< اعداد 10 >

و خداوند موسی را خطاب کرده، گفت: ۱ 1
Ubangiji ya ce wa Musa,
«برای خود دو کرنای نقره بساز، آنهارا از چرخکاری درست کن، و آنها را بجهت خواندن جماعت و کوچیدن اردو بکار ببر. ۲ 2
“Ka ƙera kakaki guda biyu na azurfa, ka kuma yi amfani da su don kira taron jama’a wuri ɗaya, don kuma ka riƙa sanar da su lokacin tashi daga sansani.
وچون آنها را بنوازند تمامی جماعت نزد تو به درخیمه اجتماع جمع شوند. ۳ 3
Sa’ad da aka busa su biyu, dukan jama’a za su taru a gabanka a ƙofar Tentin Sujada.
و چون یکی رابنوازند، سروران و روسای هزاره های اسرائیل نزد تو جمع شوند. ۴ 4
In ɗaya ne kaɗai aka busa, sai shugabannin kabilan Isra’ila, su taru a gabanka.
و چون تیز آهنگ بنوازیدمحله هایی که به طرف مشرق جا دارند، کوچ بکنند. ۵ 5
Sa’ad da aka ji karar busar kakaki, sai sansanin da yake a gabashi, su kama hanya.
و چون مرتبه دوم تیز آهنگ بنوازید، محله هایی که به طرف جنوب جا دارند کوچ کنند؛ بجهت کوچ دادن ایشان تیز آهنگ بنوازند. ۶ 6
A kara ta biyu, sansanin da yake a kudanci, su kama hanya. Busan kakaki zai zama alama ta kama hanya.
و بجهت جمع کردن جماعت بنوازید، لیکن تیزآهنگ منوازید. ۷ 7
In don a tara jama’a ne, sai a busa kakaki, amma ba da irin alama ɗaya ba.
«و بنی هارون کهنه، کرناها را بنوازند. این برای شما در نسلهای شما فریضه ابدی باشد. ۸ 8
“’Ya’yan Haruna, firistoci ne, za su busa kakaki. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla gare ku da kuma tsararraki masu zuwa.
وچون در زمین خود برای مقاتله با دشمنی که برشما تعدی می‌نمایند می‌روید، کرناها را تیزآهنگ بنوازید، پس به حضور یهوه خدای خودبیاد آورده خواهید شد، و از دشمنان خود نجات خواهید یافت. ۹ 9
Duk lokacin da za ku tafi yaƙi a ƙasarku, in akwai waɗansu da suke matsa muku, za ku yi amfani da waɗannan kakaki ta wurin hura su, alama ce, cewa za a je yaƙi. Sa’an nan Ubangiji Allahnku zai tuna da ku, yă cece ku daga maƙiyanku.
و در روز شادی خود و درعیدها و در اول ماه های خود کرناها را برقربانی های سوختنی و ذبایح سلامتی خودبنوازید، تا برای شما به حضور خدای شمایادگاری باشد. من یهوه خدای شما هستم.» ۱۰ 10
Haka ma in kuna cikin jin daɗinku, musamman lokacin da kuke bukukkuwanku, kamar Bikin Sabon Wata da dai kowane Bikinku, za ku hura waɗannan kakaki lokacin da kuke miƙa hadayunku na ƙonawa, da hadayunku na salama, za su kuma zama muku abin tunawa a gaban Allahnku. Ni ne Ubangiji Allahnku.”
و واقع شد در روز بیستم ماه دوم سال دوم که ابر از بالای خیمه شهادت برداشته شد، ۱۱ 11
A rana ta ashirin ga wata na biyu, a shekara ta biyu, sai girgijen ya tashi daga tabanakul na Shaida.
وبنی‌اسرائیل به مراحل خود از صحرای سینا کوچ کردند، و ابر در صحرای فاران ساکن شد، ۱۲ 12
Sai Isra’ilawa suka tashi daki-daki daga Hamadar Sinai, suna tafiya daga wuri zuwa wuri, har sai da girgijen ya tsaya a Hamadar Faran.
وایشان اول به فرمان خداوند به واسطه موسی کوچ کردند. ۱۳ 13
Suka kama hanya, a wannan lokaci, bisa umarnin Ubangiji, ta wurin Musa.
و علم محله بنی یهودا، اول با افواج ایشان روانه شد، و بر فوج او نحشون بن عمیناداب بود. ۱۴ 14
Ɓangarorin sansanin Yahuda suka fara tashi, bisa ga ƙa’idar da aka yi, aka kuma umarta. Nashon ɗan Amminadab ne shugaba.
و بر فوج سبط بنی یساکار، نتنائیل بن صوغر. ۱۵ 15
Netanel ɗan Zuwar ne shugaban ɓangaren kabilar Issakar,
و بر فوج سبط بنی زبولون، الیاب بن حیلون. ۱۶ 16
Eliyab ɗan Helon kuma shi ne shugaban ɓangaren kabilar Zebulun.
پس مسکن را پایین آوردند و بنی جرشون وبنی مراری که حاملان مسکن بودند، کوچ کردند. ۱۷ 17
Sa’an nan aka saukar da tabanakul ƙasa, Gershonawa da mutanen Merari da suke ɗauke da shi suka kama hanya.
و علم محله روبین با افواج ایشان روانه شد، و بر فوج او الیصور بن شدیئور بود. ۱۸ 18
Sai ɓangarori sansanin Ruben suka biyo, bisa ga ƙa’idar da aka yi, aka kuma umarta. Elizur ɗan Shedeyur ne shugaba.
