< Filibiya 2 >

1 In ma yinnu nwo unizu likara nanya Kristi duku. Inma yinnu nwo usoo mang unuzun suume. Inma yinnu nwo ligo nin Ruhu duku. Inma yinnu nwo nkunekune mi cancom nin suun bunu duku.
In kuna da wata ƙarfafawa daga tarayya da Kiristi, in da wata ta’aziyya daga ƙaunarsa, in da wani zumunci da Ruhu, in da juyayi da tausayi,
2 Tan ayiabo nin kulo nin kpiluzu urum ulele, iyitta nin suu urume, inin yita nin munu ati nanya Ruhu, anin suu nsu nimon irume.
to, sai ku sa farin cikina yă zama cikakke ta wurin kasance da hali ɗaya, kuna ƙauna ɗaya, kuna zama ɗaya cikin ruhu da kuma manufa.
3 Yenje iwasu imonimon bara usuu nati sa ukpilizu unanzang. Na nonkon atime iyenje among nafo ikatin minu.
Kada ku yi kome da sonkai ko girman kai, sai dai cikin tawali’u, ku ɗauki waɗansu sun fi ku.
4 Yenje iwa kpiliza ubelle nimon ile na idi ninsuwe cas, ama kpilizang imon su namong wang.
Bai kamata kowannenku yă kula da sha’anin kansa kawai ba, sai dai yă kula da sha’anin waɗansu ma.
5 Kpilizang libau longo na lidi lin Kristi Yesu wang.
A cikin dangantakarku da juna, ya kamata halayenku su zama kamar na Kiristi Yesu.
6 Awa yitta nin kulap Kutelle, ama na awa yaun lissosin me nin Kutelle nafo imon ilenge na ame ma minu ba.
Wanda, ko da yake cikin ainihin surar Allah yake, bai mai da daidaitakansa nan da Allah wani abin riƙewa kam-kam ba,
7 Awa na wese litime nya liti. Ayauna kulap kucin. Anuzu nin kidowon nit usurne. Iwa seghe nin yenju nafo unit.
amma ya mai da kansa ba kome ba, yana ɗaukan ainihin surar bawa, aka yi shi cikin siffar mutum.
8 Awa toltin litime aso una dortun liru udun kul, ukul un kitene kuca.
Aka kuma same shi a kamannin mutum, ya ƙasƙantar da kansa ya kuma zama mai biyayya wadda ta kai shi har mutuwa, mutuwar ma ta gicciye!
9 Bara nani Kutelle uni wa ghantighe. Awa ninghe lissa ubun kolome lissa.
Saboda haka Allah ya ɗaukaka shi zuwa mafificin wuri ya kuma ba shi sunan da ya fi dukan sunaye,
10 Awa tinane bara nanya lissa Yesu vat nalung ma tumnu, alung nalenge na idi kitene kani nin kutiin a nanya kutiin.
don a sunan Yesu kowace gwiwa za tă durƙusa, a sama da a ƙasa da kuma a ƙarƙashin ƙasa,
11 Awa sunani tutung bara kolome lilem ma punu abellin Yesu Kristi Cikilareri, udun gongon Kutelle Ucif.
kowane harshe kuma yă furta cewa Yesu Kiristi Ubangiji ne, don ɗaukakar Allah Uba.
12 Bara nani, anan suuning, nafo na idin dortu kolome liri, na se meng duku ba, ama nene gbardang ka nin salininghe, sun katwa ntuccu mine nin fiu nin ketuzu kiti.
Saboda haka, ya abokaina ƙaunatattu, kamar yadda kullum kuke biyayya ba kawai sa’ad da ina nan ba, amma yanzu da ba na nan tare da ku, ku ci gaba da yin ayyukan cetonku da tsoro da kuma rawan jiki,
13 Bara Kutelleri di katwa nanya mine vat nin yinnu a usu katwa bara nmang me.
gama Allah ne yake aiki a cikinku, don ku nufa ku kuma aikata bisa ga nufinsa mai kyau.
14 Sun ko iyapin imon sa ugbondulu sa mayardang.
Ku yi kome ba tare da gunaguni ko gardama ba,
15 Sun katwa nin nile imone inan so sa alapi nin nono kidegen Kutelle sa indinon. Sun katwa nin nile imone bara inan balta nafo nkanang nanya yii, kitik kuji ku kwarkwok nin dirun fiu Kutelle.
don ku zama marasa abin zargi, sahihai’ya’yan Allah, waɗanda ba su da laifi, a zamanin mutane karkatattu, kangararru, waɗanda kuke haskakawa a cikinsu kamar fitilu a duniya
16 Minon gangan tigbulan nlai bara inan se imon ile na imati gongon lirin Kristi. Kubere nmanin yinnu na nnasu uccum sa katwa kahem ba.
kuna kuwa cin gaba da riƙe maganar rai domin in yi taƙama a ranar Kiristi cewa ban yi gudu ko fama a banza ba.
