< لوقا 22 >

و چون عید فطیر که به فصح معروف است نزدیک شد، ۱ 1
Yanzu fa, Bikin Burodi Marar Yistin da ake kira Bikin Ƙetarewa ya yi kusa,
روسای کهنه وکاتبان مترصد می‌بودند که چگونه او را به قتل رسانند، زیرا که از قوم ترسیدند. ۲ 2
manyan firistoci da malaman dokoki kuma suna neman yadda za su kashe Yesu a ɓoye, don suna tsoron mutane.
اما شیطان در یهودای مسمی به اسخریوطی که از‌جمله آن دوازده بود داخل گشت، ۳ 3
Shaiɗan kuwa ya shiga Yahuda, wanda ake kira Iskariyot, ɗaya daga cikin Sha Biyun.
و اورفته با روسای کهنه و سرداران سپاه گفتگو کرد که چگونه او را به ایشان تسلیم کند. ۴ 4
Sai Yahuda ya je ya tattauna da manyan firistoci, da ma’aikatan’yan gadin haikali, a kan yadda zai ba da Yesu a gare su.
ایشان شادشده با او عهد بستند که نقدی به وی دهند. ۵ 5
Suka kuwa yi murna, suka yarda su ba shi kuɗi.
و اوقبول کرده در صدد فرصتی برآمد که اورا درنهانی از مردم به ایشان تسلیم کند. ۶ 6
Ya ko yarda, ya fara neman zarafin da zai ba da Yesu a gare su, sa’ad da taro ba sa nan tare da shi.
اما چون روز فطیر که در آن می‌بایست فصح را ذبح کنند رسید، ۷ 7
Sai ranar Bikin Burodi Marar Yisti ta kewayo, wato, ranar hadayar ɗan ragon kafara na Bikin Ƙetarewa.
پطرس و یوحنا را فرستاده، گفت: «بروید و فصح را بجهت ما آماده کنید تابخوریم.» ۸ 8
Sai Yesu ya aiki Bitrus da Yohanna, ya ce musu, “Ku je ku yi shirye-shiryen Bikin Ƙetarewar da za mu ci.”
به وی گفتند: «در کجا می‌خواهی مهیا کنیم؟» ۹ 9
Suka tambaye shi suka ce, “Ina kake so mu je mu yi shirin?”
ایشان را گفت: «اینک هنگامی که داخل شهر شوید، شخصی با سبوی آب به شمابرمی خورد. به خانه‌ای که او درآید، از عقب وی بروید، ۱۰ 10
Ya amsa ya ce, “Sa’ad da kuka shiga cikin gari, za ku sadu da wani mutum yana ɗauke da tulun ruwa. Ku bi shi zuwa gidan da zai shiga.
و به صاحب‌خانه گویید، استاد تو را می گوید مهمانخانه کجا است تا در آن فصح را باشاگردان خود بخورم. ۱۱ 11
Ku ce wa maigidan, Malam ya aike mu mu ce maka, ‘Ina ɗakin baƙi, inda ni da almajiraina za mu ci abincin Bikin Ƙetarewa?’
او بالاخانه‌ای بزرگ ومفروش به شما نشان خواهد داد در آنجا مهیاسازید.» ۱۲ 12
Zai nuna muku wani babban ɗakin sama a shirye. Nan za ku yi shirin.”
پس رفته چنانکه به ایشان گفته بودیافتند و فصح را آماده کردند. ۱۳ 13
Sai suka tafi, suka kuma iske kome kamar yadda Yesu ya faɗa musu. Sai suka shirya Bikin Ƙetarewa.
و چون وقت رسید با دوازده رسول بنشست. ۱۴ 14
Da lokaci ya yi, sai Yesu ya zauna tare da manzanninsa don cin abinci.
و به ایشان گفت: «اشتیاق بی‌نهایت داشتم که پیش از زحمت دیدنم، این فصح را باشما بخورم. ۱۵ 15
Sai ya ce musu, “Na yi marmari ƙwarai don in ci wannan Bikin Ƙetarewa tare da ku, kafin in sha wahala.
