< 2 Ukorintiyawa 6 >

1 nani katwa logow, idin foo minu nnacara na wa seruu ubolu Kutelle hen nani ba
A matsayinmu na abokan aikin Allah, muna roƙonku kada ku karɓi alherin Allah a banza.
2 Bara na abenle “Nanya kubi ku mang inwa lanza minu, ninwe liri intucu nwa bun minu “Yeneng nenere kubi kumanghe yeneng nenere lirin tucua.
Gama ya ce, “A lokacin samun alherina, na ji ka, a ranar samun ceto kuma, na taimake ka.” Ina gaya muku, yanzu ne lokacin samun alherin Allah, yanzu ne ranar samun ceto.
3 Na arik na ceu litalan tirzu nbun mun b, bara na tidinin su katwa bite se ulazi ba.
Ba ma sa abin tuntuɓe wa kowa, domin kada hidimarmu ta zama abin zargi.
4 Nin yenu nani, ti duro atibite nin nitwa bite vat au arike acin Kutelleari nanya nteru nibinai umin ijasi.
A maimakon haka, duk abin da muke yi, muna yin shi ne don mu nuna cewa mu masu hidimar Allah ne. Muna yin haka cikin jimrewa, da shan wahala, da shan wuya, har da shan masifu.
5 utecu, nannya kuti licin ufizu nayi nin katwa kagbagba, nin salin moroninkitik nin kukpon.
Da shan dūka, da shan dauri, da yawan hargitsi, da yawan fama, da rashin barci, da kuma yunwa.
6 Nin lau uyiru, kbinai ki shau nin washalang nin fip me al, nin su nanya kibinai.
Da cikin tsarki, da fahimta, da haƙuri, da kirki, da cikin Ruhu Mai Tsarki, da cikin ƙauna mai gaskiya,
7 Nin ligbulang kidegen, nin likara Kutelle nin ticilak nibinai nilau ncra ulime nin cara ugule.
da cikin magana mai gaskiya, da kuma cikin ikon Allah. Muna riƙe da makaman adalci dama da hagu,
8 Ti di katwa nin ngongon nin salin ngongo, nin tizugo nin lir. I wa yicu nari anan kinu arik nin kidegene bite.
ta wurin ɗaukaka da ƙasƙanci, da cikin ɓata suna, da kuma cikin yabo. Cikin faɗin gaskiya, an ɗauke mu masu ƙarya,
9 Tidin su katwa we nafon na iwa yiru nari ba a iyiro nari lau nafo tidin kul na tiyita nin lai nafo anan burn, bara nitwa bite na nafo anan caa ukul ba.
mu sanannu ne, duk da haka an ɗauke mu kamar ba a san mu ba, muna mutuwa, duk da haka a raye muke, an ba mu horo, duk da haka ba a kashe mu ba,
10 Tidi katwa nafo nin nibinai nisirne bara nani tidi nin nibinai nibo, nafo nan diru nimum tina yita mum. tina
cikin baƙin ciki, duk da haka kullum cikin murna muke. Cikin matalauta, duk da haka muna azurtar da mutane da yawa. Ba mu da kome, alhali kuwa kome namu ne.
11 Tina me belin minu kidegene bite va, anan Korintiy, nibinai bite pun pas.
Ya ku Korintiyawa, mun yi muku magana a sake, muka kuma saki zuciya da ku ƙwarai.
12 Nati wantin minu nibinai mine b, bara nani anughere wanting ukpilizu ni binai mine
Ba mu ƙi nuna muku ƙaunarmu ba, sai dai ku kuka ƙi nuna mana.
13 Nene nanya kpilizu ubarabara indi liru nan ghenu nafo nono punun nibinai mine pash
A wannan zance kam, ina magana da ku kamar’ya’yana, ku ma ku saki zuciya da mu.
14 Na iwa teru nibinai mine nin nanan salinyinu b, bara nanin iyanghari munu kibinai ki lau nin sali udoka? Sa iyanghari munu njana nin sirti?
Kada ku haɗa kai da marasa bi. Gama me ya haɗa adalci da mugunta? Ko kuwa me ya haɗa haske da duhu?
15 Iyapin iyinari di Kristi ku nin nin Beliyar [kudodoa]? Sa uyapi uladari di unanyinu sauyenu ninnan salin yinuri.
Wace daidaituwa ce tsakanin Kiristi da Iblis? Me ya haɗa mai bi da marar bi?
16 Nin yapin uyenuari di kuti Kutelle nin Chill? Bara na arik ati alau Kutelle unan laiyar, nafo na ana belin “in ma so nanya mine in kuru cinu nanya mine inin yita Kutelle mine, anin wang yita aniti nin.
Wane alkawari ne tsakanin haikalin Allah da na gumaka? Gama mu haikalin Allah mai rai ne. Kamar yadda Allah ya ce, “Zan zauna tare da su, in yi tafiya a cikinsu, zan zama Allahnsu, su kuma za su zama mutanena.”
17 nani Ucif nabelin”nuzun nanya mine iso kusari kurum.” Na iwa dudo imon inazan ile isali lau b, menbah ba timinu mahabi.''
Saboda haka, “Sai ku fito daga cikinsu, ku keɓe kanku, in ji Ubangiji. Kada ku taɓa wani abu marar tsabta, zan kuma karɓe ku.”
18 Menghe ma so Ucif kiti fer. Anunghe nin soo ason nin ni na shono nin “Ubenlun Ucif udia.
Kuma, “Zan zama Uba a gare ku, ku kuma za ku zama’ya’yana, maza da mata, in ji Ubangiji Maɗaukaki.”

< 2 Ukorintiyawa 6 >