< Luka 21 >

1 Yesu fiya iyizi ayene kitene kani anin yene anan nikurfunghe din nizun usadaka mine nanya kukuzenghe.
Da Yesu ya ɗaga ido, sai ya ga waɗansu masu arziki suna sa baikonsu a ma’ajin haikalin.
2 A yene umon uwani na ulese wa ku adin ti nikubu iba nanya kukuzunghe.
Ya kuma ga wata gwauruwa matalauciya, ta saka anini biyu.
3 Anin woro, “Kidegene mbelen minu, ule uwanin derun lese inta vat a kata anit ane.
Sai ya ce, “Gaskiya ina faɗa muku, wacce nan gwauruwa matalauciya ta sa fiye da dukan sauran.
4 Vat mene wani nanya nigbardan ile na idimun. Bara nani ule uwanin salin lese, wani nanya likimun me, vat nikurfun mere a wanutun.
Dukan mutanen nan sun ba da baikonsu daga cikin arzikinsu ne, amma ita daga cikin talaucinta, ta saka duk abin da take da shi na rayuwa.”
5 Nafo na amon waliru kutii nlira, nafo na ma kye nin natala acine nin sadaka, a woro,
Waɗansu daga cikin almajiransa, suka fara magana a kan yadda aka yi wa haikalin ado da duwatsu masu kyau, da kuma kyautai da aka keɓe wa Allah. Amma Yesu ya ce,
6 “Bara ile imune na idin yenju, ayiri ba dak na ima sunu nlon litala kitene nlong na ima sali sa uturne ba.”
“Wannan abin da kuke kallo a nan, lokaci yana zuwa da ba za a bar wani dutse a kan wani dutse ba. Kowannensu, za a rushe shi.”
7 Bara nani itiringhe, I woro, “Kumallami, nin shiyari ile imone ba ti?”
Suka tambaye shi suka ce, “Malam, yaushe waɗannan za su faru? Kuma wace alama za tă nuna cewa suna dab da faruwa?”
8 Yesu kawa, “Yenjen umon wada rusuzu minu Bara anit gbardan ba dak nin lisa ning, I din belu, 'Mere ame,' 'Kuben ndaa susut.' Na i wa dufin nani ba.
Ya amsa ya ce, “Ku lura, kada ku kuma a ruɗe ku. Gama da yawa za su zo a cikin sunana, suna cewa, ‘Ai, ni ne shi,’ da kuma, ‘Lokaci ya yi kusa.’ Kada ku bi su.
9 I wa lanza ubelen likum nin fizu nayi, na I wa lanza fiu ba, bara na ile imone ma dak nin burne, nara nani na liganghe nsa da ba.”
Sa’ad da kuka ji labarin yaƙe-yaƙe, da juye juyen mulki, kada ku tsorota. Dole ne waɗannan abubuwa su fara faruwa, amma ƙarshen ba zai zo nan da nan ba.”
10 Akuru a woro nani, “Nmgiin ma su likum nin umong nmgiin, kipin tigoo nin kan kipin tigoo.
Sai ya ce musu, “Al’umma za tă tasar wa al’umma, mulki zai tasar wa mulki.
11 Kutyene ma zullunu kang, nin nite gbardan kukpan ma yitu nin nijase tekanu tididya. Adadu fiyu ma yitu nin nalap adidya kitene kani.
Za a yi manyan girgizar ƙasa, da yunwa, da annoba a wurare dabam-dabam, da kuma abubuwa masu bantsoro, da manyan alamu daga sama.
12 Bara nani makin ile imoone vat, ima ti minu acara iti minu ayiasirne, ima du nin ghinu nanya ni larin nlira nin nilari licin, I ma du nin ghinu ubun tigoo nin nbun na gumna bara lisa ning.
“Amma kafin duk abubuwa nan, za a kama ku a tsananta muku. Za a kai ku majami’u, da kurkuku. Za a kuma kai ku gaban sarakuna da gwamnoni, kuma dukan waɗannan saboda sunana.
13 Uba soo kube na iba belu imoon icine ile na Kutelle nsuu minu.
Wannan zai sa ku zama shaidu a gare su.
14 Bara nani keleng nibinai mine na ima kesuzu ati mine udu kuni kube ba.
Amma ku yi ƙuduri, wato, ku shirya zuciyarku, a kan ba za ku damu ba kafin lokacin, game da yadda za ku kāre kanku.
15 Bara na nba ni minu tigbulan nin kujinjin, na vat anan nari mine wasa ita mayardan ku sa I kpiliya umon uleru ba.
Gama zan ba ku kalmomi, da hikima waɗanda ba ko ɗaya daga cikin maƙiyanku, za su iya tsayayya da ku, ko su ƙaryata.
16 Bara nani acef, nwana, adondon nin nakura ma nakpu minu, ima ti among mine ikuzu.
Har iyayenku, da’yan’uwanku maza, da danginku, da abokanku ma, duk za su bashe ku, su kuma kashe waɗansunku.
17 Ima nari minu bara lisa ning.
Duk mutane za su ƙi ku saboda ni.
18 Bara nani na liti titi mine lirum ma wulu ba.
Amma ko gashi ɗaya na kanku, ba zai hallaka ba.
19 Nenyan nteru nibinai mine I ba se imon kitene tilai mine.
Ta wurin tsayawa da ƙarfi, za ku sami rai.
