< Ukolosiya 1 >

1 Bulus, unan kaduran Yesu unuzu nyinnu Kutelle, nin Timoti gwana bit,
Bulus, wanda Allah ya zaɓa don yă zama manzon Kiristi Yesu, da kuma daga Timoti ɗan’uwanmu,
2 udu kiti nalege na Kutelle na fere nani, alenge na ina ni nibinai mine kitin Yesu, ale na idi Nkolosiya. Ubolu Kutelle nin lisosin limang nnuzu Kutelle Ucif bit.
Zuwa ga tsarkaka da kuma amintattun’yan’uwa cikin Kiristi da suke a Kolossi. Alheri da salama daga Allah Ubanmu, su kasance tare da ku.
3 Tidinin liburi liboo kiti Kutelle, Ufin Yesu Kristi, ti din suu minu nlira kokome kubi.
Kullum muna gode wa Allah, Uban Ubangijinmu Yesu Kiristi, sa’ad da muke addu’a dominku.
4 Tina lanza uyinu mine sa uyenu nanya Yesu Kristi, nin suu kiti na lena Kutelle nafere nani.
Gama mun ji labarin bangaskiyarku a cikin Yesu Kiristi da kuma ƙaunar da kuke yi saboda dukan tsarkaka.
5 Bara uni kibinai nghinua, nin ciu nanyi mine kiti nimong ile idi kitene kan, anughe wa cizin ulanzu ubelen nni nibinai nine unuzu ligbulang kidagen, ullirun nlai.
Kuna yin haka ne kuwa domin abin da kuke bege yana a ajiye a sama. Kun riga kun ji game da wannan bege sa’ad da kuka gaskata saƙon nan na gaskiya wanda shi ne bisharar
6 Ulenge na una dak kitimine, nafo ulenge na adin macu, akunjo vat inye, nafo na anughe ditutung, uyire liyiru longo na iwa lanza, ida yinno nkunekune Kutelle nanya kidegen mye.
da ta zo muku. Ko’ina a duniya wannan bishara tana yi ta haihuwa tana kuma girma, kamar yadda take yi a cikinku tun daga ranar da kuka ji ta kuka kuma fahimci alherin Allah cikin dukan gaskiyarta.
7 Udi nafo na iwa lanza kitin Abafras, udon licin bite ule na adi kucin kulau ku Yesu kitimine.
Kun koyi wannan gaskiya daga wurin Efafaras, ƙaunataccen abokin hidimarmu, wanda yake amintacce mai hidimar Kiristi a madadinmu,
8 Ame ule na ana puun nari usu mine nanya Nfip milau.
wanda kuma ya faɗa mana ƙaunar da kuke yi cikin Ruhu.
9 Bara ule usuwe unuzu liyiri longo na tiwa lanza ubellen minu nati sunan nlirang nin tirinu nworo uyinnu kullo munu nin se nyinnunu nanya nn Ufip milau.
Shi ya sa tun daga ranar da muka sami labarin, ba mu fasa yin addu’a dominku ba. Kullum muna roƙon Allah yă sa ku san kome da yake so ku yi, domin ku sami hikima ta Ruhu, ku kuma sami ganewar kome duka.
10 Anit din nliran nworo ucin mine cinu dert, nin vat, nafo na iba macu nanya liddu licine nin nkunju mine nanya nyinu Kutelle.
Ta haka za ku yi rayuwa wadda ta dace da Ubangiji, ku kuma gamshe shi a ta kowace hanya, kuna yin aiki mai kyau ta kowace hanya, kuna kuma yin girma cikin sanin Allah.
11 Tidin nliran nworo vat nile imong na idin suwe, nanya likara nzinu mye, una dorfino nin ghinu nanya ncin nibinai mine nin nayi ashau
Allah yă ƙarfafa ku da dukan iko bisa ga ɗaukakar ƙarfinsa domin ku kasance da jimrewa sosai da kuma haƙuri, cikin farin ciki
12 Tidin nlira nworo ule imone yita iba zazinu Ucif bite nin nayi aboo ulenge na atanari tinanin nbatina ulii ngadu nanya anan yinu sa uyenu nanya uhaske.
kuna gode wa Uba, wanda ya sa kuka cancanci ku sami rabo a gādon tsarkaka a cikin mulkin haske.
13 Ana bolu nari nanya likara nsirti, anin kpiliya nari udu kitetne tigo Ngono me nayi mye.
Gama ya riga ya cece mu daga mulkin duhu ya kuma kawo mu cikin mulkin Ɗan da yake ƙauna,
14 Nanya Ngono mere tina se utucu nin nshawu kulapi.
wanda ta wurinsa muka sami fansa da kuma gafarar zunubai.
15 Gone amere tina se utucu nin shawu na lapi bite
Kiristi shi ne surar da ake gani na Allah wanda ba a iya gani, ɗan fari a kan dukan halitta.
16 Bara kitimere iwa ke imong vat ilengene na idi kitene kani nin nilenge na idi inye vat, ulenge na idin yenju nin nilenge nsalin nyenju, sa kuteet tigo, sa uminu kipin, sa tigo vat nimon amere wa kee bara litime.
