< Lucas 11 >

1 Y anacó, que sinando beqelando andré yeque stano, pur achinóse a mui, penó á ó yeque es discipules de ó. Erañó, bedela amangue a manguelar á Un-debél, sasta tambien Juan bedó á desqueres discipules.
Wani lokaci, Yesu yana yin addu'a a wani wuri, sai daya daga cikin almajiransa yace da shi, “Ubangiji, ka koya mana yin addu'a kamar yadda Yahaya ya koya wa almajiransa.”
2 Y les penó: Pur manguelareis, penelad: Amaro Dada, oté andré o Tarpe, majarificable sinele tun nao. Abillele tun chim. Sinele querdi tun pesquital andré a jolili, sasta andré o Tarpe.
Yesu ya ce ma su, “Sa'anda ku ke yin addu'a ku ce, 'Uba a tsarkake sunanka. Mulkin ka ya zo.
3 Diñamangue achibes amaro manro de cada chibes.
Ka ba mu abin da za mu ci a kowacce rana.
4 Y amangue ertina amarias visabas, andiar sasta mu ertinamos á os sares, sos debisarelen amangue buchi. Y na enseeles amangue andré o chungalo y choro.
Gafarta mana zunubanmu, kamar yadda muke gafarta ma wadanda suke mana laifi. Kada ka kai mu cikin jaraba.'”
5 Les penó tambien: Coin de sangue terela yeque monro, y chalará á ó á pas-rachi, y le penará: Monro, prestelamangue trin manres,
Yesu ya ce masu, “Wanene a cikinku idan yana da aboki, za ya je wurinsa da tsakar dare ya ce masa, ''Aboki, ka ba ni rancen dunkulen gurasa guda uku,
6 Presas monro de mangue ha bigoreado del drun, y na terelo buchi que chitar anglal de ó.
da ya ke wani abokina ya iso yanzu daga tafiya, kuma ba ni da abin da zan ba shi ya ci,'
7 Y o aver rudelase de enrun, penando: Na sinele á mangue trajatoso, ya sinela pandada a bundal, y minres lacrés sinelan tambien sasta menda andré a cheripen, n’astis que menda me costunase somia diñartelos.
Sai wanda yake ciki, ya amsa, ya ce, 'Kada ka dame ni. Na riga na rufe kofa ta, kuma ni da yarana mun riga mun kwanta. Ba zan iya tashi in ba ka gurasa ba.'
8 Y si o aver perseverase araquerando á la bundal, penelo á sangue, que ya que na se costunase á diñarselos por sinelar desquero quiribo; aromali por desqueres goles se costunaria, y le diñaria sares os manres hubiese menester.
Na fada maku, ko da bai tashi ya ba ka gurasar ba, a matsayin abokinsa, ba ka ji kunya ba, ka nace da rokonsa, za ya tashi ya ba ka dukan yawan gurasar da kake bukata.
9 Y menda penelo á sangue: Manguelad, y se os diñará: orotelad, y alachalareis: araquelad, y se os pendrabará.
Ni kuma ina ce maku, ku roka za a ba ku; ku nema za ku samu; ku kwankwasa za a bude maku.
10 Presas o saro sos manguela, ustilela: y ó sos orotela, alachela: y al sos araquela, se le despandará.
Domin dukan wanda yake roko ya na karba; dukan wanda ya ke nema kuma yana samu; kuma wanda yake kwankwasawa, za a bude masa.
11 ¿Y si yeque de sangue manguelare manro á desquero batu, le diñara ó yeque bar? ¿ó si yeque macho, por baji le diñará yeque julistraba en lugar e macho?
Wanne uba ne a cikinku, idan dansa ya tambaye shi kifi, zai ba shi maciji a maimakon kifi?
12 ¿O si le manguelare yeque anro, por baji le bucharará yeque escorpion?
Ko kuwa idan ya tambaye shi kwai, za ya ba shi kunama?
13 Pues si sangue, sinando chorés, chanelais diñar lachias diñipenes á jires chabores ¿cuanto butér jire Dada del Tarpe diñara suncai lachi á junos sos se lo manguelaren?
To, da yake ku da kuke masu mugunta kun san ku ba 'yanyan ku abu mai kyau. Yaya fa ga Ubanku wanda yake cikin sama, za ya ba da Ruhu Mai Tsarki ga wadanda suka roke shi?”
14 Y sinaba Jesus bucharando abri yeque bengue: y ocona sinaba musilé, y pur hubó bucharado al bengue, chamulió o musilé, y sares se zibáron.