زیرا به شما می‌گویم از این دیگرنمی خورم تا وقتی که در ملکوت خدا تمام شود.» ۱۶ 16
Ina dai gaya muku, ba zan ƙara cinsa ba, sai ya sami cika a mulkin Allah.”
پس پیاله‌ای گرفته، شکر نمود و گفت: «این رابگیرید و در میان خود تقسیم کنید. ۱۷ 17
Bayan ya ɗauki kwaf ruwan inabi, ya yi godiya, sai ya ce, “Ku karɓa, ku rarraba wa junanku.
زیرا به شما می‌گویم که تا ملکوت خدا نیاید، از میوه مودیگر نخواهم نوشید.» ۱۸ 18
Ina dai gaya muku, ba zan ƙara sha daga’ya’yan inabi ba, sai mulkin Allah ya zo.”
و نان را گرفته، شکرنمود و پاره کرده، به ایشان داد و گفت: «این است جسد من که برای شما داده می‌شود، این را به یادمن به‌جا آرید.» ۱۹ 19
Sai ya ɗauki burodi ya yi godiya, ya kakkarya ya ba su, da cewa, “Wannan jikina ne, da aka bayar dominku. Ku riƙa yin haka don tunawa da ni.”
و همچنین بعد از شام پیاله راگرفت و گفت: «این پیاله عهد جدید است در خون من که برای شما ریخته می‌شود. ۲۰ 20
Haka kuma, bayan abincin, ya ɗauki kwaf ruwan inabi ya ce, “Wannan kwaf ruwan inabi shi ne, na sabon alkawari cikin jinina, da aka zubar dominku.
لیکن اینک دست آن کسی‌که مرا تسلیم می‌کند با من در سفره است. ۲۱ 21
Amma hannun wanda zai ci amanata, yana cin abincin tare da ni.
زیرا که پسر انسان برحسب آنچه مقدراست، می‌رود لیکن وای بر آن کسی‌که او را تسلیم کند.» ۲۲ 22
Ɗan Mutum zai mutu kamar yadda aka ƙaddara, amma kaiton mutumin da zai bashe shi.”
آنگاه از یکدیگر شروع کردند به پرسیدن که کدام‌یک از ایشان باشد که این کار بکند؟ ۲۳ 23
Sai suka fara tambayar junansu, ko wane ne a cikinsu zai yi wannan.
و در میان ایشان نزاعی نیز افتاد که کدام‌یک ازایشان بزرگتر می‌باشد؟ ۲۴ 24
Gardama ta tashi a tsakaninsu, a kan ko wane ne a cikinsu ya fi girma.
آنگاه به ایشان گفت: «سلاطین امت‌ها بر ایشان سروری می‌کنند وحکام خود را ولی‌نعمت می‌خوانند. ۲۵ 25
Yesu ya ce musu, “Sarakunan Al’ummai suna nuna iko a kan mutanensu, kuma waɗanda suke nuna iko a kansu, suna kiran kansu Masu Taimakon mutane.
لیکن شماچنین مباشید، بلکه بزرگتر از شما مثل کوچکترباشد و پیشوا چون خادم. ۲۶ 26
Amma ku, kada ku zama haka. A maimakon haka, sai dai wanda ya fi girma a cikinku, ya zama kamar wanda ya fi ƙanƙanta, wanda kuma ke mulki, ya zama kamar mai hidima.
زیرا کدام‌یک بزرگتراست آنکه به غذا نشیند یا آنکه خدمت کند آیانیست آنکه نشسته است؟ لیکن من در میان شماچون خادم هستم. ۲۷ 27
Wane ne ya fi girma? Wanda yake zaune a tebur ne, ko kuma shi da yake yin hidima? Ashe, ba wanda yake zaune a tebur ba ne? Amma ga ni, ni mai yin hidima ne a cikinku.
و شما کسانی می‌باشید که در امتحانهای من با من به‌سر بردید. ۲۸ 28
Ku ne kuka tsaya tare da ni a gwaje-gwajen da na sha.
و من ملکوتی برای شما قرار می‌دهم چنانکه پدرم برای من مقرر فرمود. ۲۹ 29
Daidai kamar yadda Ubana ya ba ni mulki, haka ni ma nake ba ku.
