< Uafisawa 4 >

1 Bara nanin meng fa, nafo kucin ncikilari ndin fo minu nachara, sun ucin imusun nllenge na yicila munu.
A matsayina na ɗan kurkuku saboda Ubangiji, ina roƙonku ku yi rayuwar da ta dace da kiran da aka yi muku.
2 Nin toltinu liti ichang, Ayi ashew, iseru anit vat nin suu.
Kullum ku kasance masu sauƙinkai da kuma hankali; ku zama masu haƙuri, kuna jimrewa da juna cikin ƙauna.
3 Suing ille imon na iba suu vat inan iso ligawe nan nya nbolu Kutellẹ nin lisosin limang.
Ku yi ƙoƙari sosai ku kiyaye zaman ɗayan nan da Ruhu ya ba ku, ku yi haka ta wurin zaman lafiya da juna.
4 Kidowo kirum, duku, infip milau mirum, nafo na iwa yicilla munu nin likara kibineyi nin tikibineyi nyicilu.
Dukanku jiki ɗaya ne, kuna kuma da Ruhu guda. An ba ku bege guda sa’ad da aka kira ku.
5 Tidin cikilariuwa rum, uyinnu sa uyenu urum, usul sunu ulau urum,
Ubangiji ɗaya, bangaskiya ɗaya, baftisma kuma ɗaya,
6 Kutellẹ kurum uchifing nvat, ame ulle na adi kitene vat, nan nya nvat a imon vat.
Allah ɗaya Uban duka, wanda yake a bisa duka, ta wurin duka, a cikin duka kuma.
7 Ina ni kogha ku nan nya bite, udu diu gbardang nafo na Kristi na guchu.
Amma ga kowannenmu an ba da alheri bisa ga yadda Kiristi ya rarraba.
8 Nafo na uliru Kutellẹ na belling, kubi ko na awa ghana kitene kani, apizira ligozin nancin na idi nanya licin asuu anit mafilzunu filzunu.
Shi ya sa aka ce, “Sa’ad da ya hau sama, ya bi da kamammu kamar tawagarsa ya kuma ba da baye-baye ga mutane.”
9 Ulle ullire pa, “Awa ghana kitene kani,” din nnufi nworu, se akuru a pira nan nya nchachom kutina?
(Me ake nufin da “ya hau,” in ba cewa dā ya sauka can ƙarƙashin ƙasa ba?
10 Ame ullenge na ana tolu nchanchom kitin amere ullenge na anakuru aghana kitene nitene anan kullo imon vat.
Shi wannan da ya sauka ɗin, shi ne kuma ya hau zuwa can sama, kai, gaba da sammai, don mulkinsa yă cika duniya gaba ɗaya.)
11 Yisa wasu nafilzinu filzinu fone: among nono kadura, anan nliru nin nnu Kutellẹ, anan nuchu nbellin uliru Kutellẹ, anan libiya, nin nan dursuzu.
Saboda haka Kiristi kansa ya ba wa waɗansu baiwa su zama manzanni, waɗansu su zama annabawa, waɗansu su zama masu wa’azi, waɗansu kuma su zama fastoci, da kuma malamai.
12 Bara inan kulo nanin nin nimon katah Kutellẹ bara kye kidowon Kristi.
Ya yi haka don yă shirya mutanensa saboda ayyukan hidima, don a gina jikin Kiristi.
13 Udu kubi ko na tima se umunu nati nan nya nyinnu sa uyenu nin yina ngonoo Kutellẹ. Tiduru likulung nnit nafo allenge ikuno nin yiru ngono Kutellẹ.
Wannan zai ci gaba har sai mun zama ɗaya a cikin bangaskiya da kuma ta wurin fahimtarmu na Ɗan Allah. Sa’an nan za mu zama balagaggu, kamar yadda Kiristi yake, mu kuma zama gaba ɗaya cikakku kamar sa.
14 Udina ni natiwa libuung lisosin nafo nono. Allenge na ufunu din killu kiti nu ghinu anan yiru nbellu nliru nwultunu kiti.
An yi wannan kuwa don kada mu koma zama kamar yara, muna ta canja zukatanmu game da abin da muka gaskata don kawai wani ya faɗa mana wani abu dabam, ko domin wani ya yi wayo ya ruɗe mu, ya sa ƙarya ta zama kamar gaskiya.
15 Tima bellu kidegen nan nya nsuu me, tinau kuno nan nya mme na amere liteh, amere Kristi.
Ya kamata kullum ƙauna tă sa mu faɗa gaskiya. Ta haka za mu yi girma a kowace hanya, mu kuma zama kamar Kiristi, wanda yake kan
16 Ulle na nidowe nanan ndortine dofin kitine vat, nidowo mine munno tafat nan nati, naffo na kokome kubiri na ina fuloghe katane nan nya kitin nkunju kidowo, bare ukye nanit vat nan nya nsu.
dukan jiki. Shi ne ya haɗe jiki duka, ya kuma sa dukan gaɓoɓin jiki suna aiki daidai, yayinda kowace gaɓa take aikinta cikin ƙauna.
