< От Иоанна святое благовествование 6 >

1 По сих иде Иисус на он пол моря Галилеи Тивериадска:
Bayan waddannan abubuwa, Yesu ya ketare tekun Galili, wanda a ke kira tekun Tibariya.
2 и по Нем идяше народ мног, яко видяху знамения Его, яже творяше над недужными.
Sai taro mai yawa suka bi shi domin suna ganin alamu da yake yi akan marasa lafiya.
3 Взыде же на гору Иисус и ту седяше со ученики Своими.
Sai Yesu ya hau dutse ya zauna a can tare da almajiransa.
4 Бе же близ Пасха, праздник Жидовский.
(Kuma da idin Ketarewa, wato idin Yahudawa, ya kusato.)
5 Возвед убо Иисус очи и видев, яко мног народ грядет к Нему, глагола к Филиппу: чим купим хлебы, да ядят сии?
Da Yesu ya daga kai sai ya ga babban taro yana zuwa wurinsa, sai ya ce ma Filibus, “Ina za mu sayi gurasar da Mutanen nan za su ci?”
6 Сие же глаголаше искушая его: Сам бо ведяше, что хощет сотворити.
( Ya fadi haka ne domin ya gwada shi, saboda shi kansa ya san abin da zai yi.)
7 Отвеща Ему Филипп: двема стома пенязей хлебы не довлеют им, да кийждо их мало что приимет.
Filibus ya amsa masa, “gurasar dinari biyu ma ba zata ishi kowannensu ya samu ko kadan ba.”
8 Глагола Ему един от ученик Его, Андрей, брат Симона Петра:
Daya daga cikin almajiransa, wato Andarawus, dan'uwan Siman Bitrus, ya ce masa,
9 есть отрочищь зде един, иже имать пять хлеб ячменных и две рыбе: но сии что суть на толико?
“Ga wani dan yaro nan da dunkule biyar na sha'ir, da kifi biyu. Amma menene wadannan za su yi wa mutane masu yawa?”
10 Рече же Иисус: сотворите человеки возлещи. Бе же трава многа на месте. Возлеже убо мужей числом яко пять тысящ.
Yesu ya ce, “ku sa mutane su zauna.”( wurin kuwa akwai ciyawa.) Sai mazajen suka zauna, sun kai wajen dubu biyar.
11 Прият же хлебы Иисус и, хвалу воздав, подаде учеником, ученицы же возлежащым: такожде и от рыбу, елико хотяху.
Sai Yesu ya dauki gurasar, bayan da ya yi godiya, sai ya rarraba wa wadanda suke zaune. Haka kuma ya rarraba kifin gwargwadon abin da zai ishe su.
12 И яко насытишася, глагола учеником Своим: соберите избытки укрух, да не погибнет ничтоже.
Da Mutanen suka ci suka kuma koshi, sai ya ce wa almajiransa, ku tattara gutsattsarin da suka rage, kada ya zama asara.”
13 Собраша же и исполниша дванадесяте кошя укрух от пятих хлеб ячменных, иже избыша ядшым.
Sai suka cika kwanduna goma sha biyu da gutsattsarin gurasar nan biyar da ya rage bayan da kowa ya ci.
14 Человецы же видевше знамение, еже сотвори Иисус, глаголаху, яко Сей есть воистинну Пророк Грядый в мир.
Da jama'a suka ga alamar da ya yi, sai suka ce, “Hakika wannan shi ne annabin nan mai zuwa cikin duniya.
15 Иисус убо разумев, яко хотят приити, да восхитят Его и сотворят Его царя, отиде паки в гору един.
“Da Yesu ya gane suna shirin zuwa su dauke shi da karfi da yaji su nada shi sarki, sai ya sake komawa kan dutsen da kansa.
16 Яко позде бысть, снидоша ученицы Его на море,
Da yamma ta yi, sai almajiransa suka gangara teku.
17 и влезоша в корабль, и идяху на он пол моря в Капернаум. И тма абие бысть, и не (у) бе пришел к ним Иисус.
Suka shiga cikin jirgi, suka haye teku zuwa kafarnahum. (A lokacin duhu ya yi, Yesu kuwa bai riga ya iso wurinsu ba tukuna.)
18 Море же, ветру велию дыхающу, воздвизашеся.
Iska mai karfin gaske tana kadawa, kuma tekun yana hargowa.
19 Гребше же яко стадий двадесять пять или тридесять, узреша Иисуса ходяща по морю и близ корабля бывша, и убояшася.
Bayan da almajiran suka yi tuki na wajen kimanin mil ashirin da biyar ko talatin, sai suka hango Yesu yana tafiya a kan teku ya kuma kusa da jirgin, sai suka firgita.
