< 1 Bitrus 1 >

1 Bitrus unan kaduran Yesu Kristi ucindu kiti na nan feriu alenge na iwa malu kiti du Ubuntus, Ugalatiwa, Kappadokiya, Asiya nin Butiniya,
Bitrus, manzon Yesu Kiristi, Zuwa ga zaɓaɓɓu na Allah, baƙi a duniya, da suke a warwatse ko’ina a Fontus, Galatiya, Kaffadokiya, Asiya da kuma Bitiniya,
2 Nan nyan in yisu Kutelle ucif, nan nyan nkusu ulau nruhu, nin dortun nlirun Yesu Kristi, nin zaminu nmyi me. Na ubolu Kuttelle so nan ghinu, a na lissosin limang mine kpin.
waɗanda aka zaɓa bisa ga rigyasanin Allah Uba, ta wurin aikin tsarkakewar Ruhu, don biyayya ga Yesu Kiristi, su kuma sami yayyafan jininsa. Alheri da salama su zama naku a yalwace.
3 Na Kutelle nin cif ncikilari bite Yesu Kristi se mmari. Bari ngbardang nkunekune me ufitun in Yesu Kristi nan nya na nan kul na ti tina nase umaru upese nin nayi akone,
Yabo ya tabbata ga Allah Uban Ubangijinmu Yesu Kiristi! Cikin jinƙansa mai girma ya ba mu sabuwar haihuwa cikin bege mai rai ta wurin tashin Yesu Kiristi daga matattu,
4 nan nyan ngadu ule na uma nanu ba, na una biju ba ana una wulu ba ina ceo unin kitene kani bar anung.
da kuma cikin gādon da ba zai taɓa lalacewa, ɓacewa ko koɗewa ba, ajiyayye a sama dominku,
5 Nan nya likara Kutelle idi nin icessu nan nyan in yinnu sa uyenu bara utucu ule na ima dursu kubi nimalin.
ku waɗanda ta wurin bangaskiya ake kiyayewa ta wurin ikon Allah har yă zuwa ceton da yake a shirye da za a bayyana a ƙarshen lokaci.
6 sun liburi libo nan nya nilele, nene imon gbardang nta minu liburi lisirne bara udumunuzu nan nayiri gbardang
A kan wannan kuke cike da farin ciki ƙwarai, ko da yake yanzu na ɗan lokaci kuna fuskantar baƙin ciki daga gwaje-gwaje iri-iri.
7 Una so nani bara inan dumuna uyinnu mine sa cuyenu, uyinnu sa uyenu ule na ukatin finariya nin gegame tongo na ina ti nla inan yene ngegeme fining as a finana. Una so nani bara uyinnu sa ciyemu bite nan se uzazunu nin gongong a ughantinu kubi nsa in Yesu Kristi.
Wannan kuwa domin a tabbatar da sahihancin bangaskiyarku ne, wadda ta fi zinariya daraja nesa, ita zinariya kuwa, ko da yake mai ƙarewa ce, akan gwada ta da wuta, domin bangaskiyan nan taku ta jawo muku yabo da girma da ɗaukaka a bayyanar Yesu Kiristi.
8 Na ina yene ghe ba, ana idi nin su me, Na iyene ghe nene ba, ama ina yinin minghe idi nin nayi abo, nin nayi abo ale na akatin ubellu ana alenge na a kulun nin gongong.
Ko da yake ba ku taɓa ganinsa ba, kuna ƙaunarsa; kuma ko da yake ba kwa ganinsa yanzu, kun gaskata shi, kun kuma cika da farin ciki ƙwarai, wanda ya fi gaban faɗi,
9 Idin seru ntueu tilai mine bara uyinnu sa uyenu mine.
gama kuna samun sakamakon bangaskiyarku, ceton rayukanku ke nan.
10 A Annabawa na dortu ipizira nin nonku nibinai ublen ntueu ulele nin bolu Kutelle ulenge na udi un bite.
Game da ceton nan, annabawa, waɗanda suka yi maganar alherin da za tă zo gare ku, sun yi bincike mai zurfi, a natse,
11 Iwa pizuru iyinin uyapin utucuari din cinu ikuru ipizira nin kome kubeari uruhu Nkristi ulenge nan nya mine wadin liru naan ghiru kitene. Uwa so nani a belle nani a kubi dutu ubelen nniu Nkristi nin gongong me na mina dofughe.
suna ƙoƙari su san lokaci da kuma yanayin da Ruhun Kiristi da yake cikinsu yana nunawa sa’ad da ya yi faɗi a kan wahalolin Kiristi da kuma ɗaukaka da za tă bi.
