< 1 Ukorintiyawa 10 >

1 In dinin su iyinin, nuana nilime nin nishono, achifbite vat wa chinu kadas kuwut idi kata nan nya kurawa,
Ba na so ku kasance da rashin sani,’yan’uwa, cewa dukan kakannin-kakanninmu sun yi tafiya a ƙarƙashin girgije, dukansu kuma suka bi ta tsakiyar teku.
2 vat mine iwa shitin Nani nmeng nan nya musa nin kuwut a kurawa,
An yi wa dukansu baftisma ga bin Musa a cikin girgije da kuma cikin teku.
3 vat mine tutung wali imonli ilau irumwe,
Dukansu sun ci abincin ruhaniya guda
4 vat sono nmeng nsonu mi lau mirumme. Bara na iwa sono kiti kuparan Kongo Na kuwa dortu nani, kuparan kone wa di Kristi ari.
suka kuma sha ruwan ruhaniyan nan guda; gama sun sha daga dutsen ruhaniya nan, wanda ya yi tafiya tare da su, wannan dutsen kuwa Kiristi ne.
5 Among mine gwardan na Kutellẹ wa lanza nman mine kan ba, unare wati abimine yita bú nan nya kushoẹ.
Duk da haka, Allah bai ji daɗin yawancinsu ba; gawawwakinsu kuwa suka bazu ko’ina a cikin hamada.
6 Nene ilẹ imone inin so nari imon yenju, bara arik wa dortu imon inanza nafo na inughe wa su.
To, waɗannan abubuwa misalai ne a gare mu, kada mu yi marmarin mugayen abubuwa, kamar yadda suka yi.
7 Nati waso anan chip ba, nafo na amon mine wadi-nafo Na iyerti di “Anit wa so ileu isono, imon fits nin nibinayin nozu nan nawani, izu avu.”
Kada ku zama masu bautar gumaka, yadda waɗansunsu suka zama; kamar yadda yake a rubuce cewa, “Mutanen suka zauna don su ci su kuma sha, suka kuma tashi suka shiga rawa ta rashin kunya.”
8 Na tiwa nozo nin nawani buu ba, nafo na amon mine gwardan wa sunani, anit amoi akut aba nin Na tat nin ku liri lirume.
Kada fa mu yi fasikanci yadda waɗansunsu suka yi, har a rana guda mutane dubu ashirin da uku a cikinsu suka mutu.
9 Nati wa mala Kristi ku ba, nafo na gwardan namon mine wasu iyii ini wa kifizin nani ikuzu.
Kada mu gwada Kiristi yadda waɗansunsu suka yi, har macizai suka kakkashe su.
10 Tutun na tiwasu ugwonduluba, nafo na amon mine gwardan wa su, unan kadura Kutellẹ ulẹ wa molu nani.
Kada kuma ku yi gunaguni yadda waɗansunsu suka yi, har mala’ika mai hallakarwa ya hallaka su.
11 Nene Ile imone wase nani inan so arikeku imon yenju, inani wa yertu inin inan sonari imon wunnu natuff bara kitene bitere kubin nmalu iyii (aiōn g165)
Waɗannnan abubuwa sun same su ne, domin su zama abubuwan koyi, aka kuma rubuta su domin a gargaɗe mu, mu da ƙarshen zamani ya zo mana. (aiōn g165)
12 Bara nani ame ule na adin yenju ayisin Na asu sen bara awa diu.
Saboda haka in kana tsammani kana tsaye ne, to, ka yi hankali kada ka fāɗi!
13 Na imonmon duku ilenge na idi inmaluzu madamu irika na anit yiruba; Kutelle unan kidegenari udu ligan: na ama sun minu ise umalun indiu ule na ukati likara mineba, vat nani nin nimon malun indiuwe ama punu nari Libau nnuzu bara tinan se uteru nibinayi mun.
Ba jarrabar da ta taɓa samunku, wadda ba a saba yi wa mutum ba. Allah mai aminci ne; ba zai bari a jarrabce ku fiye da ƙarfinku ba. Amma in aka jarrabce ku, zai nuna muku mafita, domin ku iya cin nasara.
14 Bara nani nuana insu kibinayi nin, con pit kitin chil.
Saboda haka abokaina ƙaunatattu, ku guje wa bautar gumaka.
15 Ndin liru nan ghinu nafo anan kpilizu bara inan wutu kimal nimon ile na in belle.
Ina magana da ku a kan ku mutane ne fa masu azanci; ku duba da kanku ku ga abin da nake faɗa.
16 Kakuk nmari na asa tita nmari ku, ikosuzoari nan nya nmii in Kristi ba? Likalan nfungul na tidin pucu, ukosuzoari nan nya kidowon Kristiba?
Kwaf nan na godiya da muke yin godiya da shi, ashe ba tarayya ce a cikin jinin Kiristi ba? Wannan burodi kuma da muke karya mu ci, ashe, ba tarayya ne a cikin jikin Kiristi ba?
17 Bara na likalan nfungul lirumari, arik alenge nati karin kidowo kirumari, vat bite din li likalan nfungul lirume ligowe.