17 Ama ko igutuni nafo unakpu ulau nanyan ni liti nin katwa in yinnu sa uyenu mine, idin su ayiabo, nkuru nsu ayiabo nanghinu vat.
Amma ko da ana tsiyaye jinina kamar hadaya ta sha a kan hadaya da kuma hidimar da take fitowa daga bangaskiyarku, ina murna ina kuma farin ciki da ku duka.
18 Nanya nimon irume, anung wang dinayi abo, a iyitta nayi abo nin mi wang.
Haka ma ya kamata ku yi murna ku kuma yi farin ciki tare da ni.
19 Ama ndin cisu kibinayi kitin Cikilari Yesu a tuu Timitawus ku nayiri alele, meng wang nase likara asa nlaza nbelle mine.
Ina sa rai a cikin Ubangiji Yesu cewa zan aika da Timoti zuwa gare ku ba da daɗewa ba, don ni ma in ji daɗi sa’ad da na ji labarinku.
20 Bara na ndi nin mong tutung nafo ame ba, urika na adi nin nayi acine bara anunghe.
Ba ni da wani kamar sa, wanda yake da ainihin sha’awa a zaman lafiyarku.
21 Bara vat mine din pizuru imon nati minere, na imon Yesu Kristi ba.
Gama kowa yana lura da al’amuran kansa ne kawai, ba na Kiristi Yesu ba.
22 Ama fe yiru imon ile na adi, nafo na gono asa asuu ucife katwa, nanenere ame di katwa nin mi nanya nlirun laiye.
Amma, ai, kun san darajar Timoti yadda muka yi bautar bishara tare, kamar ɗa da mahaifinsa.
23 Ndin kpilizu ntuughe na nin molu kubi ba asa in yene ucin nimone kiti ninghe.
Saboda haka, ina sa rai, in aike shi da zarar na ga yadda abubuwa suke a nan.
24 Ama ndi ni kibinayi kirum nin Cikilari nworu meng liti ninghe wang ma dak na nin dadaunu ba.
Ni kuma ina da tabbaci a cikin Ubangiji cewa zan zo ba da daɗewa ba.
25 Ama inyene ukifo gbas ntuu Epaparoditus ku ukpillu kiti mine. Ame gwana nighari nin don katwa ning udu likum ning, a gono kadura nin kucin nsuu ning.
Amma ina gani ya dace in aika da Afaforiditus, ɗan’uwana, abokin aikina da kuma abokin famana, wanda kuma yake ɗan saƙonku, wanda kuka aika domin yă biya mini bukatuna.
26 Bara awa lanza kuyamine kang, amini wa yita ni suu awadi amal zuru nan ghinu vat, anung na lanza na adi ucine ba.
Gama yana marmarin ganinku duka ya kuma damu domin kun ji cewa ya yi rashin lafiya.
27 Nanere, awa su kidowo kang nafo aba ku. Ama Kutelle na lanza nkunekune me, a na ame usamme ba, umunju mengku wang bara nwa se liburi lisirne kitene liburi lisirne.
Ba shakka ya yi rashin lafiya, har ya kusa mutuwa. Amma Allah ya nuna masa jinƙai, ba shi kaɗai ba amma har da ni ma, don yă rage mini baƙin ciki kan baƙin ciki.
28 Nene nkipina usuu nworu ntuughe, bara andi iyeneghe tutung imanin yitu nin nayiabo ima kalu njirjir nibinayi mine.
Saboda haka na yi niyya ƙwarai in aike shi wurinku, don sa’ad da kuka sāke ganinsa za ku yi murna, ni kuma in rage damuwa.
29 Seren Epaporoditus ku nin naburi abo nanyan Cikilari. Taan anit nafo ame ngongong.
Ku marabce shi cikin Ubangiji da farin ciki mai yawa, ku kuma girmama mutane irinsa,
30 Bara kitene katwan Kristiari awa lantin uku. Awa nari ulai me anan suyi katwa nin kulunu katwa kanga nafe wa yinnin usue ba nanyaa katwa ninghe.
domin ya kusa yă mutu saboda aikin Kiristi, ya yi kasai da ransa don yă cikasa taimakon da ba ku iya yi mini ba.

< Filibiya 2 >