< Matiyu 12 >

1 Kubi kone na Yesu wa din cin nanya kunen nilarum liri na Sabbat. Kukpon da nono kadura me itunnan pucu nillarume nle.
A lokacin nan Yesu ya bi ta gonakin hatsi a ranar Asabbaci. Almajiransa kuwa suna jin yunwa, sai suka fara kakkarya kan hatsi suna ci.
2 A farisawa yene nani, iworo Yesu ku, “Yene nono katafe din su nimon ile na icaun isu liri na Sabar ba.”
Sa’ad da Farisiyawa suka ga wannan, sai suka ce masa, “Duba! Almajiranka suna yin abin da doka ta hana a yi a ranar Asabbaci.”
3 Yesu woro nani, “Ikuna belu iyerti ile na iwa yertin nimon ile na Dauda wasu a, na kukpon wa daghe, nin nale na awa di naghinua?
Sai ya amsa ya ce, “Ba ku karanta abin da Dawuda ya yi ba ne sa’ad da shi da abokan tafiyarsa suka ji yunwa?
4 Na awa piru nanya kilari Kutelle, aleu imonli nanan katwa kilari Kutelle, ile na iserin nworu ali ba, nan nale na awadi nanghinu, ule na uduka wa nazaghe nin le, nin nalenge na iwa di ninghe wang, uduka wa naza nani nin le, Uduke wa yinnin a Priesta ku nin le nmang?
Ya shiga gidan Allah, da shi da abokan tafiyarsa suka ci keɓaɓɓen burodin, wanda doka ta hana su yi, sai firistoci kaɗai.
5 Tutung na isa yene nanya neyert, au liri na Sabat a Priest din nanzu Asabate ana asa usonani kulapi ba?
Ko kuwa ba ku karanta a Doka cewa a ranar Asabbaci firistoci sukan karya dokar Asabbaci duk da haka ba da yin wani laifi ba?
6 Bara nani meng belin minu, umong ulenge na na akatin kutii Kutelle di kikane.
Ina faɗa muku cewa waniwanda ya fi haikali yana a nan.
7 Ndafo iyiru ilenge imone, 'Meng din pizuri nkunekune nayiari ana ma nakpizu nakpizu ba.' Na iwa ni anan sali kulapi kulapi ba.
Da a ce kun san abin da waɗannan kalmomi suke nufi, ‘Jinƙai nake bukata, ba hadaya ba,’da ba ku zargi marar laifi ba.
8 Nanere gononit ame Cikilari liri na Sabatari.”
Gama Ɗan Mutum shi ne Ubangijin Asabbaci.”
9 Yesu suna kite udu nany kutii nlira mine.
Da ya ci gaba daga wurin, sai ya shiga majami’arsu,
10 Kitene, umong uni wadduku, nin cara na una koto. A Farisawa tirino Yesu ku, i woro, “Ucaun i shin nin mong liri na Sabata?” Bara inan se kulapi kiti me.
a nan kuwa akwai wani mutum mai shanyayyen hannu. Don neman dalili su zargi Yesu, sai suka tambaye shi suka ce, “Ya dace a warkar a ranar Asabbaci?”
11 Yesu bele nani, ghari nanya mine, awadi nin kukam kurum, tutung kukam kone nnin deu nanya kuwu kucamcam liri na Sabat, na ama kifu kunin anutun ba?
Ya ce musu, “In waninku yana da tunkiya, ta kuma fāɗa a rami ran Asabbaci, ba zai cire ta daga ramin ba?
12 Bara nani, na unit katin kukam nin tigo kiti Kutelle ba! Nanere nta, ucaun isu imon icine liri n Sabat.”
Sau nawa mutum ya fi tunkiya daraja! Saboda haka ya dace a aikata alheri ran Asabbaci.”
13 Yesu woro nnite, “Nakpa ucarafe,” unite nakpa ucare, utunna ushino, uso ucine nafo uleli ucare.
Sa’an nan ya ce wa mutumin, “Miƙa hannunka.” Sai ya miƙa, hannunsa kuwa ya koma lafiyayye, kamar dai ɗayan.
