
Bayan wannan, matarsa Elizabet ta yi ciki, ta kuma riƙa ɓuya har wata biyar.
25 Taemanoja y Señot jafatinas para guajo, este sija na jaane nae jaatanyo para unajanao y mamajlaojo gui entalo taotao sija.
Sai ta ce, “Ubangiji ne ya yi mini wannan. A waɗannan kwanaki ya nuna tagomashinsa ya kuma kawar mini da kunya a cikin mutane.”
26 Y mina saes na mes, y angjet Gabriel esta tumago guine as Yuus, para un siuda guiya Galilea, ni y naanña y Nasaret,
A wata na shida, sai Allah ya aiki mala’ika Jibra’ilu zuwa Nazaret, wani gari a Galili,
27 Guiya un bitgen, nobia y un laje naanña si José, familian David; ya y naan y bitgen si Maria.
gun wata budurwar da aka yi alkawarin aurenta ga wani mutum mai suna Yusuf daga zuriyar Dawuda. Sunan budurwar Maryamu.
28 Ya jumalom manu nae estaba güe, ya ilegña: Jafa tatatmana jao na guefmaborese jao; y Señot gaegue guiya
Mala’ikan ya je wurinta ya ce, “A gaishe ki, ya ke da kika sami tagomashi ƙwarai! Ubangiji yana tare da ke.”
29 Lao pot este na sinangan, ninaestotba güe, ya jajajaso na jaftaemano este na sinaluda.
Maryamu ta damu ƙwarai da kalmominsa, tana tunani wace irin gaisuwa ce haka?
30 Entonses y angjet ilegña nu güiya: Maria, chamo maaañao; sa unsoda y finaborese gui menan Yuus.
Amma mala’ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.
31 Ya estagüe, na unmapotgue gui tiyanmo ya unfañago un patgon laje, ya umafanaan y naaaña si Jesus.
Ga shi za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa, za ki kuma ba shi suna Yesu.
32 Ya udangculo güe, ya umafanaan Lajin Gueftaquilo: ya y Señot Yuus ufannae güe y tronon David tataña.
Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi gadon sarautar kakansa Dawuda,
33 Ya ugobietna gui guima Jacob siesiempreja; ya y raenoña ugagaegue taejinecog. (aiōn g165)
zai yi mulkin gidan Yaƙub har abada, mulkinsa kuma ba zai taɓa ƙare ba.” (aiōn g165)
34 Entonses si Maria ilegña ni y angjet: Jafa jumuyong este? sa ti jutungo laje.
Maryamu ta tambayi mala’ikan ta ce, “Yaya wannan zai yiwu, da yake ni budurwa ce?”
35 Ya manope y angjet, ya ilegña nu güiya: Y Espiritu Santo umamaela guiya jago, ya y ninasiña y Gueftaquilo jafatinas y anineng gui jilomo; enaomina ayo na Santos na umafañago, umafanaan Lajin Yuus.
Mala’ikan ya amsa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki, ikon Maɗaukaki kuma zai rufe ke. Saboda haka, Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi Ɗan Allah.
36 Ya, estagüe, si Elisabet, parentesmo, locue güiya mapotgue un laje gui inamcoña; ya este y mina saes na mes nu güiya na mafanaan tifáfañago.
’Yar’uwarki Elizabet ma za tă haifi ɗa a tsufanta, ita da aka ce bakararriya, ga shi tana a watanta na shida.
37 Sa y sinangan Yuus, taya uno na taeninasiña.
Gama ba abin da zai gagari Allah.”
38 Entonses si Maria ilegña: Estagüe y tentagon Señot; ufatinas guiya guajo taemanoja y sinanganmo. Ya y angjet mapos guiya güiya.
Maryamu ta amsa ta ce, “To, ni baiwar Allah ce, bari yă zama mini kamar yadda ka faɗa.” Sai mala’ikan ya tafi abinsa.
39 Ya ayo na jaane sija, cajulo si Maria ya jumanao gusise para un tano taquilo, guiya un siudan Juda;
A lokacin sai Maryamu ta shirya ta gaggauta zuwa wani gari a ƙasar tudu ta Yahudiya,
40 Ya jumalom gui guima Sacharias ya jasaluda si Elisabet.
inda ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Elizabet.
41 Ya jumuyong taegüije na anae jajungog si Elisabet y sinaludan Maria, y patgon tumayog gui jalom tiyanña; si Elisabet bula Espiritu Santo,
Da Elizabet ta ji gaisuwar Maryamu, sai jaririn da yake a cikinta ya yi motsi. Elizabet kuma ta cika da Ruhu Mai Tsarki.
