< लूका 18 >

1 फिरी यीशुऐ अपणे चेलयां जो इदे बारे बोलया की रोज प्राथना करणा कने कदी हिम्मत नी छडणी चाईदी, इस तांई उना ने ऐ कहाणी सुणाई:
Yesu ya ba wa almajiransa wani misali, don yă koya musu yadda ya kamata su dinga yin addu’a kullum, ban da fasawa.
2 “कुसकी शेहरे च इक न्यायधीश रेंदा था; सै ना परमेश्वरे ला डरदा था ना कुसी माणुऐ दी परवाह करदा था।”
Ya ce, “A wani gari, an yi wani alƙali wanda ba ya tsoron Allah, bai kuma kula da mutane ba.
3 कने उसी शेहरे च इक बिधवा भी रेंदी थी: जड़ी उदे बाल आई करी बोलदी थी, की मेरा न्याय करी के मिंजो दुशमणे ला बचाई ले।
A garin nan kuma, akwai wata gwauruwa, wadda ta dinga zuwa wurin alƙalin nan, da roƙo cewa, ‘Ka yi mini adalci tsakanina da maƙiyina.’
4 कने बड़े दिना दीकर तां मनया नी पर आखरी च मने च सोची करी बोलया, मैं ना परमेश्वरे ला डरदा, कने ना आदमियां दी परवाह करदा है;
“An daɗe yana ƙi, amma a ƙarshe ya ce cikin tunaninsa, ‘Ko da yake ba na tsoron Allah, ba na kuma kula da mutane ba,
5 तमी ऐ बिधवा मिंजो तंग करदी रेंदी है, इस तांई मैं इसा दा न्याय करणा है, कुथी इयां ना हो की बार-बार आई करी आखरी च मिंजो बुरी तरह थकाई दे।
amma don gwauruwan nan ta dame ni, zan tabbatar cewa ta sami adalci, domin kada tă gajiyar da ni, da yawan zuwanta.’”
6 प्रभु ने बोलया, सुंणा, की इनी अधर्मी न्यायधीशे क्या बोलया है, उस बारे च ध्याने ने सोचा।
Sai Ubangiji ya ce, “Ku ji fa abin da alƙalin nan, marar gaskiya, ya ce.
7 क्या परमेश्वर अपणे चुणयो लोकां दा न्याय नी करणा, जड़े रात-दिन उदे सामणे रोंदे न; परमेश्वरे उना दी मदद करणे च देर नी करणी है?
Ashe, Allah ba zai biya wa zaɓaɓɓunsa da suke masa kuka, dare da rana adalci ba? Zai ci gaba da ƙin sauraronsu ne?
8 “मैं तुसां ने बोलदा है; उनी झट उना दा न्याय करणा; तमी जालू मैं, माणुऐ दे पुत्रे बापस धरती ओंणा, तां मिंजो हेरानी होंदी है की क्या मिंजो धरतिया पर ऐसा माणु मिलगा जड़ा मिंजो पर भरोसा करदा हो।”
Ina gaya muku, zai tabbatar sun sami adalci, ban da ɓatan lokaci. Amma sa’ad da Ɗan Mutum ya dawo, zai sami bangaskiya a duniya ke nan?”
9 कने यीशुऐ उना लोकां ने जड़े अपणे बारे च सोचदे न, की असां धर्मी न, कने दुजयां जो निच बोलदे थे, ऐ कहाणी सुणाई
Yesu ya kuma faɗi wannan misali ga waɗansu masu taƙama da adalcinsu, kuma suna rena sauran mutane ya ce,
10 “दो माणु मंदरे च प्राथना करणा गे; इक फरीसी था कने दूजा कर लेणे बाला था।
“Waɗansu mutane biyu sun tafi haikali don yin addu’a. Ɗaya Bafarisiye ne, ɗayan kuma mai karɓar haraji.