14 A Farisawa nuzu udas, itunna pizuru nimon ile na iba kifughe mun. Iwadin pizuru libau longo na iba ti imolughe.
Amma Farisiyawa suka fita suka ƙulla shawara yadda za su kashe Yesu.
15 Na Yesu nyino nani, a wonno kidowo kusari kurum, anit gbardang dofinghe, a shizuno nani nin tikonu mine.
Da ya gane wannan, sai Yesu ya janye daga wurin. Da yawa suka bi shi, ya kuwa warkar da dukan masu ciwonsu,
16 Awunno nani atuf na iwa belin umong ba.
yana jan musu kunne kada su faɗa wa kowa akan ko shi wane ne.
17 Unan so kidegen, ilemon na iwa belin nnuun Ishaya unan liru nin nu Kutelle, nbellu,
Wannan kuwa domin a cika abin da aka faɗa ta bakin annabi Ishaya ne cewa,
18 “Yene, kucin ning urika na nna fere; kinayi ning, urika na kibanayi ning din lanzu nmang me. Nma ti uruhu ning nanya me, ame manin bellu ushara kiti nanan salin bi.
“Ga bawana da na zaɓa, ƙaunataccena, wanda nake farin ciki da shi; zan sa Ruhuna a kansa, zai kuma yi shelar adalci ga al’ummai.
19 Na ama fo kidowo ba, sa agilu nin liwui kang; na umong tutung ma lanzu liwui me libau libene ba.
Ba zai yi faɗa ko yă ɗaga murya ba, ba kuwa wanda zai ji muryarsa a kan tituna.
20 Na awasa apuro kugosin ndiru likara ba; kinni ncin tutung na ama molu ba, se anin nutuno ushara unnasara.
Kyauron da ya tanƙwasa ba zai karye shi ba. Fitilar da ta yi kusan mutuwa ba zai kashe ta ba, sai ya jagoranci adalci zuwa ga nasara.
21 Alumai tutung mase likara nanya lissame.”
Cikin sunansa al’ummai za su dogara.”
22 Kube itunna ida nin mon unit kitin Yesu unan niduu nin nituri, agbergenu wadi nanya me. Ashino ninghe, unit unan niture nin niduwe yinno ulira akuru atunna nyenju kiti.
Sai aka kawo masa wani bebe kuma makaho mai aljani, Yesu kuwa ya warkar da shi, har ya iya magana ya kuma sami ganin gari.
23 vat ligozin nanit wa yatinju inin woro, “Sa ulelere ma yitu usaun Daude?”
Dukan mutane suka yi mamaki, suka ce, “Wannan Ɗan Dawuda ne kuwa?”
24 Na Farisawa nlaza uliru nimon izikiki ilele, iworo, “Na unit ulele din nutuzunu agbergenu ba se nin yinnun Belzubab, usaun ngo nagbergenu.”
Amma da Farisiyawa suka ji haka, sai suka ce, “Ahab, da Be’elzebub sarkin aljanu ne kaɗai, wannan mutum yake fitar da aljanu.”
25 Yesu wa yiru nin kpilizu mine aworo nani, “Vat tigo tongo na tidi nin nivira nin litime wulu, tutung kokame kagbiri sa kilari kanga na adi nivira nin liteme ma yisunu ba.
Yesu kuwa ya san tunaninsu sai ya ce musu, “Duk mulkin da yake gāba da kansa zai lalace, kuma duk birni ko gidan da yake rabe gāba da kansa ba zai ɗore ba.
26 Adi shitan din nutuzunu shitan ku, to adi nivira nin liteme. iyizari kipin tigo me ba yissunu?
In Shaiɗan yana fitar da Shaiɗan, ai, ya rabu yana gāba da kansa ke nan. Yaya kuwa mulkinsa zai ɗore?
27 Adi tutung ndin nutuzunu agbergenu nin yinnun Belzubal, nin yinnun ghari anan dortu mine din nutuzunu nani? Bara nani, ima sominu anan mawucu-wucu.
In kuwa ta wurin Be’elzebub nake fitar da aljanu, to, ta wa mutanenku suke fitar da su? Saboda haka, su ne za su zama alƙalanku.
