< Katwa Nono Katwa 24 >

1 Na ayiri atat in kata, Ananiyas udya na Priest, among akune nin, nin mong una yirun liru lissame Teritullus, nya udu kite. Ale anite da nin vurun liru litin Bulus.
Bayan kwana biyar sai Ananiyas babban firist ya tafi Kaisariya tare da waɗansu daga cikin dattawa da kuma wani lauya mai suna Tertullus, suka kawo ƙararsu game da Bulus a gaban gwamna.
2 Na Bulus in yissina in bun gumne, Teritullus tunna aghanan vurzughe in liru aworo ugumne, “Bara fe tidi nin lissosin limang; tutung ukpiluzung in bunfe in danin nimon icene in nmyen bit;
Sa’ad da aka shigo da Bulus, sai Tertullus ya shiga kai ƙararsa a gaban Felis yana cewa, “Mun daɗe muna zaman lafiya a ƙarƙashinka, hangen nesanka kuma ya kawo gyare-gyare a wannan ƙasa.
3 nani nin godo udya tikpana vat nin nimon ilenge na usu, Felix uniti udindya.
Ko’ina da kuma a kowace hanya, ya mafifici Felis, mun amince da wannan da godiya marar iyaka.
4 Bara na ayedi in yissafi kang ba, indin potufi acara, lanzai baat nin kunene.
Amma don kada in ƙara gajiyar da kai, ina roƙonka ka yi haƙuri ka saurari ɗan taƙaitaccen jawabinmu.
5 Bara tikpaghe nin kulapin tizu na Yahudawa vat nanya nyii inari uduka. Amere udya nanan dortu kunan Nazeret.
“Mun tarar da wannan mutum fitinanne ne, yana tā-da-na-zaune-tsaye a tsakanin Yahudawa ko’ina a duniya. Shi shugaban ɗarikar Nazarawa
6 Amani mala uti kutii inlira kudyawe facak; unare tinani kpaghe.
har ma ya yi ƙoƙari ya ƙazantar da haikali; shi ya sa muka kama shi.
7 Amma ugo likume Lisiyas wa dak, a da kpalkinghe nin likara na cara bite.
8 Asa utiro Bulusku kitenen tipinpin tone, fewang manin yinnu imon irika na tidin bellu litime.”
Ta wurin bincika shi da kanka za ka gane gaskiyar game da dukan waɗannan zargin da muke kawo a kansa.”
9 A Yahudawe ligowe vat joro Bulus iworo, uliru ulele kidegenghari.
Yahudawa ma suka goyi bayan zargin, suna tabbatar cewa waɗannan abubuwa haka suke.
10 Ama na ugumne woro Bulus ku alirin, Bulus kawa, “Inyinno nwo fedi unan mawucuwucu nmyen mone inworsu, bara nani nin kibinayi kibo inma bell uliru litining.
Da gwamna ya yi masa alama yă yi magana, sai Bulus ya amsa ya ce, “Na san cewa ka yi shekaru da yawa kana mulki a wannan ƙasa; saboda haka ina farin ciki in kāre kaina.
11 Use uyinnu in woro na isa kata ayiri likure nin naba ba nin duning u'Urushalima indi su usujada;
Da sauƙi za ka iya tabbatar cewa, bai fi kwana goma sha biyu da suka wuce ne na tafi Urushalima, domin yin sujada ba.
12 na inung wase mengku nanya kutii in lira kudywe, na meng wasu mayardang nin mong mine ba, tutung na meng na tulu ligozin nanit ba, na inansu nani kutii in lira kudywe ba, a na inna su nani nanya kagbri ba;
Masu zargina ba su same ni ina gardama da kowa a haikali, ko kuma ina tā da hankalin jama’a a majami’u ko kuwa wani wuri dabam a cikin birni ba.
13 tutung na inung wasa durofi ulire na idin vuszi mung ba nene.
Ba kuwa za su iya tabbatar maka ƙarar da suke yi yanzu a kaina ba.
14 Ama meng yinna nbunfe nworu, kitene libauwe na inung din yiccu umon ubi, in loli libau lirumere ndin su Kutelle nacif ning katwa. Meng di lau nanya vat nimon ile na idin duka nin nana liru nin nuu Kutelle.
Amma na yarda cewa ina bauta wa Allah na kakanninmu a matsayin mai bin Hanyar da suke kira ɗarika. Na gaskata dukan abin da ya amince da Doka da yake kuma a rubuce cikin Annabawa,
15 Meng dinin yinnu urumere kiti Kutelle, nafo na ale anite din caa ndakin fituzu nanan kul, nan vat nanit alau nin nanan dinong;
ina kuma da irin bege ɗaya ga Allah yadda mutanen nan suke da shi, cewa akwai tashin matattu masu adalci da masu mugunta duka.