11 फरीसी खड़ोई करी अपणे मने च इयां प्राथना करणा लग्गा, की हे परमेश्वर, मैं तेरा धन्यबाद करदा है, की मैं होरनी माणुऐ सांई बुरा करणे बाला, अन्यायी कने व्यभिचारी नी है, कने ना ही इस कर लेणेबाले सांई है।
Sai Bafarisiyen ya tashi tsaye, ya yi addu’a game da kansa yana cewa, ‘Allah, na gode maka, saboda ni ba kamar sauran mutane ba ne, wato, mafasa, masu aikata mugunta, masu zina, ko kuma kamar mai karɓar harajin nan.
12 मैं हफ्ते च दो बरी बरत रखदा है; मैं अपणिया कमाईया दा दसमां हिसा भी तुसां जो दिन्दा है।
Ina azumi sau biyu a mako, ina ba da zakka daga kowane abin da na samu.’
13 पर कर लेणेबाले दुर खड़ोई करी, स्वर्गे पासे दिखणा भी नी चाया, पर सै दुखे ने अपणिया छातिया पिटी-पिटी करी बोलणा लग्गा, हे परमेश्वर मैं पापी है, मिंजो पर दया कर, मिंजो माफ कर।
“Amma mai karɓar harajin ya tsaya daga nesa. Bai ma iya ɗaga kansa sama ba, sai ya buga ƙirjinsa, yana cewa, ‘Allah, ka yi mini jinƙai, ni mai zunubi ne.’
14 यीशुऐ बोलया मैं तुसां ने बोलदा है, की ऐ चुंगी लेणे वाला था ना की फरीसी माणु जड़ा परमेश्वरे सामणे धर्मी दसया; क्योंकि जड़ा कोई अपणे आपे जो बड़ा महान बणागा, सै छोटा करी देणा है; कने जड़ा अपणे आपे जो छोटा बणागा, उसयो आदर मान मिलणा।”
“Ina gaya muku, wannan mutum ne, ba ɗayan ba, ya koma gida baratacce, babu laifi a gaban Allah. Gama duk wanda ya ɗaukaka kansa, za a ƙasƙantar da shi. Wanda kuma ya ƙasƙantar da kansa, za a ɗaukaka shi.”
15 फिरी लोक अपणे बचयां जो यीशुऐ बाल लोणा लग्गे, ताकि सै उना पर हथ रखे; कने चेलयां दिखीकरी उना जो डांटया।
Mutane suna kawo jarirai wurin Yesu don yă taɓa su. Da almajiransa suka ga haka, sai suka kwaɓe su.
16 यीशुऐ बचयां जो अपणे बाल सदीकरी बोलया, बचयां जो मना मत करा कने इना जो मेरे बाल ओंणा दिया, क्योंकि परमेश्वरे दा राज्य उना दा है जड़ा इना बचयां सांई है।
Amma Yesu ya kira yaran a wurinsa ya ce, “Ku bar yara ƙanana su zo wurina. Kada ku hana su, gama mulkin Allah na irin waɗannan ne.
17 मैं तुसां ने सच्च बोलदा है, परमेश्वरे अपणे राज्य च सिर्फ उना लोकां जो ओणा देणा है जड़े परमेश्वरे दे राज्य जो बचयां सांई अपनांदा है।
Gaskiya nake gaya muku, duk wanda ba zai karɓi mulkin Allah kamar ƙaramin yaro ba, ba zai taɓa shiga mulkin ba.”
18 कुंनकी यहूदी अधिकारिये उसला पुछया, “उत्तम गुरू जी, मैं क्या कम्म करां की परमेश्वर मिंजो हमेशा दी जिन्दगी दे?” (aiōnios g166)
Wani mai mulki ya tambayi Yesu ya ce, “Malam managarci, me zan yi don in gāji rai madawwami?” (aiōnios g166)
19 यीशुऐ उसयो बोलया, तुसां मिंजो कजो उत्तम बोलदे न, उत्तम तां सिर्फ इक ही है, सै परमेश्वर है।
Yesu ya amsa ya ce, “Don me kake kira na managarci? Ai, ba wani nagari, sai Allah kaɗai.
