< مزامیر 116 >

خداوند را محبت می‌نمایم زیرا که آواز من و تضرع مرا شنیده است. ۱ 1
Ina ƙaunar Ubangiji, gama ya ji muryata; ya ji kukata ta neman jinƙai.
زیرا که گوش خود را به من فرا داشته است، پس مدت حیات خود، او را خواهم خواند. ۲ 2
Domin ya juye kunnensa gare ni, zan kira gare shi muddin ina da rai.
ریسمان های موت مرا احاطه کرد و تنگیهای هاویه مرا دریافت، تنگی و غم پیدا کردم. (Sheol h7585) ۳ 3
Igiyoyin mutuwa sun shaƙe ni, wahalar kabari sun zo a kaina; na cika da wahala da ɓacin rai. (Sheol h7585)
آنگاه نام خداوند را خواندم. آه‌ای خداوند جان مرارهایی ده! ۴ 4
Sai na kira ga sunan Ubangiji na ce, “Ya Ubangiji, ka cece ni!”
خداوند رئوف و عادل است و خدای ما رحیم است. ۵ 5
Ubangiji mai alheri ne da kuma mai adalci; Allahnmu yana cike da tausayi.
خداوند ساده دلان را محافظت می‌کند. ذلیل بودم و مرا نجات داد. ۶ 6
Ubangiji yana tsare masu tawali’u; sa’ad da nake cikin tsananin bukata, ya cece ni.
‌ای جان من به آرامی خود برگرد، زیراخداوند به تو احسان نموده است. ۷ 7
Ka kwantar da hankali, ya raina, gama Ubangiji mai alheri ne a gare ka.
زیرا که جان مرا از موت خلاصی دادی و چشمانم را از اشک و پایهایم را از لغزیدن. ۸ 8
Gama kai, ya Ubangiji, ka ceci raina daga mutuwa, idanuna daga hawaye, ƙafafuna daga tuntuɓe,
به حضور خداوند سالک خواهم بود، در زمین زندگان. ۹ 9
don in iya tafiya a gaban Ubangiji a ƙasar masu rai.
ایمان آوردم پس سخن گفتم. من بسیار مستمند شدم. ۱۰ 10
Na gaskata, saboda haka na ce, “An azabtar da ni ƙwarai.”
درپریشانی خود گفتم که «جمیع آدمیان دروغ گویند.» ۱۱ 11
Kuma cikin rikicewana na ce, “Dukan mutane maƙaryata ne.”
خداوند را چه ادا کنم، برای همه احسانهایی که به من نموده است؟ ۱۲ 12
Yaya zan sāka wa Ubangiji saboda dukan alherinsa gare ni?
پیاله نجات را خواهم گرفت و نام خداوند را خواهم خواند. ۱۳ 13
Zan daga kwaf na ceto in kuma kira ga sunan Ubangiji.
نذرهای خود را به خداوند ادا خواهم کرد، به حضور تمامی قوم او. ۱۴ 14
Zan cika alkawurana ga Ubangiji a gaban dukan mutanensa.
موت مقدسان خداونددر نظر وی گرانبها است. ۱۵ 15
Abu mai daraja a gaban Ubangiji shi ne mutuwar tsarkakansa.
آه‌ای خداوند، من بنده تو هستم! من بنده تو و پسر کنیز تو هستم. بندهای مرا گشوده‌ای! ۱۶ 16
Ya Ubangiji, da gaske ni bawanka ne; ni bawanka ne, ɗan baiwarka; ka’yantar da ni daga sarƙoƙi.
قربانی های تشکر نزدتو خواهم گذرانید و نام خداوند را خواهم خواند. ۱۷ 17
Zan yi hadayar godiya gare ka in kuma kira bisa sunan Ubangiji.
نذرهای خود را به خداوند ادا خواهم کرد، به حضور تمامی قوم وی، ۱۸ 18
Zan cika alkawurana ga Ubangiji a gaban dukan mutanensa,
در صحن های خانه خداوند، در اندرون تو‌ای اورشلیم. هللویاه! ۱۹ 19
a filayen gidan Ubangiji, a tsakiyarki, ya Urushalima. Yabi Ubangiji.

< مزامیر 116 >