< Mateyo 18 >

1 Pacindi copeleco beshikwiya ba Yesu balesa kulyendiye nekumwipusheti, “Inga niyani eshakabe mukulene wapita bonse mu Bwami bwa kwilu?”
A lokacin nan sai almajirai suka zo wurin Yesu suka yi tambaya suka ce, “Wane ne mafi girma a mulkin sama?”
2 Yesu walakuwa mwana ne kumwimanika pakati pabo,
Sai ya kira ƙaramin yaro ya sa shi yă tsaya a tsakiyarsu.
3 ne kwambeti, “Cakubinga ndamwambilishingeti, mwabula kusanduka, ne kubeti mwana uyu, nteti mukengile mu Bwami bwa kwilu pimbi.
Sai ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, in ba kun canja kuka zama kamar ƙananan yara ba, labudda, ba za ku shiga mulkin sama ba.
4 Ecebo cakendi muntu uliyense lalicepeshenga mbuli mwana uyu, epeloyo emukulene wapita, mu Bwami bwa kwilu.
Saboda haka, duk wanda ya ƙasƙantar da kansa kamar wannan yaro, shi ne mafi girma a mulkin sama.
5 Kayi uliyense latambulunga mwana ulyeti uyu pacebo cakame, endiye kayi lantambulunga.”
Duk kuma wanda ya karɓi ƙaramin yaro kamar wannan a cikin sunana ya karɓe ni ne.
6 “Uliyense lapeshengeti umo wabana bakute lushomo muli njame kwambeti bapuntwe, celela kuba cena kumusungilila cilibwe camwampelo munshingo ne kumuwala mulwenje.
“Amma duk wanda ya sa ɗaya daga cikin ƙananan nan da suka gaskata da ni ya yi zunubi, zai fiye masa a rataya babban dutsen niƙa a wuyarsa, a kuma nutsar da shi a zurfin teku.
7 Malele kubantu bapacishi capanshi pano, cebo cakufula kwabwipishi, Naboyo bwipishi nkabwelela kubula kuboneka, nomba malele kumuntu uyo lapeshengeti banendi bapuntwe.
Kaiton duniya saboda abubuwan da suke sa mutane su yi zunubi! Dole irin waɗannan abubuwa su zo, sai dai kaiton mutumin da ya zama sanadin kawo su!
8 “Lino na cikasa cakobe, nambi mwendo wakobe, ukute kukwipisha, kotimbula utaye, caina kuya kwingila ku buyumi koli watimbuka cikasa, nambi mwendo, kupita kuwalwa kumulilo utapu kokute makasa onse, nambi myendo yonse ibili. (aiōnios g166)
In hannunka ko ƙafarka yana sa ka zunubi, yanke shi ka yar. Zai fiye maka ka shiga rai da hannu ko ƙafa ɗaya da hannuwa biyu ko ƙafafu biyu da a jefar da kai cikin madawwamiyar wuta da hannuwa biyu ko ƙafafu biyu. (aiōnios g166)
9 Kayi na linso lyakobe lilakwipishinga, likolobolemo ulitaye, caina kuya kwingila ku buyumi kokute linso limo'wa, kupita kuwalwa mu Gehena kokute menso abili.” (Geenna g1067)
In kuma idonka yana sa ka zunubi, ƙwaƙule shi ka yar. Zai fiye maka ka shiga rai da ido ɗaya, da ka shiga jahannama ta wuta da idanunka biyu. (Geenna g1067)
10 “Cenjelani, kamutanyansha umo wa bana batwanike aba, cakubinga ndamwambilishingeti, bangelo bakwilu nkobali cindi conse pamenso a Bata bakwilu.”
“Ku lura, kada ku rena ɗaya daga cikin waɗannan ƙanana. Gama ina faɗa muku mala’ikunsu a sama kullum suna duban fuskar Ubana da yake cikin sama.
11 Mwana Muntu walesa kupulusha bantu bataika.
12 “Inga mwinseconi, na muntu kakute mbelele mwanda umo, imo itaika, sena nkelela kushiya mbelele shisa makumi asanu, ne ana, ne na shimbi shisanu ne shina mumilundu, ne kuya kulangaula imo isa ilataiki?
