< 1 Bitrus 5 >

1 Ndin wunu na kune ale na idi nan nya mine atuf, meng wang ukuneari nafo anunghe a ushaida nniu in Kristi, a tutung, yita nan nya ngongong mongo na mima dak.
Ina yiwa dattawan da ke cikinku gargadi, ni da nike dan'uwanku dattijo, mashaidin shan wuyar Almasihu, ni kuma mai samun rabo ne daga cikin daukakar daza a bayyana.
2 Bara nani, ndin wunnun minu atuf a kune, sun libya nnono Kutelle na idi nan nya mine. Yenjen nani gegeme, na bara uso minu gbas, ama bara ita nibinai ku, nafo usu Kutelle. Yenje nani gegeme, na bara ikurfung nsalin kidegen ba, ama nin yinnu.
Saboda haka na gargade ku dattawa, kuyi kiwon garken Allah dake tare da ku. Ku kula da su, ba a kan dole ba, amma domin kuna son yin haka, bisa ga yin Allah. Ku kula da su, ba don cin ribar banza ba amma sabo da yardar rai.
3 Na uwa so nafo cikilari kitene na lenge na udi libya mine ba, ama so imon in yenju kiti mine.
Kada ku zama kamar masu iko akan mutanen dake hannunku, amma ku zama abin koyi ga garken.
4 Asa Idurso ugo na nan libya we, ima seru litap ligogong nin salin nshaltu.
Sa'adda za a bayyana Sarkin Makiyaya zaku karbi rawanin da darajarsa bata dushewa.
5 Nan nya libo lirume, anung uzaman, nonkon atimine kiti na kukune. Vat mine teren atimine nin nibinai nisheu isu ati mine nitwa, bara Kutelle nari unan tikunan liti ama unan nonku liti din se ubunu Kutelle.
Hakannan, ku kuma samari kuyi biyayya ga dattawa. Dukanku kuyi damara da tawali'u, kuna bauta wa juna, domin Allah ya na tsayayya da mai girman kai, amma yana yiwa masu tawali'u alheri.
6 Bara nani nonkon atimine kadas ncara likara Kutelle mboti anan ghatinminu kubin cin dak.
Saboda haka ku kaskantar da kanku karkashin hannuwan Allah mai iko duka domin ya daukaka ku a madaidecin lokaci.
7 Toltunong imon nsu mine vat nabunume, bara a ceo kibinai nati mine.
Ku jibga masa duk taraddadin zuciyarku, domin yana kula da ku.
8 Yitan nin nonku nati, yitan nin yenju. Unan nivira mine kugbergenue -masin nafo zaka unan kuculu adin galu akilo buu, npiru nlenge na ama li.
Ku natsu, ku zauna a fadake. Magabcinku, ibilis, kamar zaki mai ruri yana zazzagawa, yana neman wanda zai cinye.
9 Yisinan ghe nin nakara. Yitan nin nakara nan nya in yinnu sa uyenu mine. Yinnon nworu nuana mine nan nyan yie din tecu ayi nin nimusun nniu uremere.
Ku yi tsayayyiyar gaba da shi. Ku yi karfi cikin bangaskiyarku. Ku sani fa abokan tarayyarku da suke cikin duniya suna jimrewa da shan wuyan nan irin taku.
10 Kimal na ima niu nin kubi bat, Kutelle nvat nbolu nanit, alenge na na yicila minu nan nya ngongong me m sali ligang nan nyan Kristi, ma kulu minu, ma ciu minu, amnin ni munu akara. (aiōnios g166)
Bayan shan wuyarku na dan lokaci kadan, Allah mai alheri mara iyaka, wanda ya kiraye ku zuwa ga madawwamiyar daukakarsa cikin Almasihu, zai kammalaku, ya kafa ku, ya kuma karfafa ku. (aiōnios g166)
11 Kiti mere tigo maso sa ligang. Uso nani. (aiōn g165)
Mulki ya tabbata a gare shi har abada abadin. Amin. (aiōn g165)
12 Meng yira Silvanisu ku nafo gwana nciu kibinai, nmini na nyertin minu bat unuzu kit me, Nwunun minu atuf nminin nduro minu nworu imon ilenge na nna nyerti minu kidegen nbolu kutelleari. Yisinan kitene ni ning.
Na amince da Sila amintaccen dan'uwa ne, kuma na rubuto maku a takaice ta hannunsa. Ina yi maku gargadi ina kuma shaida maku cewa abin da na rubuto alherin Allah ne na hakika. Ku kafu a cikinsa.
13 Kishono kanga na kidi in Babila, ulenge na ina fere ghe ligowe nan ghinu, din lissu minu; a Marku, usaun nin, din lissu minu.
Ita matar da ta ke a Babila zababbiya tare da ku, ta na gaisheku, da Markus, dana, yana gaisheku.
14 Lisson ati mine nin nilip in nyukunu tinnu un su. na lissosin lisheu so nan ghinu vat anung na idi nan nyan Kristi.
Ku gai da juna da sumbar kauna. Salama ta tabbata a gare ku dukanku da ke cikin Almasihu.

< 1 Bitrus 5 >