42 Ya umagang ni dangculo na inagang ya ilegña: Dichosojao gui entalo y famalaoan, ya dichoso y tinegchan tiyanmo.
Sai ta ɗaga murya da ƙarfi ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata. Mai albarka ne kuma ɗan da za ki haifa!
43 Ya guine manu este guiya guajo, na mato guiya guajo y nanan y Señotto.
Me ya sa na sami wannan tagomashi har da mahaifiyar Ubangijina za tă zo wurina?
44 Sa estagüe, na anae mato y inagang y sinaludamo gui talangajo, y patgon, gui jalom tiyanjo, tumayog ni minagofña.
Da jin gaisuwarki, sai jaririn da yake cikina ya yi motsi don murna.
45 Ya dichosogüe y jumonggue; sa uguaja y quinimple gui güinaja, ni esta masangane güe ni guinin y Señot.
Mai albarka ce wadda ta gaskata cewa abin da Ubangiji ya faɗa mata zai cika!”
46 Entonses ilegña si Maria: Janadangculo y antijo y Señot,
Sai Maryamu ta ce, “Raina yana ɗaukaka Ubangiji
47 Ya y espiritujo ninamagof gui as Yuus y Satbadotto.
ruhuna kuma yana farin ciki da Allah Mai Cetona,
48 Sa jaatan y dinespresiaoña y tentgoña; sa estagüe na desde pago jumafanaan dichosa ni todo y generasion.
gama ya lura da ƙasƙancin baiwarsa. Daga yanzu nan gaba dukan zamanai za su ce da ni mai albarka,
49 Sa ayo na guaja ninasiña, jafatinas guiya guajo dangculo na güinaja; ya santos y naanña.
gama Mai Iko Duka ya yi mini manyan abubuwa, sunansa labudda Mai Tsarki ne.
50 Ya y minaaseña gaegue gui generasion taotao sija, gui jiloñija ni manmaañao nu güiya.
Jinƙansa ya kai ga masu tsoronsa, daga zamani zuwa zamani.
51 Ya pot y canaeña jafanue minetgot; janafañuja y sobetbio sija gui jinason y corasonñija.
Ya aikata manyan ayyuka da hannunsa; ya watsar da waɗanda suke masu girman kai a zurfin tunaninsu.
52 Ya jayute papa y magas gui tronoñija, ya jajatsa y manumitde.
Ya saukar da masu mulki daga gadajen sarautarsu amma ya ɗaukaka ƙasƙantattu.
53 Ya y manñalang janafanbula ni y minauleg; ya y manmigüinaja janafanjanao yan y tae sinajguan.
Ya ƙosar da masu yunwa da kyawawan abubuwa amma ya sallami mawadata hannu wofi.
54 Ya jaayuda si Israel tentagoña, para ufanjaso y miñaase,
Ya taimaki bawansa Isra’ila, yana tunawa yă nuna jinƙai
55 (Taemano y jasangane y mañaenata), as Abraham yan y semiyaña para todo y tiempo. (aiōn g165)
ga Ibrahim da zuriyarsa har abada, kamar yadda ya faɗa wa kakanninmu.” (aiōn g165)
56 Si Maria sumaga yan güiya calang tres meses ya despues jumanao asto iyasija.
Maryamu ta zauna da Elizabet kusan wata uku sa’an nan ta koma gida.
57 Ya si Elisabet jacumple y tiempo nae para ufañago; ya mañago un patgon laje.
Sa’ad da kwanaki suka yi don Elizabet ta haihu, sai ta haifi ɗa.
58 Ya anae majungog ni tiguangña yan y parientesña, na si Yuus janadangculo y minaaseña guiya güiya; ya manmagof yan güiya.
Maƙwabtanta da’yan’uwanta suka ji cewa Ubangiji ya nuna mata jinƙai mai yawa, suka kuma taya ta farin ciki.
59 Ya susede na y mina ocho na jaane manmato para umasircunsida y patgon: ya malagoñija umafanaan ni y naan tataña as Sacharias.
A rana ta takwas, sai suka zo don a yi wa yaron kaciya, dā za su sa masa sunan mahaifinsa Zakariya ne,
60 Ya manope y nanaña ya ilegña: Aje, sa umafanaan si Juan.
amma mahaifiyar yaron ta ce, “A’a! Za a ce da shi Yohanna.”