20 तू परमेश्वरे दे हुक्मा जो तां जाणदा है की: “व्यभिचार नी करणा, झूठी गबाई नी देंणी, अपणे माता पिता दा आदर करणा।”
Ka san dokokin da suka ce, ‘Kada ka yi zina, kada ka yi kisankai, kada ka yi sata, kada ka ba da shaida ta ƙarya, ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka.’”
21 उनी बोलया, “मैं तां इना सबना हुक्मा जो तां बचपन ला मनदा आया है।”
Mutumin ya ce, “Ai, tun ina ƙarami, na kiyaye duka waɗannan.”
22 ऐ सुणीकरी, यीशुऐ उसला बोलया, तिजो च अजे भी इक गल्ला दी कमी है, जा, कने जड़ा कुछ तेरा है उसयो बेची करी गरीबां जो देई दे, तां तिजो स्वर्गे दा धन मिलणा, इयां करणे बाद आ कने मेरा चेला बणिया।
Da Yesu ya ji haka, sai ya ce masa, “Akwai abu ɗaya har yanzu da ya rage maka. Ka sayar da duk abin da kake da shi, ka ba wa matalauta, sa’an nan za ka sami dukiya a sama. Bayan haka, ka zo ka bi ni.”
23 सै ऐ सुणीकरी बड़ा उदास होई गिया, क्योंकि सै बड़ा अमीर था।
Da jin haka, sai ya ɓata rai, domin shi mai arziki ne sosai.
24 यीशुऐ उसयो दिखीकरी बोलया, अमीरां दा परमेश्वरे दे राज्य च जाणा बड़ा मुशकिल है।
Yesu ya kalle shi ya ce, “Yana da wuya fa, masu arziki su shiga mulkin Allah!
25 ऊंटे दा सुइया दे नाके चे निकलना असान है, पर अमीरां दा परमेश्वरे दे राज्य च जाणा बड़ा भरी मुशकिल है।
Tabbatacce, zai fi sauƙi raƙumi ya shiga ta kafar allura, da mai arziki ya shiga mulkin Allah.”
26 कने सुणने बालयां बोलया, “अगर ऐसा है तां कुण अपणे पापां दी सजा मिलणे ला बची सकदा है?”
Waɗanda suka ji wannan suka yi tambaya suka ce, “To, wa zai iya samun ceto?”
27 यीशुऐ जबाब दिता, “जड़ा माणुऐ ला नी होई सकदा है सै परमेश्वरे ला होई सकदा है।”
Yesu ya amsa ya ce, “Abin da ba ya yiwuwa ga mutane, mai yiwuwa ne ga Allah.”
28 पतरसे यीशुऐ जो पुछया, दिख, असां तां घर-बार छडी करी तेरे पिच्छे चलयो न।
Sai Bitrus ya ce, masa, “To, ga shi mun bar kome da muke da shi, don mu bi ka!”
29 यीशुऐ उना जो जबाब दिता, “मैं तुसां ने सच्च बोलदा है, जिनी भी परमेश्वरे दे राज्य तांई घर, या घरे बाली, या भाई, या माता पिता, या बाल बचयां जो छडी दितया हो।
Yesu ya ce musu, “Gaskiya nake gaya muku, ba wanda ya bar gida, ko mata, ko’yan’uwa maza, ko iyaye, ko yara, saboda mulkin Allah,
30 कने इस बेले केई गुणा जादा मिलणा; पर परलोके च हमेशा दी जिन्दगी मिलणी।” (aiōn g165, aiōnios g166)
da zai kāsa samun riɓi mai yawa, a wannan zamani, ya kuma sami rai madawwami a zamani mai zuwa.” (aiōn g165, aiōnios g166)
31 फिरी यीशुऐ बाहरां चेलयां जो एकांत च लेईजाई करी उना ने बोलया, दिखा, असां यरूशलेम शेहरे जो जाणा है, कने जितणियां भी गल्लां मेरे, माणुऐ दे पुत्रे तांई परमेश्वरे दा संदेश देणेबालयां लिखियां न सै सारियां पुरियां होणियां न।
Sai ya kai Sha Biyun gefe ɗaya, ya ce musu, “Za mu Urushalima, kuma dukan abin da annabawa suka rubuta a kan Ɗan Mutum zai cika.