Da yake burodin nan ɗaya ne, ashe kuwa, mu da muke da yawa jiki ɗaya ne, gama dukanmu muna ci daga burodi nan guda.
18 Yenen anutin Israila nburnu: na asa ileo ujuju ulauwe, na uso limununari nin nimon ile na isu napik alaunwe ba?
Ku dubi mutanen Isra’ila mana. Ashe, waɗanda suke cin hadayu, ba ɗaya suke da juna cikin cin hadayun da aka miƙa a bagade ba?
19 Iyaghari ndin bellu nene? Au inchil imoimonaria? Sa imon ile na ikanja kiti inchil imoimonari?
To, me kuke tsammani nake nufi a nan? Hadayar da aka miƙa wa gunki ce wani abu, ko kuma gunkin ne wani abu?
20 Nbelle nenge, imon ile na alumai din duzu idi nakwiza natala na Kutellẹri idin nizughe ba, agwargenuari. Na ndinin su imunu ati nin nagwergonu ba!
A’a, ina nufin akan miƙa hadayun da masu bautar gumaka suka wa aljanu ne, ba Allah ba. Ba na so ku zama ɗaya da aljanu.
21 Na iwasa isono kakkuk Ncikilari ini kuru ida sono kakkuk nagwergenu ba. Na uwasa uyita nin Cikilari bite kutebul me ukuru uyita kiti kutebul nagwergenu ba.
Ba zai yiwu ku sha daga kwaf na Ubangiji ku kuma sha daga kwaf na aljanu ba, ba ya yiwuwa ku ci a teburin Ubangiji, ku kuma ci a teburin aljanu.
22 Sa timananzu Cikilare ayi asu liyarina? Akara bite katin ame?
Ashe, so muke mu tsokani Ubangiji ya yi kishi? Mun fi shi ƙarfi ne?
23 “Imon vat inseruari” na vat nimonari di in libunba.
“Ana da dama a yi kome” sai dai ba kome ba ne yake da amfani. “Ana da dama a yi kome” sai dai ba kome ba ne mai ginawa.
24 Na umon wa pizurru nman litime ba. Nani, na kogha pizuru nmang ndon lisosin me.
Kada wani yă kula da kansa kawai, sai dai yă kula da waɗansu kuma.
25 Uwasa uleu imon ilenge na idin lessu nkasau sa utirunu.
Ku ci kowane abin da ake sayarwa a kasuwar nama ba sai kun tambaya ba don kada lamiri yă damu da inda abin ya fito,
26 “Uyẹ nin nimon ilenge na idin nan nyẹ in Kutellẹari.''
gama “Duniya da duk abin da yake cikinta na Ubangiji ne.”
27 Asa unan salin yinnun nin Kutellẹ nyichilafi ndi li nimonli, fe ta kibinayi umadu, leu imon ilenge na iceu nbunfe sa utirunu.
In wani marar bi ya gayyace ku cin abinci kuka kuwa yarda ku je, sai ku ci ko mene ne da aka sa a gabanku, ba tare da tambaya don kada lamiri yă damu da inda abin ya fito.
28 Vat nani, adi umon worofi, “imoli ilele inuzumun kiti ncillari nari uli ninin. Nane bara ulenge na abellin fiari, a bara ukpilluzu kibinayi tutun.
Sai dai in wani ya ce muku, “Ai, wannan an miƙa ne wa gunki,” to, kada ku ci, saboda duban mutuncin wannan da ya gaya muku, don kuma lamiri yă kasance babu laifi
29 Ndin bellu ni kpiluzu kibinayi inlelere, a na kinfe ba. Bara iyari bati nfang kibinayi nighe umoghari kpilizai muna?
ina nufin lamirin wancan mutum ne fa, ba naku ba. Don me lamirin wani zai shari’anta’yancina?
30 Nwali imonli ilele nin liburi libo bara iyaghari iliri nanzan kitene nimon ilenge na nta nlira ku?
In na ci abinci da godiya, don me za a zarge ni a kan abin da na ci da godiya ga Allah?
31 Bara nani, sa idin li sa idin so, sa vat nimon ile na idin su, sun vat bara uzazunu Kutellẹ.
Saboda haka, duk abin da kuke yi, ko ci ko sha, ku yi shi duka saboda ɗaukakar Allah.
32 Na iwati umon se imon ntiruba, sa nan nya na Yahudawa sa a Hellenawa, sa nan nya kilari Kutellẹ.
Kada ku sa wani yă yi tuntuɓe, ko mutumin Yahuda ne, ko mutumin Al’ummai ko kuma ikkilisiyar Allah
33 Tan kayiri isu nafo na nna su kayir npo vat nanit ayi nan nya vat nimon, na nin pizuru nimoimon in litinin ba, bara anit gwardan nan se utuchu.
kamar dai yadda nake ƙoƙarin faranta wa kowa rai, ta kowace hanya. Gama ba don kaina kaɗai nake yi ba, sai dai don amfanin mutane da yawa, don su sami ceto.

< 1 Ukorintiyawa 10 >