< لوقا 19 >

پس وارد اریحا شده، از آنجا می گذشت. ۱ 1
Yesu ya shiga Yeriko, yana ratsa ta cikinta.
که ناگاه شخصی زکی نام که رئیس باجگیران و دولتمند بود، ۲ 2
Akwai wani mutum a garin, mai suna Zakka. Shi shugaban masu karɓar haraji ne, mai arziki kuma.
خواست عیسی را ببیند که کیست و از کثرت خلق نتوانست، زیرا کوتاه قد بود. ۳ 3
Ya so yă ga ko wane ne Yesu, amma saboda taron, bai iya ba, domin shi gajere ne.
پس پیش دویده بردرخت افراغی برآمد تا او را ببیند. چونکه اومی خواست از آن راه عبور کند. ۴ 4
Saboda haka, ya yi gaba da gudu, kuma ya hau itacen sikamo, don yă gan shi, tun da Yesu zai bi wannan hanyar ne.
و چون عیسی به آن مکان رسید، بالا نگریسته او را دید و گفت: «ای زکی بشتاب و به زیر بیا زیرا که باید امروز درخانه تو بمانم.» ۵ 5
Da Yesu ya iso wurin, sai ya ɗaga ido sama, ya ce masa, “Zakka, ka yi maza ka sauka. Ni kam, dole in sauka a gidanka yau.”
پس به زودی پایین شده او را به خرمی پذیرفت. ۶ 6
Sai ya sauka nan da nan, ya karɓe shi da murna.
و همه چون این را دیدند، همهمه‌کنان می‌گفتند که در خانه شخصی گناهکار به میهمانی رفته است. ۷ 7
Dukan mutane suka ga haka, kuma suka fara gunaguni, suka ce, “Ya je don yă zama baƙon ‘mai zunubi.’”
اما زکی برپا شده به خداوند گفت: «الحال‌ای خداوند نصف مایملک خود را به فقرامی دهم و اگر چیزی ناحق از کسی گرفته باشم، چهار برابر بدو رد می‌کنم.» ۸ 8
Amma Zakka ya tashi a tsaye, ya ce wa Ubangiji, “Duba, Ubangiji! Nan take, rabin dukiyar da nake da shi, na ba wa matalauta. In kuma na taɓa cutan wani, a kan wani abu, zan mayar da shi ninki huɗu.”
عیسی به وی گفت: «امروز نجات در این خانه پیدا شد. زیرا که این شخص هم پسر ابراهیم است. ۹ 9
Sai Yesu ya ce masa, “Yau, ceto ya zo gidan nan, domin wannan mutum shi ma ɗan Ibrahim ne.
زیرا که پسرانسان آمده است تا گمشده را بجوید و نجات‌بخشد.» ۱۰ 10
Saboda Ɗan Mutum ya zo ne, domin yă nemi abin da ya ɓata, yă cece shi kuma.”
و چون ایشان این را شنیدند او مثلی زیادکرده آورد چونکه نزدیک به اورشلیم بود و ایشان گمان می‌بردند که ملکوت خدا می‌باید در همان زمان ظهور کند. ۱۱ 11
Yayinda suna cikin sauraron wannan, sai ya ci gaba da gaya musu wani misali, domin ya yi kusa da Urushalima, kuma mutanen suna tsammani mulkin Allah zai bayyana, nan da nan.
پس گفت: «شخصی شریف به دیار بعید سفر کرد تا ملکی برای خود گرفته مراجعت کند. ۱۲ 12
Ya ce, “Wani mutum mai martaba ya tafi wata ƙasa mai nisa don a naɗa shi sarki sa’an nan ya dawo.
پس ده نفر از غلامان خود راطلبیده ده قنطار به ایشان سپرده فرمود، تجارت کنید تا بیایم. ۱۳ 13
Saboda haka ya kira bayinsa goma ya ba su mina goma. Ya ce, ‘Ku yi kasuwanci da kuɗin nan, sai na dawo.’
اما اهل ولایت او، چونکه او رادشمن می‌داشتند ایلچیان در عقب او فرستاده گفتند، نمی خواهیم این شخص بر ما سلطنت کند. ۱۴ 14
“Amma talakawansa suka ƙi shi, sai suka aikar da wakilai bayansa, domin su ce, ‘Ba mu son wannan mutum ya zama sarkinmu.’