32 “क्योंकि सै होर जातियां दे हथे देई देणा है। कने उना मेरा मजाक उड़ाणा है, कने मेरी निंदा करी के मिंजो पर थुकणा,
Za a ba da shi ga Al’ummai, za su yi masa ba’a, su zage shi, su tofa masa miyau,
33 कने मिंजो कोड़े मारणे, कने मिंजो मारी देणा है, कने मैं तिजे दिने मैं मरयां चे जिंदे होई जाणा है।”
za su yi masa bulala, su kuma kashe shi. A rana ta uku kuma zai tashi.”
34 कने चेलयां इना गल्लां चे कोई भी गल्ल नी समझ आई: कने ऐ गल्ल उना च ही लुक्की रेई, कने जड़ा बोलया था सै उना दिया समझा च नी आया।
Almajiran ba su gane da ko ɗaya daga cikin wannan ba. An ɓoye musu ma’anarsa, kuma ba su gane da abin da yake magana a kai ba.
35 जालू यीशु यरीहो शेहरे दे बखे पुज्जा, तां इक अन्ना सड़का कंडे बेईकरी भिख मंगा दा था।
Da Yesu ya yi kusa da Yeriko, akwai wani makaho da yake zaune a gefen hanya, yana bara.
36 कने भिड़ा दी चलने दी अबाज सुणीकरी पुछणा लग्गा, ऐ क्या होआ दा है?
Da ya ji taron suna wucewa, sai ya yi tambaya ko mene ne ke faruwa.
37 उना उसयो दसया, “नासरत दा यीशु मसीह जा दा है।”
Suka ce masa, “Ai, Yesu Banazare ne ke wucewa.”
38 तालू उनी अबाज लाईकरी बोलया, “हे यीशु, राजा दाऊदे दे बंशज, मिंजो पर दया कर।”
Sai ya yi kira ya ce, “Yesu, Ɗan Dawuda, ka yi mini jinƙai!”
39 जड़े अग्गे-अग्गे चलयो थे, सै उसयो डांटणा लग्गे की चुप रे: पर सै होर जोरे ने बकणा लग्गा, “हे राजा दाऊदे दी बंशज मिंजो पर दया कर।”
Mutane da suke gaba suka kwaɓe shi, suka ce masa ya yi shiru. Amma sai ya ƙara ɗaga murya, yana cewa, “Ɗan Dawuda, ka yi mini jinƙai!”
40 तालू यीशुऐ ऐ सुणया कने रुकी करी बोलया, “उसयो ऐथू लोआ।” कने तालू सै बखे आया तां यीशुऐ उसयो पुछया,
Sai Yesu ya tsaya, ya ba da umarni a kawo mutumin wurinsa. Da ya zo kusa, Yesu ya tambaye shi ya ce,
41 “तू क्या चांदा है की मैं तेरे तांई करे?” अन्ने उसने बोलया, गुरू जी, ऐ की मिंजो मिलणा लगी पोऐ।
“Me kake so in yi maka?” Sai ya amsa ya ce, “Ubangiji, ina so in sami ganin gari.”
42 यीशुऐ उसयो बोलया, “दिखणा लग, तेरे भरोसे जड़ा मिंजो पर है तिजो ठीक करी दिता है।”
Yesu ya ce masa, “Ka sami ganin garinka; bangaskiyarka ta warkar da kai.”
43 कने सै झट मिलणा लगी पिया; कने परमेश्वरे दी बड़ाई करदा होया उदे पिच्छे चली पिया, कने सारे लोंका ऐ दिखीकरी परमेश्वरे दी स्तुति किती।
Nan da nan, ya sami ganin garinsa, kuma ya bi Yesu, yana yabon Allah. Da dukan mutane suka ga wannan, sai su ma suka yabi Allah.

< लूका 18 >