< mathiH 18 >

1 tadAnIM ziSyA yIzOH samIpamAgatya pRSTavantaH svargarAjyE kaH zrESThaH?
A lokacin nan sai almajirai suka zo wurin Yesu suka yi tambaya suka ce, “Wane ne mafi girma a mulkin sama?”
2 tatO yIzuH kSudramEkaM bAlakaM svasamIpamAnIya tESAM madhyE nidhAya jagAda,
Sai ya kira ƙaramin yaro ya sa shi yă tsaya a tsakiyarsu.
3 yuSmAnahaM satyaM bravImi, yUyaM manOvinimayEna kSudrabAlavat na santaH svargarAjyaM pravESTuM na zaknutha|
Sai ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, in ba kun canja kuka zama kamar ƙananan yara ba, labudda, ba za ku shiga mulkin sama ba.
4 yaH kazcid Etasya kSudrabAlakasya samamAtmAnaM namrIkarOti, saEva svargarAjayE zrESThaH|
Saboda haka, duk wanda ya ƙasƙantar da kansa kamar wannan yaro, shi ne mafi girma a mulkin sama.
5 yaH kazcid EtAdRzaM kSudrabAlakamEkaM mama nAmni gRhlAti, sa mAmEva gRhlAti|
Duk kuma wanda ya karɓi ƙaramin yaro kamar wannan a cikin sunana ya karɓe ni ne.
6 kintu yO janO mayi kRtavizvAsAnAmEtESAM kSudraprANinAm EkasyApi vidhniM janayati, kaNThabaddhapESaNIkasya tasya sAgarAgAdhajalE majjanaM zrEyaH|
“Amma duk wanda ya sa ɗaya daga cikin ƙananan nan da suka gaskata da ni ya yi zunubi, zai fiye masa a rataya babban dutsen niƙa a wuyarsa, a kuma nutsar da shi a zurfin teku.
7 vighnAt jagataH santApO bhaviSyati, vighnO'vazyaM janayiSyatE, kintu yEna manujEna vighnO janiSyatE tasyaiva santApO bhaviSyati|
Kaiton duniya saboda abubuwan da suke sa mutane su yi zunubi! Dole irin waɗannan abubuwa su zo, sai dai kaiton mutumin da ya zama sanadin kawo su!
8 tasmAt tava karazcaraNO vA yadi tvAM bAdhatE, tarhi taM chittvA nikSipa, dvikarasya dvipadasya vA tavAnaptavahnau nikSEpAt, khanjjasya vA chinnahastasya tava jIvanE pravEzO varaM| (aiōnios g166)
In hannunka ko ƙafarka yana sa ka zunubi, yanke shi ka yar. Zai fiye maka ka shiga rai da hannu ko ƙafa ɗaya da hannuwa biyu ko ƙafafu biyu da a jefar da kai cikin madawwamiyar wuta da hannuwa biyu ko ƙafafu biyu. (aiōnios g166)
9 aparaM tava nEtraM yadi tvAM bAdhatE, tarhi tadapyutpAvya nikSipa, dvinEtrasya narakAgnau nikSEpAt kANasya tava jIvanE pravEzO varaM| (Geenna g1067)
In kuma idonka yana sa ka zunubi, ƙwaƙule shi ka yar. Zai fiye maka ka shiga rai da ido ɗaya, da ka shiga jahannama ta wuta da idanunka biyu. (Geenna g1067)
10 tasmAdavadhaddhaM, EtESAM kSudraprANinAm Ekamapi mA tucchIkuruta,
“Ku lura, kada ku rena ɗaya daga cikin waɗannan ƙanana. Gama ina faɗa muku mala’ikunsu a sama kullum suna duban fuskar Ubana da yake cikin sama.
11 yatO yuSmAnahaM tathyaM bravImi, svargE tESAM dUtA mama svargasthasya piturAsyaM nityaM pazyanti| EvaM yE yE hAritAstAn rakSituM manujaputra Agacchat|
12 yUyamatra kiM viviMgghvE? kasyacid yadi zataM mESAH santi, tESAmEkO hAryyatE ca, tarhi sa EkOnazataM mESAn vihAya parvvataM gatvA taM hAritamEkaM kiM na mRgayatE?