Ta wurinsa aka halicci dukan abu, abubuwan da suke cikin sama da abubuwan da suke a duniya, waɗanda ake gani, da waɗanda ba a gani, ko kursiyoyi ko ikoki ko masu mulki ko hukumomi; an halicci dukan abu ta wurinsa da kuma dominsa ne.
17 Ame di ubun nin ko iyang, nanya mere ko iyang di kiti kirum.
Ya kasance kafin dukan abu, kuma a cikinsa ne dukan abubuwa suke a harhaɗe.
18 Amere liti nanit mye, kidowo mye amere unan cizinu likara, kumat ncizinu nanya na nan nkul, adinnin kitin ncizunu nanya nimon vat.
Shi ne kuma kan ikkilisiya, wadda take jikinsa. Shi ne mafari da kuma na farko da ya tashi daga matattu, domin a cikin kowane abu yă zama mafifici.
19 Nanere bara una poo Kutelle liburi a kpiliya, nworo vat nkullu nimon nan so kitimye.
Gama Allah ya ji daɗi yă sa dukan cikarsa ta kasance a cikin Kiristi,
20 Anan keele imon vat unuzu ngono mye udu kiti mye, Kutelle wa su nani kubi na awa keele ko iyang unuzu mmi Ngono mye na iwa gutun kitene nbanu kutea, sa imon inyi sa kitene kan.
ta wurin Kiristi ne ya komar da kome zuwa ga kansa. Ya kawo salama ga abubuwan da suke ƙasa da abubuwan da suke sama, ta wurin jinin Kiristi da ya zubar a kan gicciye.
21 Au anung wang nkon kubi, iwadi amara kitin Kutelle, iwa di anan nivira mye nanya nibinai nin katwa kananzang.
A dā kuna a ware da Allah, kuka kuma zama abokan gāba a cikin tunaninku saboda mugun halinku.
22 Udak nene Kutelle wa munu minu kitene kidowo Yesu kin nkul, ankpa min annit alau, anan sali nimong tizogo anan sali nnanu lidu nbun mye.
Amma Ɗansa ya zama mutum ya kuma mutu. Saboda haka Allah ya yi sulhu da ku, yanzu kuwa ya bar ku ku tsaya a gabansa da tsarki, marasa aibi, da kuma marasa abin zargi.
23 Andi tutun anughe ashono ati nanya nyinu sa uyenu anan liyisi nari gagang, na ana nworo iba kalu nani kiti katwa Kutelle na ina latiza ulenge na inasu uwa azi nin vat makeke na udi kadas, meny tutun na ina tii nso unan katuwa meng Bulus.
Sai ku ci gaba cikin bangaskiyarku, kuna tsaye a kafe kuma tsayayyu, ba tare da gusawa daga begen da kuka ji daga bishara ba. Wannan ita ce bisharar da kuka ji wadda aka yi shelarta ga kowace halittar da take ƙarƙashin sama, wadda kuma ni Bulus, na zama mai hidimarta.
24 Idinin liburi liboo nin nniu nighe bara anughe, nkulun ile imonghe na idarni nin lanzu nkul nama kidowo Yesu na unere ana dortu mye.
Yanzu, ina farin ciki saboda wuyar da nake sha dominku, don ta wurin wuyan nan zan cika abin da ya rage na wuyar da Kiristi ya sha saboda jikinsa, wato, ikkilisiya.
25 Nwwasu katwa kutyi nliran dert nin katwa kutelle ka na iwa nii bara anughe uliru Kutelle nan kullo.
Na zama mai hidimar ikkilisiya bisa ga aikin nan da Allah ya ba ni amana saboda ku, domin in sanar da maganar Allah sosai.
26 Kidegen ka na kiwa nyeshin nin nakus piit udu kuji kidung na kudi ncinu, bara nene ina puun kti nanit alau mye. (aiōn g165)
Wannan magana da nake gaya muku asiri ne da yake a ɓoye tun zamanai masu yawa, wanda yanzu aka bayyana ga tsarkaka. (aiōn g165)
27 Anughere ale na Kutelle wa yinin a belle nani ko iyagari use nkanang micine mongo na midi nanya nanit. Ame Kristi na adi nanya mine amere uciu kibinai ngongong mine.
Su ne Allah ya so yă sanar da yadda irin yalwar ɗaukakar asirin nan take a cikin al’ummai, asirin nan kuwa shi ne Kiristi a cikinku, begen ɗaukakar da za a bayyana.
28 Amere ulele na tidin su nin lisa mye, tidin gbaru ko gha ku, ti dursuzo ko gha ku nin vat nyiru unan so dert kitin Yesu.
Saboda haka ko’ina muka tafi, muna shela, muna gargaɗi, muna kuma koyar da kowa da dukan hikima, don mu miƙa kowa cikakke a cikin Kiristi.
29 Nenere ndi katuwa nin nfo kidowo bara katwa mye ka na atii ndi suwe nin likaraa.
Don haka ne ina fama, ina kuma ƙoƙari da duk ƙarfin nan da Kiristi ya ba ni.

< Ukolosiya 1 >