تا در ملکوت من از خوان من بخورید و بنوشید و بر کرسیها نشسته بردوازده سبط اسرائیل داوری کنید.» ۳۰ 30
Saboda ku ci, ku sha a teburina a cikin mulkina. Kuma ku zauna a kan gadon sarauta, ku yi wa kabilu goma sha biyu na Isra’ila shari’a.
پس خداوند گفت: «ای شمعون، ای شمعون، اینک شیطان خواست شما را چون گندم غربال کند، ۳۱ 31
“Siman, Siman, Shaiɗan ya nemi izini ya sheƙe kakamar alkama.
لیکن من برای تو دعا کردم تاایمانت تلف نشود و هنگامی که تو بازگشت کنی برادران خود را استوار نما.» ۳۲ 32
Amma na yi maka addu’a, Siman, domin kada bangaskiyarka ta kāsa. Bayan ka juyo, ka ƙarfafa’yan’uwanka.”
به وی گفت: «ای خداوند حاضرم که با تو بروم حتی در زندان و درموت.» ۳۳ 33
Amma ya amsa ya ce, “Ubangiji, ina a shirye in tafi tare da kai har kurkuku, ko mutuwa ma.”
گفت: «تو را می‌گویم‌ای پطرس امروزخروس بانگ نزده باشد که سه مرتبه انکار خواهی کرد که مرا نمی شناسی.» ۳۴ 34
Yesu ya ce, “Ina gaya maka Bitrus, kafin zakara ya yi cara yau, za ka yi mūsun sanina sau uku.”
و به ایشان گفت: «هنگامی که شما را بی‌کیسه و توشه‌دان و کفش فرستادم به هیچ‌چیز محتاج شدید؟» گفتند هیچ. ۳۵ 35
Sai Yesu ya tambaye, su ya ce, “Lokacin da na aike ku ba tare da jakar kuɗi, ko jaka, ko takalma ba, kun rasa wani abu?” Suka amsa, “Babu.”
پس به ایشان گفت: «لیکن الان هر‌که کیسه دارد، آن را بردارد و همچنین توشه‌دان را و کسی‌که شمشیر ندارد جامه خود را فروخته آن رابخرد. ۳۶ 36
Ya ce musu, “Amma yanzu, in kuna da jakar kuɗi, ko jaka, ku ɗauka. In kuma ba ku da takobi, ku sayar da rigarku, ku saya.
زیرا به شما می‌گویم که این نوشته در من می‌باید به انجام رسید، یعنی با گناهکاران محسوب شد زیرا هر‌چه در خصوص من است، انقضا دارد. ۳۷ 37
A rubuce yake cewa, ‘An lissafta shi tare da masu zunubi.’ Ina kuwa gaya muku, dole wannan ya cika a kaina. I, abin da aka rubuta a kaina yana kusan cikawa.”
گفتند: «ای خداوند اینک دوشمشیر.» به ایشان گفت: «کافی است.» ۳۸ 38
Almajiran suka ce, “Duba Ubangiji, ga takuba biyu.” Yesu ya ce, “Ya isa.”
و برحسب عادت بیرون شده به کوه زیتون رفت و شاگردانش از عقب او رفتند. ۳۹ 39
Yesu ya fita zuwa Dutsen Zaitun kamar yadda ya saba, almajiransa kuma suka bi shi.
و چون به آن موضع رسید، به ایشان گفت: «دعا کنید تا درامتحان نیفتید.» ۴۰ 40
Da ya kai wurin, sai ya ce musu, “Ku yi addu’a don kada ku fāɗi cikin jarraba.”
و او از ایشان به مسافت پرتاپ سنگی دور شده، به زانو درآمد و دعا کرده، گفت: ۴۱ 41
Sai ya janye daga wurinsu, misalin nisan jifa, ya durƙusa a ƙasa ya yi addu’a,
«ای پدر اگر بخواهی این پیاله را از من بگردان، لیکن نه به خواهش من بلکه به اراده تو.» ۴۲ 42
“Uba, in ka yarda, ka ɗauke mini wannan kwaf, amma ba nufina ba, sai dai naka.”
وفرشته‌ای از آسمان بر او ظاهر شده او را تقویت می‌نمود. ۴۳ 43
Wani mala’ika daga sama ya bayyana gare shi, ya ƙarfafa shi.
