< Yakubu 4 >

1 Nweri kabung nin diru yinnu nin nati ku nanya mine? na kudin fitizu nan nya mine unucu nlip nibinai ni nanzang na udin su likum nan nya mine ba, linuwa anan yinnu nin kutellẹ ba?
Me yake jawo faɗace-faɗace da gardandami a tsakaninku? Ashe, ba sha’awace-sha’awacenku da suke yaƙi a zukatanku ba ne?
2 Idin nlip nimon ille na idumun ba, idin molsu ikuru ipizira imon ile na i wasa ise ba. Idin su nnun.
Kukan nemi abu ku rasa, sai ku yi kisa da ƙyashi. In kuka rasa abin da kuke nema sai ku shiga yin gardama da faɗa. Kukan rasa ne, domin ba ku roƙi Allah ba.
3 Isu kabung ku, vat nani na isebabura na itirino kutellẹ ba. Idin tiru a na i sare ba, bara idin ntiru imon inanzang, inan moluso libau nsu nibinai mine.
Sa’ad da kuka roƙa, ba kwa samu, don kun roƙa da mugun nufi, don ku kashe abin da kuka samu a kan sha’awace-sha’awacenku.
4 Anung anam zina! akilaki, Na iyiru nwoni lidondong nin yih ulele nshinari nin kutellẹ ba? Bara nani ulle na ayinna asu lidondon nin yih a durso litime unan shina Kutellẹ.
Ku mazinata, ba ku san cewa abokantaka da duniya gāba ce da Allah ba? Duk wanda ya zaɓa yă zama abokin duniya ya zama abokin gāban Allah ke nan.
5 Sa idin cissu uliru Kutellẹ naso lem na unaworo uruhu Kutellẹ na ina ti nan nyo bite ukulun nin lip liyarin na?
Ko kuna tsammani a banza ne Nassi ya ce ruhun da ya sa yă zauna a cikinmu yana kishi sosai?
6 Nan nya nani Kutellẹ na nani ubolu me gbardang, bara na uliru Kutellẹ na woro, “Kutellẹ nari anan tikunang liti, ana niza ubelu me kiti nale na itoltuno uti mine”.
Amma yakan ba mu alheri a yalwace. Shi ya sa Nassi ya ce, “Allah yana gāba da masu girman kai amma yakan ba da alheri ga masu tawali’u.”
7 Bara nani, nan ati mine kiti Kutellẹ, taan shakk nin nshaitan, a nan nya pit nan ghinu.
Saboda haka, ku miƙa kanku ga Allah. Ku yi tsayayya da Iblis, zai kuwa guje ku.
8 Dan susut nin Kutellẹ, amac wang ma daksusul nan ghinu, kusun achare mine lau anung anan nalapi, wesen nibincu mine, anung anan nibinayi nibaba.
Ku matso kusa da Allah shi kuwa zai matso kusa da ku. Ku wanke hannuwanku, ku masu zunubi, ku kuma tsarkake zukatanku, ku masu zuciya biyu.
9 Sun liburi lisirne a tiyom nin kuculu. Kpilliyan tisina mine ti tinana nayi, so ulanzun nmang mine lawa liburi lisirne.
Ku yi baƙin ciki, ku yi makoki ku kuma yi kuka. Ku mai da dariyarku ta zama makoki, farin cikinku kuma yă zama ɓacin zuciya.
10 Toltunon atimine nbun Ncikilari Ame ma ghantin minu.
Ku ƙasƙantar da kanku a gaban Ubangiji, zai kuwa ɗaukaka ku.
11 Na iwansu kubellum natimine ba, linuana, unit ulle na asu kubellum ngwana sa ushariya ngwana, adin su ushara nan nyan nshara Kutellẹ. Asa usu uduka ushara fe wang na una dortu nsharawere ba, fe nso sharan nin nari.
’Yan’uwa, kada ku ɓata wa juna suna. Duk wanda ya zargi ɗan’uwansa ko ya ɗora masa laifi, yana gāba da doka ne yana kuma yin mata shari’a ke nan. In kuwa ka ɗora wa shari’a laifi, kai ba mai binta ba ne, mai ɗora mata laifi ne.
12 Unit urumari cas unan nizun duka nin shariyawe, ame Kutellẹ, ulle na amere wasa asu utucu nin molsu, fe ghari, unan su ndọ lissan fe ushara?
Akwai Mai ba da doka da kuma Alƙali guda ɗaya tak, shi ne yake da ikon ceto da kuma hallakarwa. Amma kai, wane ne da za ka hukunta maƙwabcinka?
13 Lanza fe ulle na udin bellu, “Kitimone sa udun kwoi tiba du nanya kipin, ti duru likus kikans, ti di su kujauna tise uriba”.
Yanzu fa sai ku saurara, ku da kuke cewa, “Yau ko gobe za mu je wannan ko wancan birni, mu yi shekara a can, mu yi kasuwanci, mu ci riba.”
14 Ghari yiru imon ille na ina se ninkwui, iyaghari ulai mine? Idi nafo ulonna3i na sas unuzu nin kubiri bat umala kiti.
Alhali kuwa ba ku ma san abin da zai faru gobe ba. Wane iri ne ranku? Ku kamar hazo ne da yake bayyana na ɗan lokaci sa’an nan yă ɓace.
15 Bara nani mbara iworo nengbe “asa cikilari inyinna tiba yitu nin lai tisu ilenge sa ileli.
A maimakon haka, ya kamata ku ce, “In Ubangiji ya yarda, muna kuma a raye, za mu yi wannan ko wancan.”
16 Nene idin fo figiri nin zkpilizu mine, vat ulle ufo figire unanzanghari.
Ga shi, kuna fariya da taƙama. Duk irin wannan taƙama mugun abu ne.
17 Bara nani kitin nle na ayiru usu nimon icine amini nari usue, kitime kulapiyari.
Saboda haka, duk wanda ya san abu mai kyan da ya kamata yă yi, bai kuwa yi ba, ya yi zunubi ke nan.

< Yakubu 4 >