< Lucas 10 >

1 Y despues de ocono araqueró o Erañó tambien averes setenta y dui; y os bichabó de dui en dui anglal de ó á saro foros y gau, aduque ó terelaba de abillar.
Bayan haka, Ubangiji ya naɗa waɗansu mutum saba’in da biyu, ya aike su biyu-biyu, su riga shi yin gaba zuwa kowane gari da kowane wuri da zai shiga.
2 Y les penaba! Aromali a mies sinela baribustri, tami os randiñadores frimés. Manguelelad pues al Erañó e mies, que bichabele randiñadores á desqueri mies.
Ya ce musu, “Girbi na da yawa, amma ma’aikata kaɗan ne. Saboda haka, ku roƙi Ubangijin girbi ya aikar da ma’aikata zuwa gonarsa.
3 Chalad: He acoi menda bichabelo sangue, sasta brajias en medio de lueyes.
Ku tafi! Ina aikan ku kamar tumaki cikin kyarketai.
4 Na lliguereleis quisóbu, ni manrañea, ni calcos, ni aspasareis á cayque por o drun.
Kada ku ɗauki jakar kuɗi, ko jaka, ko takalma. Kada ma ku gai da kowa a kan hanya.
5 André o saro quer que chalareis, brotobo penelad: paz sinele á ocona quer.
“Sa’ad da kuka shiga wani gida, ku fara da cewa, ‘Salama a gare ku mutanen gida.’
6 Y si sinare oté chaboro de paz, se chibará opré ó jiré paz; y si nanai, se limbidiará á sangue.
In akwai mutum mai salama a gidan, salamarku za tă kasance tare da shi, in kuwa babu, salamarku za tă koma muku.
7 Y socabelad andré o matejo quer, jamando y piyando ma junos terelen, presas o randiñador digno sinela de desquero jayere. Na naqueleis de quer andré quer.
Ku zauna a wannan gidan, kuna ci kuna shan duk abin da suka ba ku, gama ma’aikaci ya cancanci albashinsa. Kada ku yi yawan sāke masauƙi, daga gida zuwa gida.
8 Y andré o saro foros andré coin chalareis, y sangue ustilaren, jamelad ma sangue childaren anglal.
“Sa’ad da kuka shiga garin, kuma aka karɓe ku, ku ci ko mene ne da aka ajiye a gabanku.
9 Y chibelad mistos á os merdés, sos andré ó terelare, y penadles: Se ha abillado sunparál á sangue o chim de Debél.
Ku warkar da marasa lafiya da suke wurin. Ku kuma faɗa musu cewa, ‘Mulkin Allah yana kusa da ku.’
10 Tami si andré o foros andré que chalareis, na ustilaren sangue, abillando por desqueres maasqueres, penelad:
Amma sa’ad da kuka shiga garin, kuma ba a karɓe ku ba, ku bi titi-titi ku ce,
11 Aun o pracos, sos se ha pegado á amangue de jiré foros, chibelamos contra sangue: Chanelad no obstante, que ha abillado sunparal o chim de Debél.
‘Ko ƙurar garinku da kuke manne a ƙafafunmu, mun karkaɗe muku. Duk da haka, ku tabbatar da wannan, “Mulkin Allah yana kusa.”’
12 Sangue penelo, que andré ocola chibes sinará fetér a baji de Sodoma que de ocola foros.
Ina dai faɗa muku, a ranan nan, za a fi jin tausayin Sodom fiye da wannan garin.
13 ¡Ysna de tucue, Corozain! ¡Ysna de tucue Bethsaida! Que si andré Tyro, y andré Sydón se hubiéran querdi as buchias, sos se han querdi andré sangue, chiros há que bestelados andré conel de gono y andré jaquestaro, hubieran querdi penitencia.
“‘Kaitonki, Korazin! Kaitonki, Betsaida!’ Ai, da a ce a Taya da Sidon ne aka yi ayyukan banmamaki da aka yi a cikinku, da tuni sun tuba, suna zama cikin rigar makoki da toka.
14 Aromali para Tyro, y Sydón, sinará andré o juicio fetér baji, que para sangue.
A ranar shari’a, za a fi jin tausayin Taya da Sidon fiye da ku.
15 Y tucue, Capharnaúm, ardiñado disde o Charos, disde o butrón sinarás chibado ostely. (Hadēs g86)
Ke kuma Kafarnahum, kina tsammani za ki sami ɗaukaka ne? A’a, za a hallaka ki. (Hadēs g86)
16 O sos junela á sangue, junela á mangue. Y ó sos girela á mangue, girela á ocola, sos mangue bichabó.
“Wanda ya saurare ku, ni yake saurara. Wanda ya ƙi ku, ni yake ƙi. Amma wanda ya ƙi ni kuwa, ya ƙi wanda ya aiko ni ne.”
