< مزامیر 91 >

آنکه در ستر حضرت اعلی نشسته است، زیر سایه قادرمطلق ساکن خواهد بود. ۱ 1
Shi wanda yake zama a wurin Mafi Ɗaukaka zai huta a cikin inuwar Maɗaukaki.
درباره خداوند می‌گویم که او ملجاو قلعه من است و خدای من که بر او توکل دارم. ۲ 2
Zan ce game da Ubangiji, “Shi ne mafakata da kagarata, Allahna, wanda nake dogara.”
زیرا که او تو را از دام صیاد خواهد رهانید و ازوبای خبیث. ۳ 3
Tabbatacce zai cece ka daga tarkon mai farauta da kuma daga cututtuka masu kisa.
به پرهای خود تو را خواهدپوشانید و زیر بالهایش پناه خواهی گرفت. راستی او تو را مجن و سپر خواهد بود. ۴ 4
Zai rufe ka da fikafikansa, a ƙarƙashin fikafikansa kuwa za ka sami mafaka; amincinsa zai zama maka garkuwa da katanga.
از خوفی درشب نخواهی ترسید و نه از تیری که در روزمی پرد. ۵ 5
Ba za ka ji tsoron razanar dare, ko kibiyoyi da suke firiya da rana ba,
و نه از وبایی که در تاریکی می‌خرامد ونه از طاعونی که وقت ظهر فساد می‌کند. ۶ 6
ko bala’in da yake aukowa cikin duhu, ko annobar da take hallakarwa da tsakar rana.
هزارنفر به‌جانب تو خواهند افتاد و ده هزار به‌دست راست تو. لیکن نزد تو نخواهد رسید. ۷ 7
Dubu za su iya fāɗuwa a gefenka, dubu goma a hannun damanka, amma ba abin da zai zo kusa da kai.
فقط به چشمان خود خواهی نگریست و پاداش شریران را خواهی دید. ۸ 8
Za ka dai gan da idanunka yadda ake hukunta mugaye.
زیرا گفتی تو‌ای خداوندملجای من هستی و حضرت اعلی را ماوای خویش گردانیده‌ای. ۹ 9
In ka mai da Mafi Ɗaukaka wurin zamanka, har ma Ubangiji wanda yake mafakata,
هیچ بدی بر تو واقع نخواهد شد و بلایی نزد خیمه تو نخواهد رسید. ۱۰ 10
to, babu wani mugun abin da zai same ka, ba masifar da za tă zo kusa da tentinka.
زیرا که فرشتگان خود را درباره تو امر خواهدفرمود تا در تمامی راههایت تو را حفظ نمایند. ۱۱ 11
Gama zai umarci mala’ikunsa game da kai don su tsare ka a dukan hanyoyinka;
تو را بر دستهای خود برخواهند داشت، مباداپای خود را به سنگ بزنی. ۱۲ 12
za su tallafe ka da hannuwansu, don kada ka buga ƙafarka a kan dutse.
بر شیر و افعی پای خواهی نهاد؛ شیربچه و اژدها را پایمال خواهی کرد. ۱۳ 13
Za ka taka zaki da gamsheƙa; za ka tattake babban zaki da maciji.
«چونکه به من رغبت دارد او را خواهم رهانید و چونکه به اسم من عارف است او راسرافراز خواهم ساخت. ۱۴ 14
Ubangiji ya ce, “Domin ya ƙaunace ni, zan kuɓutar da shi; zan kiyaye shi, gama ya yarda da sunana.
چون مرا خواند او رااجابت خواهم کرد. من در تنگی با او خواهم بود واو را نجات داده، معزز خواهم ساخت. ۱۵ 15
Zai kira bisa sunana, zan kuma amsa masa; zan kasance tare da shi a lokacin wahala, zan kuɓutar da shi in kuma girmama shi.
به طول ایام او را سیر می‌گردانم و نجات خویش را بدونشان خواهم داد.» ۱۶ 16
Da tsawon rai zan ƙosar da shi in kuma nuna masa cetona.”

< مزامیر 91 >