Wani lokaci, Yesu yana fitar da wani beben aljani. Sa'adda aljanin ya fita, sai mutumin da yake bebe ya yi magana. Sai taron mutanen suka yi mamaki!
15 Tami yeques de junos penáron: André sila de Beelzebub Manclay es bengues, bucharela os bengues.
Amma, wadansu daga cikin mutanen suka ce, “Da ikon Ba'alzabuba sarkin aljanu ne yake fitar da aljanu.”
16 Y averes somia pesquibarle, le manguelaban simache del Tarpe.
Wadansu suka gwada shi, suka nemi ya nuna masu wata alama daga sama.
17 Y pur dicó os carlochines de junos, les penó: Saro chim chingarando contra sí matejo, sinará chibado andré najipen; y perará quer opré quer.
Amma Yesu da yake ya san tunaninsu, ya ce da su, “Dukan mulkin da ya rabu biyu, gaba da kansa, ya rushe kenan, kuma idan gida ya rabu biyu, gaba da kansa za ya fadi.
18 Pues si Satanas sinele tambien en billa contra sí matejo, ¿como sinará en pindré o chim de ó? presas penelais que menda bucharelo abrí bengues por sila de Beelzebub.
Idan Shaidan ya rabu biyu gaba da kansa, ta yaya mulkinsa zai iya tsayawa? Gama kun ce ina fitar da aljanu ta wurin Ba'alzabuba.
19 Pues si menda por sila de Beelzebub bucharelo os bengues, ¿jirés chabores por coin os bucharelan? Por ocono sinarán junos jueces de sangue.
Idan ni na fitar da aljanu ta wurin Ba'alzabuba, ta wurin wa wadanda suke bin ku suke fitar da aljanu? Saboda haka, su ne zasu zama masu yi maku shari'a.
20 Tami si sat l’angusti de Debél bucharelo os bengues, aromalí o chim de Debél ha bigoreado á sangue.
Amma idan daga wurin Allah na ke fitar da aljanu, to, ya zama ke nan mulkin Allah ya zo wurinku.
21 Pur o manusalo ujarela desquero quer, andré trifusco sinelan sarias as buchias que terela.
Idan mutum mai karfi, mai kayan fada ya tsare gidansa, kayansa za su tsira.
22 Tami si abillando aver butér manusalo que ó, le venciere, le nicobará sarias as armas de ó, andré que pachibelaba, y sicobará desquero jayere.
Amma idan wani mutum wanda ya fi shi karfi ya zo ya ci nasara a kansa, zai dauke kayan fadan daga wurin mutumin, kuma ya kwashe kayansa.
23 O sos na sinela con-a-mangue, contra mangue sinela: O sos na ustilela con-a-mangue, najibela.
Wanda ba ya tare da ni, gaba da ni ya ke yi, kuma wanda ba ya tattarawa tare da ni, watsarwa yake yi.
24 Pur o bengue jindo ha chalado abrí de yeque manu, pirela por stanes bipaniosos orotando paratuté: y pur no lo alachela, penela: Mangue limbidiare á minrio quer, d’uque chalé abrí.
Idan kazamin ruhu ya fita daga cikin mutum, ya kan bi ta wurin busassun wurare yana neman wurin da zai huta. Idan bai samu ba sai ya ce, 'Bari in koma gidana inda na baro.
25 Y pur limbidiela, lo alachela julabado y chito.
Sa'adda ya dawo, ya tarar an share gidan, an kuma gyara shi tsaf.
26 Entonces chala, y ustilela sat ó averes efta bengues, butér chores que ó, y chalan andré, y socabelan oté. Y lo segriton de ocola manu sinela butér choro que lo brotobo.
Sai ya je ya dauko wadansu aljanu guda bakwai wadanda su ka fi shi mugunta, su zo su zauna a wurin. Sai karshen mutumin nan ya fi farkonsa muni.”
27 Y anacó, que penando ó ocono, yeque cadchi de enré a sueti ardiñó a voz, y le garló: Majari a poria sos te chindó, y as chuchais sos mamaste.
Ya zama, lokacin da ya ke fadin wadannan abubuwa, wata mace ta tada muryarta a cikin taron mutanen ta ce da shi, “Mai albarka ne cikin da ya haife ka, da maman da ka sha.”