پس به مجاهده افتاده به سعی بلیغتردعا کرد، چنانکه عرق او مثل قطرات خون بود که بر زمین می‌ریخت. ۴۴ 44
Domin tsananin azaba, sai ya ƙara himma cikin addu’a, zuffansa kuma na ɗigowa ƙasa kamar jini.
پس از دعا برخاسته نزدشاگردان خود آمده ایشان را از حزن در خواب یافت. ۴۵ 45
Da ya tashi daga addu’a, ya koma inda almajiransa suke, sai ya iske su suna barci, daga gajiyar baƙin ciki.
به ایشان گفت: «برای چه در خواب هستید؟ برخاسته دعا کنید تا در امتحان نیفتید.» ۴۶ 46
Ya tambaye su, “Don me kuke barci? Ku tashi ku yi addu’a, don kada ku fāɗi cikin jarraba.”
و سخن هنوز بر زبانش بود که ناگاه جمعی آمدند و یکی از آن دوازده که یهودا نام داشت بردیگران سبقت جسته نزد عیسی آمد تا او راببوسد. ۴۷ 47
Yana cikin magana sai ga taro sun zo. Mutumin nan da ake kira Yahuda, ɗaya daga cikin Sha Biyun, shi ya bi da su. Sai ya matso kusa da Yesu don yă yi masa sumba.
و عیسی بدو گفت: «ای یهودا آیا به بوسه پسر انسان را تسلیم می‌کنی؟» ۴۸ 48
Amma Yesu ya tambaye shi ya ce, “Yahuda, ashe, da sumba za ka bashe Ɗan Mutum?”
رفقایش چون دیدند که چه می‌شود عرض کردند خداوندابه شمشیر بزنیم. ۴۹ 49
Da masu bin Yesu suka ga abin da zai faru, sai suka ce, “Ubangiji, mu yi sara da takubanmu ne?”
و یکی از ایشان، غلام رئیس کهنه را زده، گوش راست او را از تن جدا کرد. ۵۰ 50
Sai ɗayansu ya kai sara ga bawan babban firist, ya sare kunnen damansa.
عیسی متوجه شده گفت: «تا به این بگذارید.» وگوش او را لمس نموده، شفا داد. ۵۱ 51
Amma Yesu ya amsa ya ce, “Kada a ƙara yin wannan!” Sai ya taɓa kunnen mutumin da aka sara, ya warkar da shi.
پس عیسی به روسای کهنه و سرداران سپاه هیکل و مشایخی که نزد او آمده بودند گفت: «گویا بر دزد با شمشیرها و چوبها بیرون آمدید. ۵۲ 52
Sai Yesu ya ce wa manyan firistoci, da ma’aikatan’yan gadin haikali, da dattawa, waɗanda suka zo don su kama shi, “Ina jagoran wani tawaye ne, da za ku zo da takuba da sanduna?
وقتی که هر روزه در هیکل با شما می‌بودم دست بر من دراز نکردید، لیکن این است ساعت شما و قدرت ظلمت.» ۵۳ 53
Kullum ina tare da ku a filin haikali, amma ba ku kama ni ba. Amma wannan ne sa’a naku, lokacin da duhu yake mulki.”
پس او را گرفته بردند و به‌سرای رئیس کهنه آوردند و پطرس از دور از عقب می‌آمد. ۵۴ 54
Sai suka kama shi suka kai shi gidan babban firist. Bitrus ya bi su daga nesa.
و چون در میان ایوان آتش افروخته گردش نشسته بودند، پطرس در میان ایشان بنشست. ۵۵ 55
Amma da suka hura wuta a tsakiyar harabar gidan, kowa ya zauna, sai Bitrus ya zo ya zauna tare da su.
آنگاه کنیزکی چون او را در روشنی آتش نشسته دید بر او چشم دوخته گفت: «این شخص هم با او می‌بود.» ۵۶ 56
Wata baiwa ta gan shi zaune kusa da wutar. Ta dube shi sosai sa’an nan, ta ce, “Ai, wannan mutum ma yana tare da shi.”