“Me kuka gani? In wani yana da tumaki ɗari, sai ɗaya daga cikinsu ta ɓace, ba sai yă bar tasa’in da taran a kan tuddai yă je neman guda ɗayan da ta ɓace ba?
13 Ndamwambilinga cakubinga kwambeti, aicana ukute kusekelela kupita kusekelela ne shisa shilabulu kutaika.
In kuwa ya same ta, ina gaya muku gaskiya, zai yi murna saboda ɗayan fiye da tasa’in da taran da ba su ɓace ba.
14 Nicimo cimo Ba meshenu bakwilu nkabasuni kwambeti umo wabana batwanike aba ataike?”
Haka ma Ubanku da yake cikin sama ba ya so ko ɗaya daga cikin ƙananan nan yă ɓace.
15 “Na mwanse wakobe lakwipishili koya kulyendiye, wenga umuleshe cilubo cakendi, mubandike pambali mobabili, na mulanyumfwana ekwambeti ulamubweshe munshila,
“In ɗan’uwanka ya yi maka laifi, ka je ka nuna masa laifinsa, tsakaninku biyu kaɗai. In ya saurare ka, ka maido da ɗan’uwanka ke nan.
16 Nomba na ubula kukunyumfwila, umantepo umo nambi babili, nambi batatu. kwambeti makani nakashininkishiwe ne bukamboni bwa bantu babili nambi batatu.
Amma in bai saurare ka ba, ka je tare da mutum ɗaya ko biyu, domin ‘a tabbatar da kowace magana a bakin shaidu biyu ko uku.’
17 Na naboyo ubula kubanyumfwila, wambileko bamubungano. Kayi na ubula kunyumfwila bamubungano, komubonangeti muntu wamishobo naimbi, nambi shimisonko.”
In kuwa ya ƙi yă saurare su, sai ka gaya wa ikkilisiya; in kuma ya ƙi yă saurari ikkilisiya ma, ka yi da shi kamar marar sanin Allah ko mai karɓar haraji.
18 “Cakubinga ndamwambilishingeti, ciliconse ncoti mukasunge panshi pano, nicikasungwe kwilu, kayi ciliconse nceti mukasungulule panshi pano, nicikasungululwe kwilu.
“Gaskiya nake gaya muku, duk abin da kuka daure a duniya, za a daure a sama, duk kuma abin da kuka kunce a duniya, za a kunce shi a sama.
19 Kayi cakubinga ndamwambilishingeti, mwanyumfwana mobabili pacishi capanshi, pakusenga cintu ciliconse, Bata bakwilu nibakamwinshile.
“Har wa yau, ina gaya muku cewa in mutum biyu a cikinku a duniya suka yarda su roƙi wani abu, Ubana da yake cikin sama zai yi muku.
20 Pali babili, nambi batatu balabungana mu Lina lyakame, ame mpondi pakati pabo.”
Gama inda mutum biyu ko uku suka taru cikin sunana, a can ma ina tare da su.”
21 Popelapo Petulo walesa kuli Yesu, ne kumwipusheti, “Nkambo, na mukwetu kapitilishowa kunjipishila, ngandimulekelela tunkanda tungaye? Sena nganshikisha tunkanda tusanu ne tubili?”
Sai Bitrus ya zo wurin Yesu ya yi masa tambaya ya ce, “Ubangiji, sau nawa zan yafe wa ɗan’uwana sa’ad da ya yi mini zunubi? Har sau bakwai?”
22 Yesu walamukumbuleti, “Sena ndambangowa tunkanda tusanu ne tubili, sobwe, nsombi tunkanda makumi asanu ne abili kufulisha tunkanda tusanu ne tubili.”
Yesu amsa ya ce, “Ina gaya maka, ba sau bakwai ba, amma sau saba’in da bakwai.
23 Lino Bwami bwa kwilu tubwelanishe cisa. Palikuba mwami uyo walakuwa basebenshi bakendi kwambeti, abone cena nkongole nshobalikukute.