28 Adin tutun ndin nutuzunu nagbergenu nin Ruhu Kutelleri, to kipin tigo Kutelle nda nanya mine.
Amma in ina fitar da aljanu ta wurin Ruhun Allah ne, to, fa, mulkin Allah ya zo muku ke nan.
29 Tutung iyizari unit ba piru kilari nnan nagang asu likiri nomon irika na adumun sa ucizunun teru nan nagaghe? Aning su likiri nimon nnite kilari me.
“Ko kuwa, yaya wani zai iya shiga gidan mai ƙarfi yă ƙwace masa kaya ba tare da ya fara daure mai ƙarfin nan tukuna ba? Sa’an nan zai iya washe gidansa.
30 Ulenge na adi nin miba adi nivira nin mi, ulenge tutung na adin piture nin mi ba, unan musuzuri.
“Wanda ba ya tare da ni, yana gāba da ni ne, kuma wanda ba ya taya ni tarawa, watsarwa yake yi.
31 Bara nani ndin bellu minu vat nalapi nin nanzu lissa iba kusu anit mun, ama unanzu lissan Ruhu na iba kusu ba.
Saboda haka ina gaya muku, za a gafarta wa mutane kowane zunubi da kuma saɓo, amma saɓo game da Ruhu, ba za a gafarta ba.
32 Tutung vat nlenge na abele nlon ligulang kitenen Nsaun nit, ilele ima kusughe mun. Ama vat nlenge naa abele uliru nivira nin Ruhu ulau, na iba kusu alele ba, na nle uyii ba, ana nyii ulenge na udin cinu wang ba. (aiōn g165)
Duk wanda ya zargi Ɗan Mutum, za a gafarta masa, amma duk wanda ya zargi Ruhu Mai Tsarki, ba za a gafarta masa ba, ko a wannan zamani ko a zamani mai zuwa. (aiōn g165)
33 Sa ukyele kuca gegeme a iburi me yita gegeme, sa kyele kuce nanzang a iburi kuni yita nanzang.
“Itace mai kyau, yakan ba da’ya’ya masu kyau. Itace marar kyau kuma, yakan ba da’ya’ya marasa kyau. Itace dai, da irin’ya’yansa ne ake gane shi.
34 Anung nono nabuni, tunda na idi nin likara lifacak, iba bellu imon icine nyizari? Bara unuzu nanya adadu liburari asa unu lira.
Ku macizai, ta yaya ku da kuke mugaye za ku iya magana kirki? Gama daga baki, mutum yakan faɗi abin da yake cikin zuciya.
35 Unit ulau unuzu filai kibinayi me asa anutuno imon icine, unit unan likara lifacak tutung unuzu filai kibinayi me asa anutuno ileli imon na idi facak.
Mutumin kirki yakan fito da abubuwa masu kyau daga ajiyar da aka a yi cikinsa, mugun mutum kuwa yakan fito da mugayen abubuwa daga cikin muguntar da aka yi ajiya a cikinsa.
36 Ndin bellu minu tutung, lirin shara, anit mani litul vat nliru unanzang ule na ina bellu.
Amma ina gaya muku cewa mutane za su ba da lissafi a ranar shari’a a kan kowace kalmar banza da suka faɗa.
37 Bara nanya nliru minere ima se ucinu, nanya nliru minere tutung ibase uteru.
Gama ta wurin kalmominka za a kuɓutar da kai, kuma ta wurin kalmominka za a hukunta ka.”
38 Among anan niyerti nin na Farisawa kawa Yesu ku iworo, “Unan dursuzu, tidi ninsu tuyene kulap unuzu kitife.”
Sa’an nan waɗansu Farisiyawa da malaman dokoki suka ce masa, “Malam, muna so mu ga wata alama mai banmamaki daga gare ka.”
39 Yesu kawa aworo nani, “Aji likara linanzang nin nanan funu din pizuru kulap. Ama na nkon kulap duku na iba ninani ba se kun Yunana unan liru nin nu Kutelle.
Sai ya amsa ya ce, “Mugaye da masu zinan zamanin nan suna neman wata alama mai banmamaki! Amma babu wadda za a nuna musu, sai dai alama ta annabi Yunana.