او وی را انکار کرده گفت: «ای زن او را نمی شناسم.» ۵۷ 57
Amma ya yi mūsu ya ce, “Mace, ban san shi ba!”
بعد از زمانی دیگری او را دیده گفت: «تو از اینها هستی.» پطرس گفت: «ای مرد، من نیستم.» ۵۸ 58
Bayan ɗan lokaci kaɗan, wani dabam ya gan shi ya ce, “Kai ma ɗayansu ne.” Bitrus ya amsa ya ce, “Kai, ba na cikinsu!”
و چون تخمین یک ساعت گذشت یکی دیگر با تاکیدگفت: «بلاشک این شخص از رفقای او است زیراکه جلیلی هم هست.» ۵۹ 59
Bayan kamar sa’a ɗaya, sai wani mutum ya ce, “Ba shakka, mutumin nan ma yana tare da shi, don shi mutumin Galili ne.”
پطرس گفت: «ای مردنمی دانم چه می‌گویی؟» در همان ساعت که این رامی گفت خروس بانگ زد. ۶۰ 60
Bitrus ya amsa ya ce, “Kai, ban ma san abin da kake magana a kai ba!” Yana cikin magana, sai zakara ya yi cara.
آنگاه خداوندروگردانیده به پطرس نظر افکند پس پطرس آن کلامی را که خداوند به وی گفته بود به‌خاطرآورد که قبل از بانگ زدن خروس سه مرتبه مراانکار خواهی کرد. ۶۱ 61
Ubangiji kuma ya juya ya kafa wa Bitrus ido. Sai Bitrus ya tuna da maganar da Ubangiji ya ce masa, “Kafin zakara ya yi cara yau, za ka yi mūsun sanina sau uku.”
پس پطرس بیرون رفته زارزار بگریست. ۶۲ 62
Sai ya fita waje, ya yi kuka mai zafi.
و کسانی که عیسی را گرفته بودند، او راتازیانه زده استهزا نمودند. ۶۳ 63
Mutanen da suke gadin Yesu suka fara masa ba’a da dūka.
و چشم او را بسته طپانچه بر رویش زدند و از وی سوال کرده، گفتند: «نبوت کن که تو را زده است؟» ۶۴ 64
Suka rufe masa idanu suna tambaya cewa, “Ka yi annabci! Wa ya mare ka?”
و بسیارکفر دیگر به وی گفتند. ۶۵ 65
Suka kuma yi masa waɗansu baƙaƙen maganganu masu yawa.
و چون روز شد اهل شورای قوم یعنی روسای کهنه و کاتبان فراهم آمده در مجلس خوداو را آورده، ۶۶ 66
Da gari ya waye, sai majalisar dattawa na mutane, da manyan firistoci, da malaman dokoki, suka taru wuri ɗaya. Sai aka kawo Yesu a gabansu.
گفتند: «اگر تو مسیح هستی به مابگو: «او به ایشان گفت: «اگر به شما گویم مراتصدیق نخواهید کرد. ۶۷ 67
Suka ce, “Ka faɗa mana, ko kai ne Kiristi?” Yesu ya amsa ya ce, “Ko na gaya muku, ba za ku gaskata ni ba,
و اگر از شما سوال کنم جواب نمی دهید و مرا رها نمی کنید. ۶۸ 68
in kuma na yi muku tambaya ba za ku iya ba ni amsa ba.
لیکن بعداز این پسر انسان به طرف راست قوت خداخواهد نشست.» ۶۹ 69
Amma daga yanzu, Ɗan Mutum zai zauna a hannun dama na Allah Mai Iko.”
همه گفتند: «پس تو پسر خداهستی؟» او به ایشان گفت: «شما می‌گویید که من هستم.» ۷۰ 70
Sai dukansu suka yi tambaya suka ce, “Wato, kai Ɗan Allah ke nan?” Ya amsa ya ce, “Kun faɗa daidai, ni ne.”
گفتند: «دیگر ما را چه حاجت به شهادت است، زیرا خود از زبانش شنیدیم.» ۷۱ 71
Sai suka ce, “Wace shaida kuma muke nema? Ai, mun ji abin da ya ce da bakinsa.”

< لوقا 22 >