61 Ya ilegñija nu güiya: Taya gui manparientesmo mafanaan nu este na naan.
Sai suka ce mata, “Ba wani a cikin danginku mai wannan suna.”
62 Ya maseñat y tataña, ya mafaesen jafa malagoña umafanaan.
Sai suka yi alamu wa mahaifinsa, don su san sunan da zai su a kira yaron.
63 Ya mangagao un diquique na tabla ya jatugue ilegña: Si Juan naanña. Ya todo sija ninafanmanman.
Ya yi alama a kawo masa allo, a gaban kowa sai ya rubuta, “Sunansa Yohanna.” Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.
64 Ya enseguidas mababa y pachotña, ya mapula y jilaña, ya cumuentos, jabendise si Yuus.
Nan da nan bakinsa ya buɗe harshensa kuma ya saku, sai ya fara magana yana yabon Allah.
65 Ya guaja minaañao gui jiloñija todo y mañasaga gui oriyañija: ya gui todo y tano taquilo guiya Judea, masasangan este sija na sinangan.
Maƙwabta duk suka cika da tsoro, mutane kuwa suka yi ta yin magana game da dukan waɗannan abubuwa a ko’ina a cikin ƙasar tudu ta Yahudiya.
66 Ya todosija y jumujungog jaadaje gui corasonñija ya ilegñija: Jafa jumuyong este na patgon? Sa y canae Yuus gaegue guiya güiya.
Duk waɗanda suka ji wannan kuwa sun yi mamaki suna cewa, “To, me yaron nan zai zama?” Gama hannun Ubangiji yana tare da shi.
67 Ya si Sacharias, tataña, bula Espiritu Santo ya japrofetisa, ilegña:
Mahaifinsa Zakariya ya cika da Ruhu Mai Tsarki sai ya yi annabci ya ce,
68 Bendito y Señot, y Yuus y Israel; sa jabisita ya jafatinas y redension, para taotaoña,
“Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin ya zo ya kuma fanshe mutanensa.
69 Ya janacajulo para jita un canggelon y satbasion, gui guima y tentagoña as David,
Ya tā mana ƙahon ceto a gidan bawansa Dawuda
70 (Taegüijija na jasasangan gui pachot y mañantos na profetaña, ni esta gaegue guinin tutujonña y tano), (aiōn g165)
(yadda ya yi magana tun tuni ta wurin annabawansa masu tsarki), (aiōn g165)
71 Satbasion gui y enemiguta yan gui canae todo y chumatliijit;
cewa zai cece mu daga abokan gābanmu daga kuma hannun dukan waɗanda suke ƙinmu
72 Para umafanue y minaaseña gui mañaenata, ya umajaso y santos na tratoña;
don yă nuna jinƙai ga kakanninmu, yă kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
73 Y juramento ni manjula as Abraham ni tatata,
rantsuwar da ya yi wa mahaifinmu Ibrahim,
74 Na güiya unaejit linibreta gui canae y enemiguta ya utasetbe güe sin minaañao,
don yă kuɓutar da mu daga hannun abokan gābanmu, yă kuma sa mu iya yin masa hidima babu tsoro,
75 Y sinantos yan y tinunas gui menaña todo y jaanita.
cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakinmu.
76 Ya, jago, patgon, unmafanaan profetan y Gueftaquilo; sa unjanao gui menan y Señot para unfamauleg y chalanña;
“Kai kuma, ɗana, za a ce da kai annabin Maɗaukaki; gama za ka sha gaban Ubangiji don ka shirya masa hanya,
77 Para ufanamatungo y satbasion gui taotaoña ni y maasiin y isaoñija,
don ka sanar da mutanensa ceto, ta wurin gafarar zunubansu,
78 Pot causa y corason y minaaseña y Yuusta, anae y candit ogaan guinin taquilo, jabisitajit,
saboda jinƙai na Allahnmu mai ƙauna, hasken nan na ceto zai ɓullo mana daga sama,
79 Para junae inina y manmatatachong gui jemjom yan y anineng y finatae; para ufanue y patasta gui chalan y pas.
don yă haskaka a kan waɗanda suke zama cikin duhu, da kuma cikin inuwar mutuwa, don yă bi da ƙafafunmu a hanyar salama.”
80 Ya y patgon lumala ya mumetgot gui espiritu ya sumaga gui desierto asta y jaane anae esta matungo guiya Israel.
Yaron kuwa ya yi girma ya kuma ƙarfafa a ruhu; ya zauna a hamada sai lokacin da ya fito a fili ga mutanen Isra’ila.

< San Lucas 1 >