17 Y limbidiáron os setenta y dui sat pesquital, penando: Erañó, aun os bengues se nos sujetan andré tiro nao.
Mutum saba’in da biyun nan suka dawo da murna, suka ce, “Ubangiji, har mun sha ƙarfin aljanu ma a cikin sunanka.”
18 Y les penó: Dicaba á Satanas sasta yeque maluno, sos peraba del Charos.
Sai ya amsa ya ce, “Na ga Shaiɗan ya fāɗi daga sama kamar walƙiya.
19 Diquelais: que sangue he diñado sila de pirar opré gulistrabas, y birberechas, y opré saro o ezor e daschmanu: y chichi sangue dañará.
Na ba ku iko da za ku tattaka macizai, da kunamai, ku kuma shawo kan dukan ikon abokin gāba, kuma ba wani lahani da zai same ku.
20 Tami andré ocono na asaseleis sangue: que os bengues os sinelen sujetos, antes asaselaos de que jires naues sinelan randados andré o Charos.
Duk da haka, kada ku yi farin ciki da cewa, kun sha ƙarfin ruhohi, amma ku yi farin ciki, domin an rubuta sunayenku a sama.”
21 André ocola mateja ocana se asaseló andré o Peniche, y penó; Díñelo á tucue chimusolano, Dada Erañó e Tarpe y de la pu, presas ucharaste oconas buchias, á os Chandes y peruiques, y as has chibado en dut a os chinores. Andiar sinela, Dada: presas andiar ha sinado de tun pesquital.
A wannan lokaci, Yesu, cike da murna ta wurin Ruhu Mai Tsarki ya ce, “Na yabe ka, ya Uba, Ubangijin sama da ƙasa, domin ka ɓoye waɗannan abubuwa ga masu hikima, da masu ilimi, ka kuma bayyana su ga ƙananan yara. I, ya Uba, gama wannan shi ne nufinka mai kyau.
22 Sarias as buchias a mangue sinelan diñadas de minrio Dada. Y cayque chanela, coin sinela o Chaboro, sino o Dada, ni coin sinela o Dada, sino o Chaboro, y ocola, á sos lo camelare penar o Chaboro.
“Ubana ya danƙa mini dukan kome. Ba wanda ya san Ɗan sai Uban, kuma ba wanda ya san Uban, sai Ɗan, da kuma waɗanda Ɗan ya zaɓa ya bayyana musu shi.”
23 Y limbidiándose hacia os discipules, penó: Majares as aquias, sos diquelan ma sangue diquelais.
Sai ya juya wajen almajiransa, ya ce musu a ɓoye, “Albarka ga idanun da suka ga abin da kuke gani.
24 Presas á sangue penelo, que baribustres Prophetas, y Crallises camelaron dicar ma sangue diquelais, y na lo dicáron; y junelar ma junelais, y na lo juneláron.
Ina faɗa muku, annabawa da sarakuna da yawa sun so su ga abin nan da kuke gani, amma ba su gani ba. Sun so su ji abin da kuke ji, amma ba su ji ba.”
25 Y se ardiñó yeque Chande de la Eschastra, y le penó somia pesquilarle: ¿Duquendio, que quereláre somia terelar chipen deltó? (aiōnios g166)
Wata rana, sai wani masanin dokoki ya miƙe tsaye don yă gwada Yesu. Ya tambaya ya ce, “Malam, me zan yi don in gāji rai madawwami?” (aiōnios g166)
26 Y ó le penó: ¿André á Eschastra qué sinela randado? ¿sasta lirenas?
Yesu ya amsa ya ce, “Me aka rubuta a cikin Doka? Yaya kake karanta ta?”
27 O rudelando penó: Camelarás al Erañó tun Debél de saro tun carlochin, y de sari tun ochi, y de sari tun sila, y de sari tun chaneleria: y á tun proximo sasta á tun matejo.
Sai ya amsa ya ce, “‘Ka ƙaunaci Ubangiji Allahnka da dukan zuciyarka, da dukan ranka, da dukan ƙarfinka, da kuma dukan hankalinka’; kuma, ‘Ka ƙaunaci maƙwabcinka kamar kanka.’”
28 Y le penó: Mistos has rudelado: Querelad ocono, y vivisarás.
Yesu ya ce, “Ka amsa daidai. Ka yi haka, kuma za ka rayu.”
29 O camelandose justificar á desquero matejo, penó a Jesus: ¿Y coin sinela minrio proximo?
Amma domin ya kāre kansa, sai ya tambayi Yesu ya ce, “Shin, wane ne maƙwabcina?”