20 Он же глагола им: Аз есмь, не бойтеся.
Amma ya ce masu, “Ni ne! kada ku firgita.”
21 Хотяху убо прияти Его в корабль: и абие корабль бысть на земли, в нюже идяху.
Sa'an nan suka yarda suka karbe shi a cikin jirgin, kuma nan da nan jirgin ya kai gacci.
22 Во утрий (же) народ, иже стояше об он пол моря, видев, яко корабля иного не бе ту, токмо един той, в оньже внидоша ученицы Его, и яко не вниде со ученики Своими Иисус в корабль, но едини ученицы Его идоша:
Kashe gari, sauran taron da suke tsaye a dayan hayin tekun suka ga cewa babu wani jirgi a wajen sai dayan, Yesu kuma bai shiga ciki da almajiransa ba, amma almajiransa suka tafi su kadai.
23 и ини приидоша корабли от Тивериады близ места, идеже ядоша хлебы, хвалу воздавше Господеви:
Sai dai, akwai wadansu jirage da suka zo daga Tibariya kusa da wurin da taron suka ci gurasa bayan da Ubangiji ya yi godiya.
24 егда же видеша народи, яко Иисуса не бысть ту, ни ученик Его, влезоша сами в корабли и приидоша в Капернаум, ищуще Иисуса,
Sa'anda taron suka gane cewa Yesu da almajiransa ba su wurin, su da kansu su ka shiga cikin jiragen suka tafi Kafarnahum neman Yesu.
25 и обретше Его об он пол моря, реша Ему: Равви, когда зде бысть?
Da suka same shi a hayin tekun, suka ce masa, “Mallam, yaushe ka zo nan?”
26 Отвеща им Иисус и рече: аминь, аминь глаголю вам, ищете Мене, не яко видесте знамение, но яко яли есте хлебы и насытистеся:
Yesu ya amsa masu, da cewa, “hakika, kuna nema na ne, ba don kun ga alamu ba, amma domin kun ci gurasar nan kun koshi.
27 делайте не брашно гиблющее, но брашно пребывающее в живот вечный, еже Сын Человеческий вам даст: Сего бо Отец знамена Бог. (aiōnios g166)
Ku daina yin wahala a kan neman abinci mai lalacewa, sai dai a kan abinci mai dawwama wanda zai kaiku ga rai madawwami wanda Dan Mutum zai ba ku, domin Ubangiji Allah ya sa hatiminsa a kansa.” (aiōnios g166)
28 Реша же к Нему: что сотворим, да делаем дела Божия?
Sai suka ce Masa, “Me za mu yi, domin mu aikata ayyukan Allah?
29 Отвеща Иисус и рече им: се есть дело Божие, да веруете в Того, Егоже посла Он.
Yesu ya amsa, “Wannan shi ne aikin Allah: wato ku gaskata da wanda ya aiko.”
30 Реша же Ему: кое убо Ты твориши знамение, да видим и веру имем Тебе? Что делаеши?
Sai suka ce masa, “To wace alama za ka yi, don mu gani mu gaskata ka?
31 Отцы наши ядоша манну в пустыни, якоже есть писано: хлеб с небесе даде им ясти.
Me za ka yi? Kakanninmu sun ci manna a jeji, kamar yadda aka rubuta, “Ya ba su gurasa daga sama su ci.”
32 Рече убо им Иисус: аминь, аминь глаголю вам, не Моисей даде вам хлеб с небесе, но Отец Мой дает вам хлеб истинный с небесе:
Sa'an nan Yesu ya ce masu, “hakika, hakika, ina gaya maku ba Musa ne ya ba ku gurasa nan daga sama ba, amma Ubana ne ya baku gurasa ta gaskiya daga sama.
33 хлеб бо Божии есть сходяй с небесе и даяй живот миру.
Gurasar Allah itace mai saukowa daga sama mai kuma bada rai ga duniya,”
34 Реша убо к Нему: Господи, всегда даждь нам хлеб сей.
Sai suka ce masa, “Mallam, ka rika ba mu irin wannan gurasa kodayaushe.”
35 Рече же им Иисус: Аз есмь хлеб животный: грядый ко Мне не имать взалкатися, и веруяй в Мя не имать вжаждатися никогдаже.
Yesu ya ce masu, “Ni ne gurasa mai ba da rai. Wanda ya zo wurina ba zai ji yunwa ba, wanda kuma ya gaskanta da ni ba zai kara jin kishi ba.
36 Но рех вам, яко и видесте Мя, и не веруете.