16 tutung nanya nile imon, ndi katwa nwo in yitta nin kibinayin sali nalapi nbun Kutelle nin nanit nanyan vat nimon.
Saboda haka, ina ƙoƙari kullum in kasance da lamiri mai tsabta a gaban Allah da mutane.
17 Nene kimalin katu nakus gbardan inna dak nin bunnu udya a ufillu nikubu bara anit ning.
“Bayan’yan shekaru da dama da ba na nan, sai na dawo Urushalima don in kawo wa mutanena kyautai saboda matalauta in kuma yi sadaka.
18 Na nwa din sunani, among a Yahudawa in Asiya wasei nanya lidun kusu litining nanya kutii inlire, na nwa di nin ligozin sa ufiu nayi ba.
Ni tsarkake ne sa’ad da suka same ni cikin filin haikalin ina yin haka. Babu taro tare da ni, ba kuwa ina tā da hankali ba.
19 Ale anite na idin bunfe, na ibellin imon irika na idumun kibinayi ninmi, adi idimun nimonimon.
Amma akwai waɗansu Yahudawa daga lardin Asiya, waɗanda ya kamata suna a nan a gabanka su kawo ƙara in suna da wani a kaina.
20 Sa na anit alele bellin utanu ule na inasei mun kubi ko nq nwq yissin kudaru na Yahudawe;
Ko kuwa waɗannan da suke a nan su faɗi laifin da suka same ni da shi sa’ad da na tsaya a gaban Majalisa,
21 andi na macas ile imon irume na nwa ghatin liwui nbelle kube na nwa yissin nbun mine, 'Ubelen fitu nanan kularita udi mawucuwucu kitimone.'”
sai ko wannan abu ɗaya kaɗai da na ɗaga murya na faɗi yayinda nake tsaye a gabansu cewa, ‘A game da tashin matattu ake mini shari’a a gabanku yau.’”
22 Iwa bellu Felix ku gegeme kitene libauwe, bara nani ata a Yahudawe so ncaa. Aworo, “Vat kubi ko na Lasiya udya nasoje da unuzun Urushalima imanin wusu uliru mine.”
Sai Felis, wanda yake da cikakken sani game da Hanyar, ya ɗaga sauraron ƙarar. Ya ce, “In Lisiyas shugaban ƙungiyar soja ya iso, zan yanke muku shari’a.”
23 Anin woro kusoje asu ucaa in Bulus, tutung na awayita gangang ba, yenje awa nazu adondon me nin bunghe sa uda lissughe.
Ya yi wa jarumin umarni yă tsare Bulus amma yă ba shi’yanci yă kuma bar abokansa su lura da bukatunsa.
24 Na ayiri baat in kata, Felix kpila nin Durisilla uwani me, kunan Jewess, anin to iyiccila Bulus ku, anin lanza kitime ubelle yinnu sa uyenu kitene Kristi Yesu.
Bayan’yan kwanaki da dama sai Felis ya zo da matarsa Durusilla, mutuniyar Yahuda. Sai ya aika a zo da Bulus ya kuma saurare shi da yake magana game da bangaskiya cikin Kiristi Yesu.
25 Ama na Bulus lira ninghe kitene lissosin lilau, ukifu litin, nin dakin shara, fiu kpa Felix ku; anin kawa, “Can nene, asa nse kubi tutung inma yicculu fi.”
Da Bulus ya ci gaba jawabi a kan adalci, kamunkai da kuma hukunci mai zuwa, sai Felis ya tsorata ya ce, “Yanzu kam, ya isa haka! Kana iya tafi. In na sami zarafi, zan kira ka.”
26 Kubi kurum kone, awadin su Bulus ma ninghe ikurfu, unare asa to idak ninghe anin lira ninghe.
A wani fanni yana sa rai cewa Bulus zai ba shi toshiyar baki, saboda haka ya yi ta aika a kira masa Bulus yă yi magana da shi.
27 Ama na akusu aban kata, posiyus Fistus so ugumna kimal in Felix, Felix wadi ninsu ase useru kitin na Yahudawa, asuna Bulus ku alii ubun nanya tursu.
Da shekaru biyu suka wuce, sai Forsiyus Festus, ya gāji Felis, amma domin Felis ya so yă biya wa Yahudawa bukata, sai ya bar Bulus a kurkuku.

< Katwa Nono Katwa 24 >