< Yuhana 16 >

1 Nbelin minu ile imone bara iwa ti minu itiro.
“Na faɗa muku wannan duka, domin kada ku bauɗe.
2 ima nutuzun minu nanya nilari nlira; kube din cinu kongo na alenge na ima molusu minu ma cissu idi su Kutelle katwa kacine.
Za su kore ku daga majami’a; lalle, lokaci yana zuwa da duk wanda ya kashe ku, zai ɗauka yana yin wa Allah hidima ne.
3 Ima su ileli imone bara na isa yinno Ucife sa menku ba.
Za su yi waɗannan abubuwa ne domin ba su san Uba ko ni ba.
4 Ndin belu minu ile imone bara asa kube nda na ima se, ima lizinu inin nin woru iyiziari nna belin minu. Na nna belinminu ubellenghe nin cizunue ba bara nwa di ligowe na ghinu.
Na faɗa muku wannan, domin in lokacin ya yi, ku tuna na gargaɗe ku. Ban faɗa muku wannan tun da fari ba domin ina tare da ku.
5 Nene nba du kiti nlenge na ana tuyi; vat nani, na umong mine ntirini ba. 'Udin cinu udu weri'?
“Yanzu zan tafi wurin wanda ya aiko ni, duk da haka ba waninku da ya tambaye ni, ‘Ina za ka?’
6 Bara na nna bellin minu ile imone, liburi lisirne nmal kulu nibinayi mine.
Saboda na faɗa waɗannan abubuwa ga shi kun cika da baƙin ciki.
7 Vat nani, nbeling minu kidegene; uma caunu minu meng nya; bara asa na nya ba, na unan bunue ma dak kitimine ba; ama nwan nya nma tughe kiti mine.
Amma gaskiya nake gaya muku. Don amfaninku ne zan tafi. Sai ko na tafi, in ba haka ba Mai Taimakon nan ba zai zo muku ba. Amma in na tafi, zan aiko shi gare ku.
8 Asa ada, unan bunue ma kpashulu uye nbeleng kulapi, nbeleng katwa kacine, nin beleng nshara.
Sa’ad da ya zo kuwa, zai kā da duniya a kan zunubi da adalci da kuma hukunci,
9 Nbeleng kulapi bara na ina yinnin nimi ba,
a kan zunubi, domin mutane ba su gaskata da ni ba;
10 nbeleng katwa kacine. Ndin cinu ucin du kitin Cif, na ima kuru iyene tutung ba.
a kan adalci, domin zan tafi wurin Uba, inda ba za ku ƙara ganina ba;
11 a ubeleng nshara, ina malu usu ugo nyii ulele ushara.
a kan hukunci kuma, domin an yanke hukunci a kan mai mulkin duniyan nan.
12 Ndin nin nimon gbardang na nma belin minu, na ima yinnu inin nene ba.
“Ina da sauran abubuwa da yawa da zan faɗa muku, amma ba za ku iya ɗauka a yanzu ba.
13 Vat nani, asa ame Uruhu kidegene nda, ama dofunu ninghinu nanya kidegene vat; bara na ama su uliru unlitime ba, ama vat nimon ile na alanza, nanere ama belu, amaa nin pun minu imon ile na idin cinu.
Amma sa’ad da shi, Ruhun gaskiya ya zo, zai bi da ku zuwa ga dukan gaskiya. Ba zai yi magana don kansa ba; zai faɗi abin da ya ji ne kaɗai, zai kuma faɗa muku abin da bai faru ba tukuna.
14 Ama tii gongong, ama yiru imon ning a pun minu inin.
Zai kawo ɗaukaka gare ni ta wurin ɗaukan abin da yake nawa, ya bayyana muku.
15 Vat ligang nimon ile na Uci dumun. inaghari, unnare nbelle, Uruhu ma yiru imon ning ada pun minu inin.
Duk abin da yake na Uba nawa ne. Shi ya sa na ce, ‘Ruhun zai ɗauko daga abin da yake nawa, yă bayyana muku.’”
16 Nin kubiri bat, ima kuru iyene ba; nin kubiri bat tutung, ima kuru iyenei.”
Yesu ya ci gaba da cewa, “Jim kaɗan, ba za ku ƙara ganina ba, sa’an nan bayan an jima kaɗan kuma, za ku gan ni.”
17 Among nono katwa me woro nadon mine, “Uyapin uliruari ulele na aworo nari, 'nin kubiri bat, na ima kuru iyenei ba; aminin woro tutung nin kubiri bat tutung, ima yenei,' tutung, 'Bara nma du kitin Ncifa?'
A nan fa sai waɗansu almajiransa suka ce wa juna, “Me yake nufi da cewa, ‘Jim kaɗan ba za ku ƙara ganina ba, kuma bayan an jima kaɗan, za ku gan ni,’ da kuma, ‘Domin zan tafi wurin Uba’?”
18 Inin woro, “Iyaghari ilele a belle, 'Kubi cingiling'? Na tiyino iyaghari adin belu ba.”
Suka yi ta tambaya, “Me yake nufi da ‘jim kaɗan’? Ba mu fahimci abin da yake faɗi ba.”