Amma na gaya maku cewa, hakika kun gan ni, duk da haka ba ku ba da gaskiya ba.
37 Все, еже дает Мне Отец, ко Мне приидет, и грядущаго ко Мне не изжену вон:
Duk wanda Uba ya bani zai zo gare ni, wanda kuwa ya zo gare ni ba zan kore shi ba ko kadan.
38 яко снидох с небесе, не да творю волю Мою, но волю пославшаго Мя Отца.
Gama na sauko daga sama, ba domin in bi nufin kaina ba, sai dai nufin wanda ya aiko ni.
39 Се же есть воля пославшаго Мя Отца, да все, еже даде Ми, не погублю от Него, но воскрешу е в последний день.
Wannan shi ne nufin wanda ya aiko ni, kada in rasa ko daya daga cikin wadannan da ya bani, sai dai in tashe su a ranar karshe.
40 Се же есть воля Пославшаго Мя, да всяк видяй Сына и веруяй в Него имать живот вечный, и воскрешу его Аз в последний день. (aiōnios g166)
Gama wannan shi ne nufin Ubana, duk wanda yake ganin Dan ya kuma gaskata da shi zai sami rai madawwami, ni kuma zan tashe shi a ranar karshe. (aiōnios g166)
41 Роптаху убо Иудее о Нем, яко рече: Аз есмь хлеб сшедый с небесе.
Sai Yahudawa suka yi gunaguni akansa, domin ya ce, “Nine Gurasar da ta sauko daga sama.”
42 И глаголаху: не Сей ли есть Иисус сын Иосифов, Егоже мы знаем отца и Матерь? Како убо глаголет Сей, яко с небесе снидох?
Suka ce, “Ba wannan ne Yesu Dan Yusufu, wanda Ubansa da Uwarsa mun san su ba? Ta yaya yanzu zai ce, 'Na ya sauko daga sama'?
43 Отвеща убо Иисус и рече им: не ропщите между собою:
Yesu ya amsa, ya ce masu, “Kada ku yi gunaguni a junanku.
44 никтоже может приити ко Мне, аще не Отец пославый Мя привлечет его, и Аз воскрешу его в последний день.
Ba mai iya zuwa wurina sai dai in Uba wanda ya aiko ni ya jawo shi, ni kuwa zan tashe shi a rana ta karshe.
45 Есть писано во пророцех: и будут вси научени Богом. Всяк слышавый от Отца и навык, приидет ко Мне.
A rubuce yake cikin litattafan anabawa cewa, 'Dukkansu Allah zai koya masu'. Duk wanda ya ji ya kuma koya daga wurin Uba, ya kan zo gare ni.
46 Не яко Отца видел есть Кто, токмо сый от Бога, Сей виде Отца.
Ba cewa wani ya taba ganin Uban ba, sai shi wanda yake daga wurin Allah - shine ya ga Uban.
47 Аминь, аминь глаголю вам: веруяй в Мя имать живот вечный. (aiōnios g166)
Hakika, hakika, wanda ya bada gaskiya, yana da rai Madawwami. (aiōnios g166)
48 Аз есмь хлеб животный:
Ni ne Gurasa ta rai.
49 отцы ваши ядоша манну в пустыни и умроша:
Ubanninku sun ci manna cikin jeji, suka kuma mutu.
50 сей есть хлеб сходяй с небесе, да, аще кто от него яст, не умрет:
Ga gurasa da ta sauko daga sama, domin mutum ya ci daga cikinta ba kuwa zai mutu ba.
51 Аз есмь хлеб животный, иже сшедый с небесе: аще кто снесть от хлеба сего, жив будет во веки: и хлеб, егоже Аз дам, Плоть Моя есть, юже Аз дам за живот мира. (aiōn g165)
Ni ne gurasa mai rai da ya sauko daga sama. Duk wanda ya ci daga gurasar, zai rayu har abada. Wannan gurasar da zan bayar jiki na ne don ceton duniya.” (aiōn g165)
52 Пряхуся же между собою Жидове, глаголюще: како может Сей нам дати Плоть (Свою) ясти?
Sai Yahudawa suka fusata a tsakanin junansu suka kuma fara gardama, cewa, “Yaya mutumin nan zai iya bamu naman jikinsa mu ci?
53 Рече же им Иисус: аминь, аминь глаголю вам: аще не снесте Плоти Сына Человеческаго, ни пиете Крове Его, живота не имате в себе.
Sai Yesu ya ce masu, “hakika, hakika, in ba ku ci naman jikin Dan mutum ba, ba ku kuma sha jininsa ba, ba za ku sami rai a cikin ku ba.