“Me kuka gani? In wani yana da tumaki ɗari, sai ɗaya daga cikinsu ta ɓace, ba sai yă bar tasa’in da taran a kan tuddai yă je neman guda ɗayan da ta ɓace ba?
13 yadi ca kadAcit tanmESOddEzaM lamatE, tarhi yuSmAnahaM satyaM kathayAmi, sO'vipathagAmibhya EkOnazatamESEbhyOpi tadEkahEtOradhikam AhlAdatE|
In kuwa ya same ta, ina gaya muku gaskiya, zai yi murna saboda ɗayan fiye da tasa’in da taran da ba su ɓace ba.
14 tadvad EtESAM kSudraprAEnAm EkOpi nazyatIti yuSmAkaM svargasthapitu rnAbhimatam|
Haka ma Ubanku da yake cikin sama ba ya so ko ɗaya daga cikin ƙananan nan yă ɓace.
15 yadyapi tava bhrAtA tvayi kimapyaparAdhyati, tarhi gatvA yuvayOrdvayOH sthitayOstasyAparAdhaM taM jnjApaya| tatra sa yadi tava vAkyaM zRNOti, tarhi tvaM svabhrAtaraM prAptavAn,
“In ɗan’uwanka ya yi maka laifi, ka je ka nuna masa laifinsa, tsakaninku biyu kaɗai. In ya saurare ka, ka maido da ɗan’uwanka ke nan.
16 kintu yadi na zRNOti, tarhi dvAbhyAM tribhi rvA sAkSIbhiH sarvvaM vAkyaM yathA nizcitaM jAyatE, tadartham EkaM dvau vA sAkSiNau gRhItvA yAhi|
Amma in bai saurare ka ba, ka je tare da mutum ɗaya ko biyu, domin ‘a tabbatar da kowace magana a bakin shaidu biyu ko uku.’
17 tEna sa yadi tayO rvAkyaM na mAnyatE, tarhi samAjaM tajjnjApaya, kintu yadi samAjasyApi vAkyaM na mAnyatE, tarhi sa tava samIpE dEvapUjakaiva caNPAlaiva ca bhaviSyati|
In kuwa ya ƙi yă saurare su, sai ka gaya wa ikkilisiya; in kuma ya ƙi yă saurari ikkilisiya ma, ka yi da shi kamar marar sanin Allah ko mai karɓar haraji.
18 ahaM yuSmAn satyaM vadAmi, yuSmAbhiH pRthivyAM yad badhyatE tat svargE bhaMtsyatE; mEdinyAM yat bhOcyatE, svargE'pi tat mOkSyatE|
“Gaskiya nake gaya muku, duk abin da kuka daure a duniya, za a daure a sama, duk kuma abin da kuka kunce a duniya, za a kunce shi a sama.
19 punarahaM yuSmAn vadAmi, mEdinyAM yuSmAkaM yadi dvAvEkavAkyIbhUya kinjcit prArthayEtE, tarhi mama svargasthapitrA tat tayOH kRtE sampannaM bhaviSyati|
“Har wa yau, ina gaya muku cewa in mutum biyu a cikinku a duniya suka yarda su roƙi wani abu, Ubana da yake cikin sama zai yi muku.
20 yatO yatra dvau trayO vA mama nAnni milanti, tatraivAhaM tESAM madhyE'smi|
Gama inda mutum biyu ko uku suka taru cikin sunana, a can ma ina tare da su.”
21 tadAnIM pitarastatsamIpamAgatya kathitavAn hE prabhO, mama bhrAtA mama yadyaparAdhyati, tarhi taM katikRtvaH kSamiSyE?
Sai Bitrus ya zo wurin Yesu ya yi masa tambaya ya ce, “Ubangiji, sau nawa zan yafe wa ɗan’uwana sa’ad da ya yi mini zunubi? Har sau bakwai?”
22 kiM saptakRtvaH? yIzustaM jagAda, tvAM kEvalaM saptakRtvO yAvat na vadAmi, kintu saptatyA guNitaM saptakRtvO yAvat|
Yesu amsa ya ce, “Ina gaya maka, ba sau bakwai ba, amma sau saba’in da bakwai.
