< 7 >

1 Porventura não tem o homem guerra sobre a terra? e não são os seus dias como os dias do jornaleiro?
“Mutum bai sha wahalar aiki ba a duniya? Rayuwarsa ba kamar ta wanda aka yi hayarsa ba ne?
2 Como o cervo que suspira pela sombra, e como o jornaleiro que espera pela sua paga,
Kamar yadda bawa yakan jira yamma ta yi, ko kuma kamar yadda wanda aka yi hayarsa yakan jira a biya shi kuɗin aikin da ya yi.
3 Assim me deram por herança mezes de vaidade: e noites de trabalho me prepararam.
Saboda haka rabona shi ne watanni na zama banza, kowane dare kuwa sai ɓacin rai nake samu.
4 Deitando-me a dormir, então digo, Quando me levantarei? mas comprida é a noite, e farto-me de me voltar na cama até á alva.
Lokacin da na kwanta ina tunani, ‘Har sai yaushe zan tashi?’ Gari ya ƙi wayewa, ina ta jujjuyawa har safe.
5 A minha carne se tem vestido de bichos e de torrões de pó: a minha pelle está gretada, e se fez abominavel.
Jikina duk tsutsotsi da ƙuraje sun rufe shi, fatar jikina ta ruɓe tana fitar da ruwan miki.
6 Os meus dias são mais velozes do que a lançadeira do tecelão, e pereceram sem esperança.
“Kwanakina suna wucewa da sauri, fiye da yadda ƙoshiyar masaƙa take wucewa da sauri, za su kawo ga ƙarshe ba bege.
7 Lembra-te de que a minha vida é como o vento; os meus olhos não tornarão a ver o bem.
Ka tuna, ya Allah, raina numfashi ne kawai; idanuna ba za su taɓa sāke ganin farin ciki ba.
8 Os olhos dos que agora me vêem não me verão mais: os teus olhos estarão sobre mim, porém não serei mais.
Idanun da suke ganina yanzu ba za su sāke ganina ba; za ku neme ni amma ba za ku same ni ba.
9 Assim como a nuvem se desfaz e passa, assim aquelle que desce á sepultura nunca tornará a subir. (Sheol h7585)
Kamar yadda girgije yakan ɓace yă tafi, haka mutum yake shige zuwa kabari ba kuwa zai dawo ba. (Sheol h7585)
10 Nunca mais tornará á sua casa, nem o seu logar jámais o conhecerá.
Ba zai taɓa zuwa gidansa ba; ba za a sāke san da shi ba.
11 Por isso não reprimirei a minha bocca: fallarei na angustia do meu espirito; queixar-me-hei na amargura da minha alma.
“Saboda haka ba zan yi shiru ba; zan yi magana cikin ɓacin raina, zan nuna ɓacin raina cikin ruhu, cikin ƙuncin raina.
12 Sou eu porventura o mar, ou a baleia, para que me ponhas uma guarda?
Ni teku ne, ko kuwa dodon ruwa, don me kake tsaro na?
13 Dizendo eu: Consolar-me-ha a minha cama: meu leito alliviará a minha ancia;
Lokacin da nake zato zan sami salama in na kwanta a gadona don in huta,
14 Então me espantas com sonhos, e com visões me assombras:
duk da haka kana ba ni tsoro da mafarke-mafarke, kana tsorata ni da wahayi.
15 Pelo que a minha alma escolheria antes a estrangulação: e antes a morte do que a vida.
Na gwammace a shaƙe ni in mutu maimakon in kasance cikin wannan jiki.
16 A minha vida abomino, pois não viveria para sempre: retira-te de mim; pois vaidade são os meus dias.
Ba na so in zauna da rai; ba zan rayu ba har abada. Ku rabu da ni; rayuwata ba ta da amfani.
17 Que é o homem, para que tanto o estimes, e ponhas sobre elle o teu coração,
“Mene ne mutum har da ka kula da shi haka, har ka mai da hankali a kansa,
18 E cada manhã o visites, e cada momento o proves?
har kake duba shi kowace safiya, kake kuma gwada shi koyaushe?
19 Até quando me não deixarás, nem me largarás, até que engula o meu cuspo?
Ba za ka ɗan daina kallo na ba ko ka rabu da ni na ɗan lokaci?
20 Se pequei, que te farei, ó Guarda dos homens? porque fizeste de mim um alvo para ti por tropeço, para que a mim mesmo me seja pesado?
In na yi zunubi, me na yi maka, kai mai lura da mutane? Don me ka sa ni a gaba? Na zame maka kaya mai nauyi ne?
21 E porque me não perdoas a minha transgressão, e não tiras a minha iniquidade? porque agora me deitarei no pó, e de madrugada me buscarás, e não estarei lá.
Me ya sa ba za ka gafarta mini laifofina ba? Gama na kusa kwantawa cikin ƙasa; za ka neme ni, amma ba za ka same ni ba.”

< 7 >