30 Y Jesus ustilando a varda, penó: Elabel chalaba ostely de Jerusalém á Jerichó, y diñó andré bastes de yeques randes, sos le randáron; y despues de terelarle curado, le mequeláron pas-mulo, y se chapescáron.
Yesu ya amsa ya ce, “Wani mutum ya tashi daga Urushalima za shi Yeriko, sai ya fāɗi a hannun mafasa, wato,’yan fashi. Suka ƙwace tufafinsa, suka yi masa dūka, suka bar shi nan bakin rai da mutuwa.
31 Anacó pues, que nacaba por o matejo drun yeque erajai: y pur o dicó, nacó de muy dur.
Ya zamana wani firist ya bi kan wannan hanya. Da ya ga mutumin, sai ya bi gefe ya wuce abinsa.
32 Y andiar matejo yeque Levita, bigoreando sunparal de ocola stano, y dicandole, nacó de dur.
Haka ma wani daga kabilar Lawi, mai hidima cikin haikali, da ya zo wurin, ya gan shi, sai shi ma ya bi gefe ɗaya, ya wuce abinsa.
33 Tami yeque Samaritano, sos chalaba desquero drun, se bigoreó sunparal de ó: y pur le dicó, se lo diñó canrea.
Amma wani mutumin Samariya da yake kan tafiya, da ya kai inda mutumin yake, ya gan shi, sai ya ji tausayinsa.
34 Y bigoreandose, le pandó as merdes, chibelando andré siras ampio y mol: y chibandolo opré desquero gra, lo lligueró a yeque mesuna, y tereló cuidado de ó.
Ya je wurinsa, ya daddaure masa raunukansa, sa’an nan ya zuba mai, da ruwan inabi. Ya ɗauki mutumin ya sa a kan jakinsa, ya kai shi wani masauƙi, ya yi jinyarsa.
35 Y aver chibes sicobó dui calés, y os diñó al julai, y le penó: Garabelamanguele: y o saro sos gastisareles de butér, menda á tucue lo diñare pur limbidie.
Kashegari, sai ya ɗauki dinari biyu, ya ba wa mai masauƙin ya ce, ‘Ka lura da shi, bayan na dawo, zan biya ka duk abin da ka ƙara kashewa a kansa.’
36 ¿Coin de ocolas trin penchabelas que sinaba o proximo de ocola, sos diñó andré bastes es randes?
“A ganinka, a cikin waɗannan mutane uku, wane ne maƙwabcin mutumin da ya fāɗi a hannun mafasa?”
37 Ocola, rudeló o Chandé, sos tereló canrea sat ó: Pues cha, le penó, y querela tucue o matejo.
Masanin dokoki ya amsa ya ce, “Wanda ya nuna masa jinƙai.” Yesu ya ce masa, “Je ka, ka yi haka nan.”
38 Y anacó, que sasta sinasen andré drun, chaló Jesus andré yeque gau: y yeque cadchi, sos se hetó Martha, lo ustiló andré o quer de siró.
Yayinda Yesu da almajiransa suna cikin tafiya, sai ya kai wani ƙauye inda wata mace mai suna Marta ta marabce shi a gidanta.
39 Y ocona terelaba yeque plañi, araquerada Maria, sos bejelada á os pindres e Erañoró, junelaba su varda.
Tana da’yar’uwa mai suna Maryamu, wadda ta zauna a gaban Ubangiji tana jin maganarsa.
40 Tami Martha sinaba ocupada gajere andré as haciendas e quer: y siró se abilló y penó: ¿Erañó, na diqueles, sasta minri plañi, mangue ha mequelado colcori somia querelar? penle pues, que mangue ayude.
Marta kuwa, aikin hidima da ya kamata a yi, ya ɗauke mata hankali, sai ta zo wurin Yesu, ta ce, “Ubangiji, ba ka damu da yadda’yar’uwata ta bar mini aiki ni kaɗai ba? Gaya mata ta taimake ni!”
41 Y o Erañó le rudeló, y penó: Martha, Martha, baribu cuidadosa sinelas, y andré baribustrias buchias te trajatelas.
Amma Ubangiji ya amsa ya ce, “Marta, Marta, hankalinki ya tashi, kuma kina damuwa a kan abubuwa da yawa.
42 Aromali jomte solamente yeque buchi. Maria ha ustilado a aricata fetér, sos na le sinará nicobelada.
Amma abu ɗaya tak ake bukata, Maryamu ta zaɓi abin da ya fi kyau, kuma ba za a raba ta da shi ba.”

< Lucas 10 >