20 I wa yene ikilino Urshalima nin nasoja, yinnong unanzwe nda susut.
“In kuka ga mayaƙa sun kewaye Urushalima, za ku sani rushewarta ya yi kusa.
21 Na ale na idin Yahudiya cum udu kitene natala, ale na idi nanya kipine kitik nuzu, na I wa yining a le na idi tikauye piru ba.
A lokacin nan, bari waɗanda suke Yahudiya, su gudu zuwa cikin duwatsu. Bari waɗanda suke cikin birnin kuma su fita, bari kuma waɗanda suke ƙauye kada su shiga birnin.
22 Bara na ale ayire an tunjuari, bara vat ni lee imon na ma yertin kulo.
Gama wannan shi ne lokacin hukunci, saboda a cika duk abin da aka rubuta.
23 Kash nawani ale na idin nin naburi kumat nin nalee na idin mazinu nono nanya na yiri ane! Bara na ijasi idya ma yitu nmgine, niin tinana nayi udu anite.
Zai zama abin kaito ga mata masu ciki, da mata masu renon’ya’ya, a waɗancan kwanakin! Za a yi baƙin ciki mai tsanani a ƙasar, da kuma fushi mai tsanani a kan mutanen nan.
24 Imanin mulsu nani nin kusangali ima soo alin nanyan nmgene vat, awurmi ma patilu Urshalima udu kubin kulu na wurmi.
Za a kashe su da takobi, a kuma ɗauke su’yan kurkuku, zuwa dukan al’ummai. Al’ummai za su tattaka Urushalima, har sai lokacin Al’ummai ya cika.
25 Kulap ma yitun nwui, nanyan mpoi, nin nanya niyinin, nin kitene nyii, nin puyu nati nmgen, nany nlazu fiyu ngurzunu na rawa adidya nin fune.
“Za a yi alamu a cikin rana, da cikin wata, da cikin taurari. A duniya, al’ummai za su yi baƙin ciki, su kuma rikice don tsoro, saboda ruri da kuma tafasar teku.
26 Anit ma kuzu ifiliza bara fuyu inca nimon ile na idin cinu kitene nyii. Bara na likara kitene kani ma zulunu.
Mutane za su suma don tsoro, za su kuma yi fargaba, a kan abin da yake zuwa a bisan duniya, gama za a girgiza duniyar taurarin sararin sama.
27 I ba nin yenu Gono nnit din cinu nanya na wut nin likara nin zazu udya.
A lokacin ne za su ga Ɗan Mutum yana zuwa cikin girgije, da iko, da ɗaukaka mai girma.
28 Bara nani ile imoone nwa cizin, fitan iyisin, inin ghantin ati mine, bara na utucu mine nda duru susut.”
Sa’ad da waɗannan abubuwa sun fara faruwa, ku tashi tsaye, ku ɗaga kawunanku, domin fansarku yana matsowa kusa.”
29 Yesu benle nani tiwankari, “Yenen kuca kupul nin nace vat,
Sai ya gaya musu wannan misali ya ce, “Ku dubi itacen ɓaure da dukan itatuwa.
30 I wa yene kuca kupul ngutuna afa apese din tilu I yino bara ate mine au kubi kusik nda susut.
A duk lokacin da sun fara fitar da ganye, za ku gani da kanku, ku san cewa, damina ta yi kusa.
31 Nanere, I wa yene ile imoone din dasu, yinong au kipin tigoo Kutelle nda susut.
Haka ma, in kuka ga waɗannan abubuwa suna faruwa, ku sani mulkin Allah ya yi kusa.
32 Kidegene, mbelinminu, na ko kuje a katu ba, se imoon ilelee nkulo vat.
“Gaskiya nake gaya muku, ba shakka, wannan zamani ba zai shuɗe ba, sai dukan waɗannan abubuwa sun cika.
33 Kitene kane nin nmgen ma katu vat, bara nani na ligbulan lirum nanya nlirunighe ma katu ba.
Sama da ƙasa za su shuɗe, amma kalmomina ba za su taɓa shuɗewa ba.
34 Bara nani, dinjan atuf nati mine, bara na nibinai mine wati getek nin na dadu ananzang, inyeu mso na dadu ahem, nin kpilizun nliru nyii, bara na lere wada muu minu,
“Ku lura fa don kada son jin daɗi na banza, da shaye-shaye, da damuwa na rayuwa su rinjayi zuciyarku, har ranar ta auko muku ba tsammani kamar tarko.
35 nafo libarda, bara na lima dak liti na nit vat nanan nlai na idi nanya inyii ulele.
Gama za tă zo a kan kowa da yake kan dukan duniya.
36 Bara nani, Punon iyizi vat kubi idin tizun nlira bara inan se agan kang inan cuo ile imoone na ima dak, inin yisin mbun Gono nit.”
Ku yi tsaro kullum, ku yi addu’a don ku iya kuɓuta daga dukan waɗannan abubuwa da suke kusan faruwa, don ku iya tsayawa a gaban Ɗan Mutum.”
37 Kubi ko na awadin dusuzu nanya kutii nlira nin kitwik a nuzu udas, anin moro kiten nlon litala na idin yicu litalan Zaitun.
Kowace rana, Yesu yakan je haikalin ya yi koyarwa, da kowace yamma kuma, ya je ya kwana a kan tudun da ake kira Dutsen Zaitun.
38 Anite vat da nin koi dindin inan lanzaghe nanya kutii nlira.
Da sassafe kuma, dukan mutanen suka zo haikalin, don su saurare shi.

< Luka 21 >