28 Y ó rudeló: Nanai! antes majares junos sos junelan a varda de Debél y l’ujarelan.
Sai shi kuma ya ce, “Masu albarka ne wadanda suke jin maganar Allah suke yin biyayya da ita.”
29 Y sasta a sueti abillase de sarias aricatas, se chibó a penar: Ocona rati, rati sungali sinela, simache manguela, y simache na le sinará diñada, sino a simache e Propheta Jonás.
Lokacin da mutane suke kara taruwa, sai ya fara cewa, “Wannan tsara, muguwar tsara ce. Ta na neman alama, Ko da yake ba wata alamar da za a bata sai irin ta Yunusa.
30 Presas sasta Jonás sinaba simache a junos de Ninive; andiar tambien o Chaboro e manu la sinará á ocona rati.
Domin kamar yadda Yunusa ya zama alama ga mutanen Neneba, haka kuma Dan Mutum za ya zama alama ga wannan tsara.
31 La Crallisa e Pas-chibe se ardiñará andré juicio contra os manuces de ocona rati, y os saplará, presas abílló de os fines de la pu á junelar a chaneleria de Salomon; y he acoi butér que Salomon andré ocona stano.
Sarauniyar Kudu, za ta tsaya ta yi shari'a da mutanen wannan tsara, kuma za ta kashe su, gama ta zo daga wuri mai nisa domin ta saurari hikimar Sulaimanu. Kuma ga wani wanda ya fi Sulaimanu a nan.
32 Os manuces de Ninive se ardiñarán contra ocona rati andré juicio, y la saplarán: presas quereláron penitencia á los goles de Jonás; y he acoi buter que Jonás andré ocona stano.
Mutanen Neneba, za su tsaya shari'a da matanen wannan tsara, kuma za su kashe su. Gama sun ji wa'azin Yunusa sun tuba. Kuma ga wani wanda ya fi Yunusa a nan.
33 Cayque urdiflela á yeque mermellin, y la chitela andré yeque stano escondido, ni ostely de yeque melalo; sino opré yeque dendesquero, somia que junos sos abillelan andré diquelen a dut.
Ba wanda zai kunna fitila ya boye ta, ko kuwa ya sa ta a karkashin kasko, amma zai sa ta a mazaunin ta domin dukan wanda ya shiga dakin ya ga haske.
34 A mermellin de tun trupos sinela tun aqui. Si tun aqui sinare lachi, saro tun trupos sinará dutoso: tami si sinare chori, tambien tun trupos sinará bi dut.
Idon ku shine fitilar jikinku. Idan idonku yana gani sosai, jikinku zai cika da haske. Amma idan idonku ba ya gani sosai, jikinku zai cika da duhu.
35 Diquela pues, que a dut andré tucue, na sinela rachi.
Ku yi hankali fa, domin kada hasken da ya ke wurinku ya zama duhu.
36 Y andiar si saro tun trupos sinare dutoso, bi terelar yeque aricata de rachi, o saro sinará dutoso, y te diñará dut sasta yeque mermellin de dut.
Idan dukan jikinku yana cike da haske, babu duhu ko kadan, to sai dukan jikinku ya zama kamar fitilar da take bada haskenta a bisanku.”
37 Y pur sinaba chamuliando, le mangó yeque Phariséo, que chalase á jamar sat ó, y habiendo chalado andré, se besteló á la mensalle.
Sa'adda ya gama jawabi, sai wani Bafarise ya ce da shi ya zo gidansa ya ci abinci, sai Yesu ya shiga ya zauna.
38 Y o Phariséo se chitó á penchabar, y penar andré de sí, presas na se había chobelado antes de jamar.
Sai Bafarisen ya yi mamaki da ganin bai wanke hannu kafin ya ci abinci ba.
39 Y o Eraño penó: Acana sangue os Phariseyes chobelais lo de abrí e gote, y e plato; tami sangue de enrun sinelais perelalés de randipen y de choripen.
Amma sai Ubangiji ya ce da shi, “Ku Farisawa kuna tsabtace bayan kofi da bangaji, amma cikin yana cike da kazamta da mugunta.
40 Dineles, ¿O sos quereló ma sinela de abrí, na quereló tambien ma sinela de enrun?
Ku mutane marasa tunani, wanda ya yi wajen, ba shine ya yi cikin ba?
41 Ocono no obstante, diñelad limosna: y sarias as buchias os sinelan limpias.
Ku bayar da abin da ke ciki ga matalauta, kuma dukan abu zai zamar maku da tsafta.