17 Bara nanere imon ille nan belling munu, indin dursu minu nan nya ncikilari: na iwaa lawan ncine nafo awurme ba nan nya katah mine kalan.
To, ina dai faɗa muku, ina kuma nace faɗa muku a cikin Ubangiji, cewa kada ku ci gaba da yin rayuwa kamar yadda Al’ummai suke yi, masu banzan tunani.
18 Anan kpilizu nan nya nsirti. Alle na ina ina nutun nanin nan nya nlai kutellẹ bara utani ulle na udin nan nya mine nin gbas nibineyi mine.
Suna a cikin duhu a fahimtarsu, kuma a rabe suke daga ran Allah saboda jahilcin da yake cikinsu ta dalilin taurarewar zukatansu.
19 Alle na itah gbas inani nnapka ati mine nan nya nimon izenzen nan nya nsuu nimon vat bara litime.
Ba sa damu da wani abu ko mai kyau ko marar kyau. Rayukansu sun cika da kowace irin ƙazanta da haɗama.
20 Na nanere ina piziru uyinnu mbellen nKristi ba.
Amma ba abin da aka koya muku ke nan ba sa’ad da kuka zo ga sanin Kiristi.
21 Andi ina lanza ikuru idursuzo minu ubelleng ise, nafo na kidegen di nan nya nKristi.
Da yake kun ji duka game da shi, kuka kuma koyi gaskiyar da take cikin Yesu,
22 Sa iyinin sa inari kalan unit ukuse ullenge na udi nin lidu likuse, na idin kpilzinu unanuzu nanya nrusuzu kiti nin suu liti.
sai ku tuɓe tsohon mutumin nan naku da kuma rayuwarku ta dā, wadda take lalacewa saboda sha’awace-sha’awacen da suke ruɗe ku.
23 Bara inan so apese nan nya nfulu ulau nibineye mine.
A maimakon haka, bari Ruhu yă sabunta tunaninku da kuma halayenku.
24 Shonon unit upese, ullenge na Kutellẹ. Nakye ghe libo nfiu Kutellẹ nin lau kidegen.
Ku sanya sabon halin nan da aka halitta bisa ga kamannin Allah, halin nan kuwa, yă bayyana cikin adalci, da zaman tsarki.
25 Bara nani, sunan kinu belleng atti kidigen, arik tigap kidowo kirumari.
Saboda haka dole kowannenku yă bar yin ƙarya, yă kuma riƙa faɗa wa maƙwabcinsa gaskiya, gama dukanmu gaɓoɓi jiki ɗaya ne.
26 Assa ayi nnana munu na iwa ti kulapi ba, “Na iwa yinin uwui diu a iyita nin tinana naye ba.”
“Cikin fushinku kada ku yi zunubi.” Kada ku bar rana ta fāɗi kuna fushi,
27 Bara iwa ni shitan ku kiti.
kada kuma ku ba wa Iblis dama.
28 Ullenge na adin suu likiri na awa kura asuu likire ba, nani na asuu katah katah kacine nin nachara me, anan se abuno unan diru.
Duk wanda yake sata, sai yă daina sata, dole kuma yă yi aiki, yă yi wani abu mai amfani da hannuwansa, don yă sami abin da zai iya raba da masu bukata.
29 Na uliru unanza nwa nuchu tinu mine ba, nworu nani, tigulang ticine to na tiba kye among alle na idin pizure, anan lanze nanse ubolu Kutellẹ.
Kada wata ƙazamar magana ta fita daga bakunanku, sai dai abin da yake da amfani don gina waɗansu bisa ga bukatunsu. Ta haka maganarku za tă zama da amfani ga masu jinta.
30 Na iwa lanza ufunu alau Kutellẹ ayi ba, ullenge na ina yaci minu ninge udu lirin tuchu.
Kada kuma ku ɓata wa Ruhu Mai Tsarki na Allah rai, wanda da shi aka hatimce ku da shi don ranar fansa.
31 Nutunon vat ngbagbai nayi, tinan nayi tikhang, ughantizunu tiwui tinanza nin tizogo nutunong imon ine vat nin katahh kananzang.
Ku rabu da kowane irin ɗacin rai, haushi da hasala, faɗa da ɓata suna, ku rabu da kowace irin ƙeta.
32 Suuug ayi asheu nin nati mine, nin ni beneyi ni nese, ishauza nin na lapi nati, nafo na Kutelle nan nyan nKristi na shawa nin na lapi bite sa ubizu.
Ku yi alheri, ku kuma ji tausayin juna, kuna gafarta wa juna, kamar yadda a cikin Kiristi, Allah ya gafarta muku.

< Uafisawa 4 >