< Lamentaciones 5 >

1 Acuérdate, o! Jehová, de lo que nos ha venido: vé, y mira nuestra vergüenza.
Ka tuna, ya Ubangiji, abin da ya faru da mu; duba, ka ga kunyar da muka sha.
2 Nuestra heredad se ha vuelto a extraños, nuestras casas a forasteros.
An ba wa baƙi gādonmu, gidajenmu kuma aka ba bare.
3 Huérfanos somos sin padre: nuestras madres como viudas.
Mun zama marayu marasa ubanni, uwayenmu kamar gwauraye.
4 Nuestra agua bebemos por dinero, nuestra leña compramos por precio.
Dole mu sayi ruwan da muke sha; sai mun biya mu sami itace.
5 Sobre nuestra cerviz padecemos persecución; cansámosnos, y no hay para nosotros descanso.
Masu fafararmu sun kusa kama mu; mun gaji kuma ba dama mu huta.
6 A Egipto dimos la mano, y al Asirio, para hartarnos de pan.
Mun miƙa kanmu ga Masar da Assuriya don mu sami isashen abinci.
7 Nuestros padres pecaron, y son muertos; y nosotros llevamos sus castigos.
Kakanninmu sun yi zunubi kuma ba sa nan yanzu, mu ne aka bari muna shan hukuncinsu.
8 Siervos se enseñorearon de nosotros: no hubo quien nos librase de su mano.
Bayi suna mulki a kanmu, kuma ba wanda zai’yantar da mu daga hannuwansu.
9 Con el peligro de nuestras vidas traíamos nuestro pan delante de la espada del desierto.
Muna samun burodi a bakin rayukanmu domin takobin da yake a jeji.
10 Nuestros cueros se ennegrecieron como un horno a causa del ardor de la hambre.
Fatar jikinmu ta yi zafi kamar murhu, muna jin zazzaɓi domin yunwa.
11 Afligieron a las mujeres en Sión, a las vírgenes en las ciudades de Judá.
An yi wa mata fyaɗe a cikin Sihiyona, da kuma budurwai a cikin garuruwan Yahuda.
12 A los príncipes colgaron con su mano: no reverenciaron los rostros de los viejos.
An rataye’ya’yan sarakuna da hannuwansu; ba a ba wa dattawa girma.
13 Llevaron los mozos a moler, y los muchachos desfallecieron en la leña.
Samari suna faman yin niƙa; yara kuma suna fama da ƙyar da nauyin kayan itace.
14 Los ancianos cesaron de la puerta, los mancebos de sus canciones.
Dattawan sun bar ƙofar birnin, samari sun daina rera waƙa.
15 Cesó el gozo de nuestro corazón, nuestro corro se tornó en luto.
Farin ciki ya rabu da zuciyarmu; rayuwarmu ta zama makoki.
16 Cayó la corona de nuestra cabeza: ¡ay ahora de nosotros! porque pecamos.
Rawani ya fāɗi daga kanmu. Kaiton mu gama mun yi zunubi!
17 Por esto fue entristecido nuestro corazón, por esto se entenebrecieron nuestros ojos.
Domin wannan zuciyarmu ta yi sanyi; domin waɗannan abubuwa idanunmu sun dushe
18 Por el monte de Sión que es asolado, zorras andan en él.
gama Tudun Sihiyona ya zama kufai, sai diloli ke yawo a wurin.
19 Mas tú, Jehová, para siempre permanecerás: tu trono de generación en generación.
Ya Ubangiji, kai ne mai iko har abada; kursiyinka ya dawwama cikin dukan zamani.
20 ¿Por qué te olvidarás para siempre de nosotros? ¿dejarnos has por luengos días?
Don mene ne kake mantawa da mu koyaushe? Me ya sa ka yashe mu da jimawa?
21 Vuélvenos, o! Jehová, a ti, y volvernos hemos: renueva nuestros días como al principio.
Ka sāke jawo mu gare ka, ya Ubangiji, don mu komo; ka sabunta kwanakinmu su zama kamar yadda suke a dā
22 Porque desechando nos has desechado: háste airado contra nosotros en gran manera.
sai dai in ka ƙi mu gaba ɗaya kana fushi da mu fiye da yadda za a iya aunawa.

< Lamentaciones 5 >