و بر فوج سبط بنی شمعون، شلومیئیل بن صوریشدای. ۱۹ 19
Shelumiyel ɗan Zurishaddai ne shugaban ɓangaren kabilar Simeyon,
و بر فوج سبط بنی جاد، الیاساف بن دعوئیل. ۲۰ 20
Eliyasaf ɗan Deyuwel kuma shi ne shugaban ɓangaren kabilar Gad.
پس قهاتیان که حاملان قدس بودند، کوچ کردند و پیش از رسیدن ایشان، آنها مسکن را برپاداشتند. ۲۱ 21
Sai Kohatawa suka kama hanya, ɗauke da kayayyaki masu tsarki, domin kafin su kai wurin da za a kafa sansani, a riga an kafa tabanakul.
پس علم محله بنی افرایم با افواج ایشان روانه شد، و بر فوج او الیشمع بن عمیهود بود. ۲۲ 22
Biye da waɗannan kuma sai ɓangaren sansanin kabilar Efraim suka biyo bisa ga ƙa’ida da aka yi, aka kuma umarta. Elishama ɗan Ammihud ne shugaba.
و بر فوج سبط بنی منسی، جملیئیل بن فدهصور. ۲۳ 23
Gamaliyel ɗan Fedazur ne shugaban ɓangaren kabilar Manasse,
و بر فوج سبط بنی بنیامین، ابیدان بن جدعونی. ۲۴ 24
Abidan ɗan Gideyoni kuma shi ne shugaban ɓangaren kabilar Benyamin.
پس علم محله بنی دان که موخر همه محله‌ها بود با افواج ایشان روانه شد، و بر فوج اواخیعزر بن عمیشدای بود. ۲۵ 25
A ƙarshe, a matsayi masu gadin bayan dukan ɓangarori, sai ɓangaren sansanin Dan suka tashi bisa ga ƙa’idar da aka yi, aka kuma umarta. Ahiyezer ɗan Ammishaddai ne shugaba.
و بر فوج سبطبنی اشیر، فجعیئیل بن عکران. ۲۶ 26
Fagiyel ɗan Okran ne shugaban ɓangaren kabilan Asher,
و بر فوج سبطبنی نفتالی، اخیرع بن عینان. ۲۷ 27
Ahira ɗan Enan kuma shi ne shugaban kabilar Naftali.
این بود مراحل بنی‌اسرائیل با افواج ایشان. پس کوچ کردند. ۲۸ 28
Wannan shi ne tsarin tafiyar ɓangarorin Isra’ilawa, sa’ad da sukan kama hanya.
و موسی به حوباب بن رعوئیل مدیانی که برادرزن موسی بود، گفت: «ما به مکانی که خداوند درباره آن گفته است که آن را به شماخواهم بخشید کوچ می‌کنیم، همراه ما بیا و بتواحسان خواهیم نمود، چونکه خداوند درباره اسرائیل نیکو گفته است.» ۲۹ 29
Sai Musa ya ce wa Hobab ɗan Reyuwel Bamidiyane surukinsa, “Yanzu fa, muna shirin tashi ne daga nan, domin mu tafi inda Ubangiji ya ce, ‘Zan ba ku.’ Ka zo tare da mu, za mu kuwa yi maka alheri, gama Ubangiji ya yi wa Isra’ilawa alkawari abubuwa masu kyau.”
او وی را گفت: «نمی آیم، بلکه به زمین و به خاندان خود خواهم رفت.» ۳۰ 30
Ya amsa, ya ce “A’a, ba zan tafi ba; zan koma ƙasata da kuma wurin mutanena.”
گفت: «ما را ترک مکن زیرا چونکه تو منازل ما را در صحرا می‌دانی، بجهت ما مثل چشم خواهی بود. ۳۱ 31
Amma Musa ya ce, “Ina roƙonka kada ka rabu da mu. Ka san inda ya kamata mu kafa sansani a hamada, za ka kuma zama idanunmu.
و اگر همراه ما بیایی، هر احسانی که خداوند بر ما بنماید، همان را بر تو خواهیم نمود.» ۳۲ 32
In ka zo tare da mu, za mu raba duk abin alherin Ubangiji ya ba mu tare da kai.”
و از کوه خداوند سفر سه روزه کوچ کردند، و تابوت عهد خداوند سفر سه روزه پیش روی ایشان رفت تا آرامگاهی برای ایشان بطلبد. ۳۳ 33
Saboda haka suka kama hanya daga dutsen Ubangiji, suka yi tafiya kwana uku. Akwatin alkawarin Ubangiji ya ja gabansu a waɗannan kwanaki uku, don yă samo musu masauƙi.
و ابر خداوند در روز بالای سر ایشان بود، و وقتی که از لشکرگاه روانه می‌شدند. ۳۴ 34
A duk lokacin da suka tashi daga sansani, girgijen Ubangiji ya inuwantar da su da rana.
و چون تابوت روانه می‌شد، موسی می‌گفت: «ای خداوند برخیز و دشمنانت پراکنده شوند و مبغضانت از حضور تو منهزم گردند.» ۳۵ 35
Duk kuma sa’ad da akwatin ya kama hanya, sai Musa ya ce, “Ka tashi, ya Ubangiji! Ka sa maƙiyanka su warwatse; masu ƙinka kuma su gudu a gabanka.”
و چون فرود می‌آمد، می‌گفت: «ای خداوند نزد هزاران هزار اسرائیل رجوع نما.» ۳۶ 36
Duk sa’ad da akwatin ya sauka kuma, sai Musa ya ce, “Ka komo, ya Ubangiji, a wurin dubban da ba a iya ƙidayawa na iyalan Isra’ila.”

< اعداد 10 >