“Saboda haka, mulkin sama yana kama da wani sarki wanda ya so yă yi ƙididdigar dukiyarsa da take a hannun bayinsa.
24 Mpwalatatika kubasesa, kwalacanika musebenshi naumbi walikukute nkongole ya mali angi akwana bina myanda myanda.
Da ya fara ƙididdigar, sai aka kawo masa wani wanda yake bin bashin talenti dubu goma.
25 Mpwalalilwa kubwesha nkongole, Mwami walambeti, musebenshi usa aulishiwe ne mukashendi ne banabendi, ne bintu byonse mbyalikukute, kwambeti nkongole isa ipwe.
Da yake bai iya biya ba, sai maigida ya umarta a sayar da shi da matarsa da yaransa da kuma duk abin da yake da shi, a biya bashin.
26 Musebenshi usa walasuntama nekufulungana panshi pamenso pa mwami ne kukombeleleti, “Kamupembelelako pang'ana ninkabweshe nkongole yonse.”
“Bawan ya durƙusa a gabansa. Ya yi roƙo ya ce, ‘Ka yi mini haƙuri, zan biya ka ƙaf.’
27 Mwami usa walanyumfwila luse, ne kumulekelela nkongole yonse, ne kumusuminisheti, ayenga.
Maigidan bawan ya ji tausayinsa, ya yafe masa bashin, ya kuma sake shi.
28 Nomba uyu musebenshi mpwalapula, walakumanya musebenshi munendi walikumukutile nkongole ya mali akwana mwanda umo. Walamwikata mwabukalu ne kumutinga panshingo, ne kumwambileti, “Bwesha nkongole isa!”
“Amma da wannan bawa ya fita, sai ya gamu da wani abokin bautarsa wanda yake binsa bashin dinari ɗari. Sai ya cafke shi, ya shaƙe shi a wuya yana cewa, ‘Biya ni abin da nake binka!’
29 Musebenshi munendi usa walaliwisha panshi kumyendo yakendi ne kumukombeleleti, Kamupembelelako pang'ana, ninkabweshe nkongole njonkute kuli njamwe.
“Wannan abokin bautarsa ya durƙusa ya roƙe shi, ‘Ka yi mini haƙuri, zan biya ka.’
30 Nendi walakana kumulekelela, walamusungisha mujele, kushikila akabweshe nkongole.
“Amma ya ƙi. A maimako, sai ya je ya sa aka jefa shi a kurkuku, har yă biya bashin.
31 Basebenshi nabambi mpobalabona calenshika, balepilwa kwine. Neco balaya kumwambila mwami bintu byonse.
Sa’ad da sauran bayin suka ga abin da ya faru, abin ya ɓata musu rai ƙwarai, sai suka tafi suka faɗa wa maigidansu dukan abin da ya faru.
32 Mwami usa walamukuwa, ne kumwambileti, “Musebenshi waipa obe! Ame ndalakulekelela nkongole yonse mpowalankombelela.
“Sai maigidan ya kira wannan bawa. Ya ce, ‘Kai mugun bawa, na yafe duk bashin da nake binka domin ka roƙe ni.
33 Sena nkowanga welela kumwinshila nkumbo ne kumulekelela munobe mbuli ame ncondakwinshila nkumbo ne kukulekelela?”
Ashe, bai kamata kai ma ka ji tausayin abokin bautarka yadda na yi maka ba?’
34 Mwami usa walakalala, neco walamuwala mujele kwambeti bakamupenshe, kushikla akabweshe nkongole isa,
Cikin fushi, maigidan ya miƙa shi ga ma’aikatan kurkuku su gwada masa azaba, har yă biya dukan bashin da ake binsa.
35 Yesu walapwisha kwamba pakwambeti “Ici encoti bakense Bata bakwilu kuli umo ne umo, uyo utalekelele munendi ne moyo wonse.”
“Haka Ubana da yake cikin sama zai yi da kowannenku, in ba ku yafe wa’yan’uwanku daga zuciyarku ba.”

< Mateyo 18 >