23 aparaM nijadAsaiH saha jigaNayiSuH kazcid rAjEva svargarAjayaM|
“Saboda haka, mulkin sama yana kama da wani sarki wanda ya so yă yi ƙididdigar dukiyarsa da take a hannun bayinsa.
24 ArabdhE tasmin gaNanE sArddhasahasramudrApUritAnAM dazasahasrapuTakAnAm EkO'ghamarNastatsamakSamAnAyi|
Da ya fara ƙididdigar, sai aka kawo masa wani wanda yake bin bashin talenti dubu goma.
25 tasya parizOdhanAya dravyAbhAvAt parizOdhanArthaM sa tadIyabhAryyAputrAdisarvvasvanjca vikrIyatAmiti tatprabhurAdidEza|
Da yake bai iya biya ba, sai maigida ya umarta a sayar da shi da matarsa da yaransa da kuma duk abin da yake da shi, a biya bashin.
26 tEna sa dAsastasya pAdayOH patan praNamya kathitavAn, hE prabhO bhavatA ghairyyE kRtE mayA sarvvaM parizOdhiSyatE|
“Bawan ya durƙusa a gabansa. Ya yi roƙo ya ce, ‘Ka yi mini haƙuri, zan biya ka ƙaf.’
27 tadAnIM dAsasya prabhuH sakaruNaH san sakalarNaM kSamitvA taM tatyAja|
Maigidan bawan ya ji tausayinsa, ya yafe masa bashin, ya kuma sake shi.
28 kintu tasmin dAsE bahi ryAtE, tasya zataM mudrAcaturthAMzAn yO dhArayati, taM sahadAsaM dRSdvA tasya kaNThaM niSpIPya gaditavAn, mama yat prApyaM tat parizOdhaya|
“Amma da wannan bawa ya fita, sai ya gamu da wani abokin bautarsa wanda yake binsa bashin dinari ɗari. Sai ya cafke shi, ya shaƙe shi a wuya yana cewa, ‘Biya ni abin da nake binka!’
29 tadA tasya sahadAsastatpAdayOH patitvA vinIya babhASE, tvayA dhairyyE kRtE mayA sarvvaM parizOdhiSyatE|
“Wannan abokin bautarsa ya durƙusa ya roƙe shi, ‘Ka yi mini haƙuri, zan biya ka.’
30 tathApi sa tat nAgagIkRtya yAvat sarvvamRNaM na parizOdhitavAn tAvat taM kArAyAM sthApayAmAsa|
“Amma ya ƙi. A maimako, sai ya je ya sa aka jefa shi a kurkuku, har yă biya bashin.
31 tadA tasya sahadAsAstasyaitAdRg AcaraNaM vilOkya prabhOH samIpaM gatvA sarvvaM vRttAntaM nivEdayAmAsuH|
Sa’ad da sauran bayin suka ga abin da ya faru, abin ya ɓata musu rai ƙwarai, sai suka tafi suka faɗa wa maigidansu dukan abin da ya faru.
32 tadA tasya prabhustamAhUya jagAda, rE duSTa dAsa, tvayA matsannidhau prArthitE mayA tava sarvvamRNaM tyaktaM;
“Sai maigidan ya kira wannan bawa. Ya ce, ‘Kai mugun bawa, na yafe duk bashin da nake binka domin ka roƙe ni.
33 yathA cAhaM tvayi karuNAM kRtavAn, tathaiva tvatsahadAsE karuNAkaraNaM kiM tava nOcitaM?
Ashe, bai kamata kai ma ka ji tausayin abokin bautarka yadda na yi maka ba?’
34 iti kathayitvA tasya prabhuH kruddhyan nijaprApyaM yAvat sa na parizOdhitavAn, tAvat prahArakAnAM karESu taM samarpitavAn|
Cikin fushi, maigidan ya miƙa shi ga ma’aikatan kurkuku su gwada masa azaba, har yă biya dukan bashin da ake binsa.
35 yadi yUyaM svAntaHkaraNaiH svasvasahajAnAm aparAdhAn na kSamadhvE, tarhi mama svargasyaH pitApi yuSmAn pratItthaM kariSyati|
“Haka Ubana da yake cikin sama zai yi da kowannenku, in ba ku yafe wa’yan’uwanku daga zuciyarku ba.”

< mathiH 18 >