40 Bara Yunana wati ayiri atat nin nitik nitat nanya liburi fibo, nanere wang Usaun nnit bati ayiri atat nin nitik nitat kibinayi nyii.
Gama kamar yadda Yunana ya yi yini uku da kuma dare uku a cikin wani babban kifi, haka Ɗan Mutum zai yi yini uku da kuma dare uku a cikin ƙasa.
41 Anitin Ninivi ma yissunu kitin shara ninko kuji nanite, iba ti uteru nani. Bara iwa sun alapi mine nin lirun kpaduzun Yunana, manin yenen, umong nbun nin Yunana di kikane.
Mutanen Ninebe za su tashi a ranar shari’a tare da wannan zamani, su kuwa hukunta shi; don sun tuba saboda wa’azin Yunana, yanzu kuwa ga wanda ya fi Yunana girma a nan.
42 Ushono ngo kusarin nlime ma fitu liri nshara nin nanit nko kuje ati itere nani. Awa dak unuzu ligan nyii anan da lanza ubelen njijin Solomon, manin yeneng, umong nbun Solomon di kikane.
Sarauniyar Sheba za tă tashi a ranar shari’a tare da wannan zamani, tă kuwa hukunta shi; don ta zo daga ƙarshen duniya, ta saurari hikimar Solomon, yanzu kuwa ga wanda ya fi Solomon girma a nan.
43 Asa uruhu unanzanghe nnuzu nanya nnit, asa ukatiza nitin salin nmyen npiziru shinu, adi na ase ba.
“Sa’ad da mugun ruhu ya fita daga mutum, yakan bi wuraren da ba ruwa yana neman hutu, ba ya kuwa samu.
44 Asa aworo, 'nma kpilu kilari ning na nna nuzu ku.' Adi a kpilla, ase kilari kane ikuzu kinin inin ceu kinin lau.
Sa’an nan yakan ce, ‘Zan koma gidan da na bari.’ Sa’ad da ya iso, ya tarar da gidan ba kowa a ciki, shararre, kuma a kintse.
45 Amanin kpillu adi yiru ligowe ninghe nton tiruhu tinanzang tining kuzor na ti katinghe nin magunta, iba nin dak vat inin daso kikane. Ngisin lissosin nlele unite makatinu lin burne nin nanzang. Nanere bayitu nin ko kuje.”
Sai yă je yă ɗebo waɗansu ruhohi bakwai da suka fi shi mugunta, su kuwa zo su shiga su zauna a can. Ƙarshen mutumin nan fa zai fi farkonsa muni. Haka zai zama ga wannan mugun zamani.”
46 Na Yesu wa dutu nliru nin ligozine, uname nin nuwname tunna iyisina ndas, iwa di npizuru nwo ilirin ninghe.
Yayinda Yesu yake cikin magana da taron, sai ga mahaifiyarsa da’yan’uwansa tsaye a waje, suna so su yi magana da shi.
47 Umong woroghe, “Yene, unafe nin nuwnafine yissin ndas, idin pizuru nwo ilirin ninfi.”
Wani ya ce masa, “Mahaifiyarka da’yan’uwanka suna tsaye a waje, suna so su yi magana da kai.”
48 Yesu kawa aworo nani ulenge na abellinghe, “Ghari unanin? Ayagha tutung nuwna nin?”
Ya amsa masa ya ce, “Wace ce mahaifiyata, su wane ne kuma’yan’uwana?”
49 Atunna a nakpa ucara me udu kitin nono katwa me aworo, “Yene, kikane unaning nin nuwna ning!
Sai ya miƙa hannu wajen almajiransa ya ce, “Ga mahaifiyata da kuma’yan’uwana.
50 Bara vat nlenge na adin su imon kibinai Ncif ulenge na adi kitene kani, uleli unitere gwana ning kilime, nin kishono, a unaning.”
Ai, duk wanda yake aikata nufin Ubana wanda yake cikin sama, shi ne ɗan’uwana da’yar’uwata da kuma mahaifiyata.”

< Matiyu 12 >