12 Iwa duro a Annabawe utucue, na bara atimine ba, ama nara ubellun nluru ntucue nan nyan Ruhu ulenge na ina tumun unuzu kitene Kutelle imon ilenge na imung anan kadura Kutelle wa piziru i durso.
Aka bayyana musu cewa ba kansu ne suke bauta wa ba sai ku, sa’ad da suka yi maganar abubuwan da aka faɗa muku ta wurin waɗanda suka yi muku wa’azin bishara, ta wurin Ruhu Mai Tsarki wanda aka aika daga sama. Ko mala’iku ma suna marmari su ga waɗannan abubuwa.
13 Bara nani son dan inonko nibinai mine, iceo ayi mine kitene nbolu Kutelle na ima diminu mun kubi nsa in Yesu Kristi.
Saboda haka, ku shirya kanku don aiki; ku zama masu kamunkai; ku kafa begenku duka a kan alherin da za a ba ku sa’ad da aka bayyana Yesu Kiristi.
14 Nato nono ndortu nliru na iwa ni ati mine ntok nile imon na amung yiru ining ba.
Kamar’ya’ya masu biyayya, kada ku bi mugayen sha’awace-sha’awacen da dā kuke da su sa’ad da kuke rayuwa a cikin jahilci.
15 Nato ulenge na nan yicila minu adi lau, amung wang, yitan lau nan nya na dadu mine.
Amma kamar yadda wanda ya kira ku yake mai tsarki, haka ku ma sai ku kasance masu tsarki cikin dukan abubuwan da kuke yi;
16 Nato na ina nyerting, “yitan lau, bara na meng wang di lau”.
gama a rubuce yake cewa, “Ku zama masu tsarki, domin ni mai tsarki ne.”
17 Andi idin yicui ucif, ulenge na adin sa ushara sa usu liti adin su unin unuzun katwa in ko uyeme unit, sun lissosin nca mine nan nya ntoltuno nati.
Tun da yake kuna kira ga Uba wanda yake yin wa kowane mutum shari’a bisa ga ayyukansa ba bambanci, sai ku yi rayuwarku a nan kamar baƙi cikin tsoro mai bangirma.
18 Anung yiru na iwa seru minu nin nizinariya sa azurta imon nanuzu ba, sa lissosin tilalang na ina se kiti na cif mine,
Gama kun san cewa ba da abubuwa masu lalacewa kamar azurfa ko zinariya ce aka fanshe ku daga rayuwar banza da kuka karɓa daga kakanni-kakanninku ba,
19 ana nin nmii mi lau nmiu Gono Kutelle min salin dinong.
sai dai an fanshe ku da jini mai daraja na Kiristi, ɗan rago marar aibi ko lahani.
20 Iwa fere Kristi ku kafin ituno uyii ulele, ana nan nya nayiri nimalin ina durso minu ame.
An zaɓe shi kafin halittar duniya, amma an bayyana shi a zamanin ƙarshe saboda ku.
21 unuzu mere ina yinin nin Kutelle, ulenge na Kutelle wa fyaghe nan nya na nan kul, ulenge na ana nighe ngogong bara uyinnu sa uyenu mine nan se ayi akone kiti Kutelle.
Ta gare shi ne kuka gaskata da Allah, wanda ya tā da shi daga matattu, aka kuma ɗaukaka shi, ta haka bari bangaskiyarku da begenku su kasance ga Allah.
22 Ina ti ati mine lau nan nya dortu kidegen, bara usu kidegen linuana, yitan nin su linuana kang nan nya nibinau mine.
Yanzu da kuka tsarkake kanku ta wurin yin biyayya ga gaskiyan nan, don ku kasance da ƙauna mai gaskiya wa’yan’uwanku, sai ku ƙaunaci juna ƙwarai, daga zuciya.
23 Ina kuru imara minu tutung na nin nimus in bijizu ba ana nin in salin bijizu, unuzun na nan lai nin gisin nliru Kutelle. (aiōn g165)
Gama an sāke haihuwarku, ba da iri da yake lalacewa ba, sai dai marar lalacewa, ta wurin rayayyiya da kuma madawwamiyar maganar Allah. (aiōn g165)
24 Bara nidowo vat masin nafo ukpiari a vat ngogong me nafo kuburin nkpi.
Gama, “Dukan mutane kamar ciyawa suke, darajarsu kuma kamar furannin jeji ne; ciyawa takan yanƙwane furannin kuma su kakkaɓe,
25 Ana uliru Kutelle maso sa ligang. Kadura nliru nlai na iwa bellinari ulele udak kitimine (aiōn g165)
amma maganar Ubangiji tana nan har abada.” Wannan kuwa ita ce kalmar da aka yi muku wa’azi. (aiōn g165)

< 1 Bitrus 1 >