19 Yesu yene idin shotu itiringhe, ame woro nani, “Idin tiru atimine ubelen nileli imone, nworu 'Nin kubi bat, na ima kuru iyenei ba; kimal kubi bat tutung, ima yenei'?
Yesu ya gane suna so su tambaye shi game da wannan, sai ya ce musu, “Kuna tambayar juna game da abin da nake nufi da na ce, ‘Jim kaɗan ba za ku ƙara ganina ba, da kuma bayan an jima kaɗan, za ku gan ni’?
20 Kidegenere, ndin belu minu, ima su kuculu nin lidurun, ama uye masu liburi libo, anung masu liburi lisirne, ama liburi lisirne mine ma kpinlu ayi aboo.
Gaskiya nake gaya muku, za ku yi kuka da kuma gunji, yayinda duniya take murna. Za ku yi baƙin ciki, amma baƙin cikinku zai koma farin ciki.
21 Uwani asa asu liburi lisirne andi adi nin konu liburi kumat bara kubin nlolu me nda; ama asa amara gone, asa a lizino uniu me ba bara ayi aboo nworu imara gono nanya in yii.
Macen da za tă haihu takan yi naƙuda domin lokacinta ya yi; amma sa’ad da ta haihu, sai ta manta da wahalar domin farin ciki an haifi jariri a duniya.
22 Nanere anung wang, idi nin naburi asirne nene, ama meng ma kuru inyene minu tutung, ima ti ayi abo.
Haka ku ma, yanzu ne lokacin baƙin cikinku, amma zan sāke ganinku za ku kuma yi farin ciki, ba kuwa wanda zai ɗauke muku farin cikinku.
23 Liri lole, ima sui umon utirinu ba, kidegenere, Ndin belu minu, asa itirino imonmong kitin Cif, ama ni minu inin nanya lissa ning.
A ranan nan, ba za ku sāke tambaya ta kome ba. Gaskiya nake gaya muku, Ubana zai ba ku kome da kuka roƙa cikin sunana.
24 Udu da duru nene na isa tirrino imonimon nya lissa ning ba; tirinon, tutung ima seru, liburi libo mine manin kulu.
Har yanzu dai ba ku roƙi kome cikin sunana ba. Ku roƙa za ku kuwa samu, farin cikinku kuwa zai zama cikakke.
25 Nsu minu ule ulire nin tinan tigoldo, ama kubi din cinu na nma kuru nsu minu uliru nin tinan tigoldo ba, ama nma na su minu kanang nbeleng Ncife.
“Ko da yake ina magana da misalai, lokaci yana zuwa da ba zan ƙara yin magana da misalai ba, sai dai in faɗa muku a fili game da Ubana.
26 Nloli lire, ima tirini nya lissa ning, a na nworo minu nba ti nlira kiti Ncif bara anung ba;
A ranan nan, za ku roƙa a cikin sunana. Ban ce zan roƙi Uba a madadinku ba.
27 ame Ucife di nin sumine, bara na anung di nin su nin, inani nyinna nin mi bara na nna dak unuzu kiti Ncife.
Ai, shi Uban kansa yana ƙaunarku domin kun ƙaunace ni kun kuma gaskata cewa daga Allah na fito.
28 Nna dak unuzu kiti Ncif, nmini na dak nanya yii ulele tutung, Nma sunu uyei nma kpilu ndo kiti Ncife.”
Na fito daga wurin Uba, na kuma shigo duniya, yanzu kuwa zan bar duniya in koma wurin Uba.”
29 Nono katwa me woro, “Yene nene udin liru kanang; na udin liru nin tinan tigoldo ba.
Sai almajiran Yesu suka ce, “Haba, yanzu ne fa kake magana a sarari ba tare da misalai ba.
30 Nene ti yinno uyiru imon vat, ana udin pizuru umong tirifi umong uliru ba. Bara nani ti yinna una dak unuzu kiti Kutelle.
Yanzu mun gane cewa ka san kome ba sai wani ya tambaye ka ba. Wannan ya sa muka gaskata ka fito daga Allah.”
31 Yesu kawa nani aworo, “Nene iyinna?”
Yesu ya amsa ya ce, “A ƙarshe kun gaskata!
32 Yenen kubi din cinu, nanere, nene kumal dak, na ima malu kiti, kogha mine udu kiti me, ima nin sunui Ussanii. Vat nani na nma yitu ussanin, bara Ucif ma yittu nin mi.
Amma lokaci na zuwa, har ma ya yi, da za a warwatsa ku, kowa yă koma gidansa. Za ku bar ni ni kaɗai. Duk da haka ba ni kaɗai ba ne, gama Ubana yana tare da ni.
33 Nsu minu ulenge ulire bara nme inan se lissosin lisheu. Nanya nyie idi nin tinanayi, ama sen likara nibinayi, Meng na li likara nyie.”
“Na faɗa muku waɗannan abubuwa ne, domin a cikina ku sami salama. A duniyan nan za ku sha wahala. Amma ku yi ƙarfin hali! Na yi nasara a kan duniya.”

< Yuhana 16 >