< Плач Иеремии 5 >

1 Молитва Иеремии пророка. Помяни, Господи, что бысть нам: призри и виждь укоризну нашу:
Ka tuna, ya Ubangiji, abin da ya faru da mu; duba, ka ga kunyar da muka sha.
2 достояние наше обратися к чуждим и домы нашя ко иноплеменником:
An ba wa baƙi gādonmu, gidajenmu kuma aka ba bare.
3 сири быхом, несть отца, матери нашя яко вдовы.
Mun zama marayu marasa ubanni, uwayenmu kamar gwauraye.
4 Воду нашу за сребро пихом, дрова наша за цену куповахом:
Dole mu sayi ruwan da muke sha; sai mun biya mu sami itace.
5 на выя нашя гоними быхом, трудихомся, не почихом.
Masu fafararmu sun kusa kama mu; mun gaji kuma ba dama mu huta.
6 Египет даде руку, Ассур в насыщение их.
Mun miƙa kanmu ga Masar da Assuriya don mu sami isashen abinci.
7 Отцы наши согрешиша, и несть их, мы же беззакония их подяхом.
Kakanninmu sun yi zunubi kuma ba sa nan yanzu, mu ne aka bari muna shan hukuncinsu.
8 Раби обладаша нами, избавляющаго несть от руку их.
Bayi suna mulki a kanmu, kuma ba wanda zai’yantar da mu daga hannuwansu.
9 В душах наших носихом хлеб наш, от лица меча в пустыни.
Muna samun burodi a bakin rayukanmu domin takobin da yake a jeji.
10 Кожа наша аки пещь обгоре, разседошася от лица бурей глада.
Fatar jikinmu ta yi zafi kamar murhu, muna jin zazzaɓi domin yunwa.
11 Жен в Сионе смириша, девиц во градех Иудиных.
An yi wa mata fyaɗe a cikin Sihiyona, da kuma budurwai a cikin garuruwan Yahuda.
12 Князи в руках их повешени быша, старейшины не прославишася.
An rataye’ya’yan sarakuna da hannuwansu; ba a ba wa dattawa girma.
13 Избраннии плачь подяша, и юноши в кладе изнемогоша.
Samari suna faman yin niƙa; yara kuma suna fama da ƙyar da nauyin kayan itace.
14 И старцы от врат оскудеша, избраннии от песней своих умолкоша.
Dattawan sun bar ƙofar birnin, samari sun daina rera waƙa.
15 Разсыпася радость сердец наших, обратися в плачь лик наш,
Farin ciki ya rabu da zuciyarmu; rayuwarmu ta zama makoki.
16 спаде венец со главы нашея: горе нам, яко согрешихом.
Rawani ya fāɗi daga kanmu. Kaiton mu gama mun yi zunubi!
17 О сем смутися сердце наше, о сем померкнуша очи наши.
Domin wannan zuciyarmu ta yi sanyi; domin waɗannan abubuwa idanunmu sun dushe
18 На горе Сионе, яко погибе, лисицы ходиша.
gama Tudun Sihiyona ya zama kufai, sai diloli ke yawo a wurin.
19 Ты же, Господи, во веки вселишися, престол Твой в род и род.
Ya Ubangiji, kai ne mai iko har abada; kursiyinka ya dawwama cikin dukan zamani.
20 Вскую во веки забываеши нас, оставиши ли нас в продолжение дний?
Don mene ne kake mantawa da mu koyaushe? Me ya sa ka yashe mu da jimawa?
21 Обрати ны, Господи, к Тебе, и обратимся, и вознови дни нашя якоже прежде.
Ka sāke jawo mu gare ka, ya Ubangiji, don mu komo; ka sabunta kwanakinmu su zama kamar yadda suke a dā
22 Яко отревая отринул еси нас, разгневался еси на ны зело.
sai dai in ka ƙi mu gaba ɗaya kana fushi da mu fiye da yadda za a iya aunawa.

< Плач Иеремии 5 >