54 Ядый Мою Плоть и пияй Мою Кровь имать живот вечный, и Аз воскрешу его в последний день. (aiōnios g166)
Dukan wanda ya ci nama na ya kuma sha jinina yana da rai Madawwami, ni kuwa zan tashe shi a ranar karshe. (aiōnios g166)
55 Плоть бо Моя истинно есть брашно, и Кровь Моя истинно есть пиво.
Domin namana abinci ne na gaske, jinina kuma abin sha ne na gaskiya.
56 Ядый Мою Плоть и пияй Мою Кровь во Мне пребывает, и Аз в нем.
Duk wanda ya ci namana, ya kuma sha jinina yana zamne a ciki na, ni kuma a cikinsa.
57 Якоже посла Мя живый Отец, и Аз живу Отца ради: и ядый Мя, и той жив будет Мене ради.
Kamar yadda rayayyen Uba ya aiko ni, nake kuma rayuwa saboda Uban, haka ma wanda ya ci namana, zai rayu sabo da ni.
58 Сей есть хлеб сшедый с небесе: не якоже ядоша отцы ваши манну и умроша: ядый хлеб сей жив будет во веки. (aiōn g165)
Wannan itace gurasar da ta sauko daga sama, ba irin wadda Ubanninku suka ci suka mutu ba. Dukan wanda ya ci gurasar zai rayu har abada.” (aiōn g165)
59 Сия рече на сонмищи, учя в Капернауме.
Yesu ya fadi wadan nan abubuwa a cikin majami'a sa'ad da yake koyarwa a Kafarnahum.
60 Мнози убо слышавше от ученик Его, реша: жестоко есть слово сие: (и) кто может Его послушати?
Da jin haka, da yawa daga cikin almajiransa suka ce, “Wannan Magana yana da karfi, wa zai iya jinta?”
61 Ведый же Иисус в Себе, яко ропщут о сем ученицы Его, рече им: сие ли вы блазнит?
Yesu, kuwa da yake ya sani a ransa da cewa almajiransa suna gunagunin wannan, sai ya ce masu, “Wannan ya zamar maku laifi?
62 Аще убо узрите Сына Человеческаго восходяща, идеже бе прежде?
Yaya Ke nan in kun ga Dan Mutum yana hawa inda yake a da?
63 Дух есть, иже оживляет, плоть не пользует ничтоже: глаголголы, яже Аз глаголах вам, дух суть и живот суть:
Ruhu shine mai bayar da rai; Jiki ba ya amfana komai. Kalmomin da na fada maku ruhu ne, da kuma rai.
64 но суть от вас нецыи, иже не веруют. Ведяше бо искони Иисус, кии суть неверующии, и кто есть предаяй Его.
Amma fa akwai wadansun ku da ba su ba da gaskiya ba. Domin tun farko Yesu ya san wadanda ba su ba da gaskiya ba, da kuma wanda zai bashe shi.
65 И глаголаше: сего ради рех вам, яко никтоже может приити ко Мне, аще не будет ему дано от Отца Моего.
Ya fada cewa, “shiyasa na gaya maku, ba mai iya zuwa wurina, sai ta wurin Uban.”
66 От сего мнози от ученик Его идоша вспять и ктому не хождаху с Ним.
Bayan haka, da yawa daga cikin almajiransa suka koma da baya, ba su kara tafiya tare da shi ba.
67 Рече же Иисус обеманадесяте: еда и вы хощете ити?
Sai Yesu ya ce wa goma sha biyun, “ku ba kwa so ku tafi, ko ba haka ba?
68 Отвеща убо Ему Симон Петр: Господи, к кому идем? Глаголголы живота вечнаго имаши, (aiōnios g166)
Bitrus ya amsa masa ya ce, “Ya Ubangiji, gun wa za mu je? kai kake da maganar rai madawwami. (aiōnios g166)
69 и мы веровахом и познахом, яко Ты еси Христос, Сын Бога живаго.
Mu kwa mun gaskata mun kuma sani kai ne mai tsarkin nan na Allah.”
70 Отвеща им Иисус: не Аз ли вас дванадесяте избрах? И един от вас диавол есть.
Yesu ya ce masu, “Ba ni na zabe ku, goma sha biyu ba, amma dayanku Iblis ne?”
71 Глаголаше же Иуду Симонова Искариота: сей бо хотяше предати Его, един сый от обоюнадесяте.
Wato yana magana akan Yahuda dan Siman Iskariyoti, shi kuwa daya daga cikin sha-biyun ne, wanda zai ba da Yesu.

< От Иоанна святое благовествование 6 >