42 ¡Tami ysna de sangue, Phariseyes, sos chibelais andré deque aricatas a cha-lachi, y a Romani cha, y sari hortaliza, y na querelaís bajin e lachiria, y e amor de Debél! Pues sinaba mistos querelar oconas buchias, y na mequelar ocolas.
Amma kaitonku Farisawa, gama kuna karbar zakka da daddoya da karkashi da kowanne irin ganye na lambu, amma kun watsar da adalci da kaunar Allah. Dole ne a yi adalci, a kaunaci Allah, a yi sauran abubuwan kuma.
43 ¡Ysna de sangue Phariseyes, sos camelais as brotoborias bestés andré as Synagogas, y sinelar saludados andré os maasqueres!
Kaitonku Farisawa, domin kuna so a ba ku wuraren zama masu kyau a cikin masujadai, a kuma yi maku gaisuwar bangirma a cikin kasuwanni.
44 ¡Ysna de sangue, sos sinelais sasta os sepulchres, sos na se diquela, y na lo chanelan os manuces, que pirelan por opré!
Kaiton ku, gama kuna kama da kabarbarun da ba yi masu shaida ba, mutane kuwa suna tafiya akansu ba tare da saninsu ba.”
45 Y rudelando yeque es Chandés e Eschastra, le penó: Duquendio, chamuliando oconas buchias, tucue afrentas tambien á amangue.
Wani malami a cikin shari'ar Yahudawa ya amsa masa ya ce, “Malam, abin da ka ce ya bata mana rai mu ma.”
46 Y ó penó: Y ysna de sangue Chandes e Eschastra: sos cargais os manuces de cargas, sos n’astis lliguerar, y sangue ni aun sat yeque de jiresias angustias pajabelais as cargas!
Sai Yesu ya ce, “Kaitonku malaman shari'a! Gama kun dora wa mutane kaya mai nauyi wanda ya fi karfinsu dauka. Amma ku, ko da dan yatsa ba ku taba kayan ba.
47 ¡Ysna de sangue, sos querelais os sepulchres es Prophetas: y jires batuces os maráron!
Kaiton ku, gama kuna gina abubuwan tunawa a kabuburan annabawa, alhali kuwa kakanni-kakanninku ne suka kashe su.
48 Aromali diñelais á chanelar, que camelais ma quereláron jires batuces: ocolas os maráron, chachipén; tami sangue querelais desqueres sepulchres.
Ya zama kenan kuna sane da ayyukan kakanni-kakanninku, domin sune suka kashe annabawan da kuke tunawa da su.
49 Por ocono penó tambien a chaneleria de Debél: Les bichabaré Prophetas y Apóstoles, y de junos mararán, y plastañarán para marar:
Saboda wannan daliline hikimar Allah ta ce, ''Zan aika manzanni da annabawa a wurinsu, kuma za su tsananta masu har ma za su kashe wadansu daga cikinsu.'
50 Somia que sinele pedida á ocona sueti a rati de sares os Prophetas, que sinaba chibada desde o principio de chiros.
Wannan tsarar, za ta dauki alhakin jinin dukan annabawan da aka kashe tun kafuwar duniya.
51 Desde a rati de Abel, disde a rati de Zacharias, sos meró entre o altar, y a cangri. Andiar os penelo, que pedida sinará á ocona sueti.
Tun daga jinin Habila, har zuwa jinin Zakariya wanda aka kashe tsakanin bagadi da wuri mai tsarki. I, na gaya ma ku za a nemi hakin su a wurin wannan tsarar
52 ¡Ysna de sangue, Chandés e Eschastra, sos ardiñasteis sat a clichi de chaneleria! sangue na chalasteis andré, y na mequelasteis á ocolas sos chalaban andré.
Kaitonku malaman shari'a na Yahudawa, domin kun dauke mabudin sani, ku da kanku ba ku shiga ba, kuma kun hana masu shiga su shiga.”
53 Y penando oconas buchias, os Phariseyes, y os Chandés e Eschastra se chibáron á chingarar con ó sat sila, y á trajatarle sat baribustrias preguntas,
Bayan da Yesu ya bar nan wurin, Marubuta da Farisawa suka yi gaba da shi, suka yi jayayya da shi a kan abubuwa da yawa,
54 Chibandole lazos, y orotando de sicobar de desquero sonsi yeque buchi somia astisar saplarle.
suna kokari su kafa masa tarko domin su kama shi a cikin kalmomin da yake fadi.

< Lucas 11 >