و چون ملک را گرفته مراجعت کرده بود، فرمود تا آن غلامانی را که به ایشان نقد سپرده بودحاضر کنند تا بفهمد هر یک چه سود نموده است. ۱۵ 15
“Duk da haka, aka naɗa shi sarki, sa’an nan ya dawo gida. Sai ya aika aka kira bayin da ya ba su kuɗin, don yă san ribar da suka samu.
پس اولی آمده گفت، ای آقا قنطار تو ده قنطار دیگر نفع آورده است. ۱۶ 16
“Na fari ya zo ya ce, ‘Ranka yă daɗe, minarka ya sami ribar goma.’
بدو گفت آفرین‌ای غلام نیکو. چونکه بر چیز کم امین بودی بر ده شهر حاکم شو. ۱۷ 17
“Maigidan ya amsa ya ce, ‘Madalla, bawana mai kirki! Tun da ka yi aminci a kan abu ƙanƙani, ka yi riƙon birane goma.’
و دیگری آمده گفت، ای آقاقنطار تو پنج قنطار سود کرده است. ۱۸ 18
“Na biyun ya zo ya ce, ‘Ranka yă daɗe, minarka ya sami ribar biyar.’
او را نیزفرمود بر پنج شهر حکمرانی کن. ۱۹ 19
“Maigidansa ya ce, ‘Kai ka yi riƙon birane biyar.’
و سومی آمده گفت، ای آقا اینک قنطار تو موجود است، آن را در پارچه‌ای نگاه داشته‌ام. ۲۰ 20
“Sai wani bawan ya zo ya ce, ‘Ranka yă daɗe, ga minarka. Na ɓoye shi a wani ɗan tsumma.
زیرا که از توترسیدم چونکه مرد تندخویی هستی. آنچه نگذارده‌ای، برمی داری و از آنچه نکاشته‌ای درومی کنی. ۲۱ 21
Na ji tsoronka, don kai mai wuyan sha’ani ne. Kakan ɗauki abin da ba ka ajiye ba, kakan kuma yi girbin abin da ba ka shuka ba.’
به وی گفت، از زبان خودت بر توفتوی می‌دهم، ای غلام شریر. دانسته‌ای که من مرد تندخویی هستم که برمیدارم آنچه رانگذاشته‌ام و درو می‌کنم آنچه را نپاشیده‌ام. ۲۲ 22
“Sai maigidansa, ya amsa ya ce, ‘Zan hukunta ka a kan kalmominka, kai mugun bawa! Ashe, ka san cewa ni mai wuyan sha’ani ne, nakan ɗauka abin da ban ajiye ba, ina kuma girbin abin da ban shuka ba?
پس برای چه نقد مرا نزد صرافان نگذاردی تاچون آیم آن را با سود دریافت کنم؟ ۲۳ 23
Don me ba ka sa kuɗina a wajen ajiya, don in na dawo, in sami riba a kai ba?’
پس به حاضرین فرمود قنطار را از این شخص بگیرید وبه صاحب ده قنطار بدهید. ۲۴ 24
“Sai ya ce wa waɗanda suke tsaye a wajen, ‘Ku karɓi minarsa ku ba wa wanda yake da mina goma.’
به او گفتند‌ای خداوند، وی ده قنطار دارد. ۲۵ 25
“Suka ce, ‘Ranka yă daɗe, ai, yana da guda goma ko!’
زیرا به شمامی گویم به هر‌که دارد داده شود و هر‌که نداردآنچه دارد نیز از او گرفته خواهد شد. ۲۶ 26
“Ya amsa ya ce, ‘Ina gaya muku, duk wanda yake da abu, za a ƙara masa. Amma wanda ba shi da shi kuwa, ko abin da yake da shi ma, za a karɓe.
اما آن دشمنان من که نخواستند من بر ایشان حکمرانی نمایم، در اینجا حاضر ساخته پیش من به قتل رسانید.» ۲۷ 27
Amma waɗannan abokan gābana, waɗanda ba su so in zama sarkinsu ba, ku kawo su nan, ku karkashe su, a gabana.’”
و چون این را گفت، پیش رفته متوجه اورشلیم گردید. ۲۸ 28
Bayan Yesu ya yi wannan magana, sai ya yi gaba zuwa Urushalima.
و چون نزدیک بیت‌فاجی وبیت عنیا بر کوه مسمی به زیتون رسید، دو نفر ازشاگردان خود را فرستاده، ۲۹ 29
Da ya kai kusa da Betfaji da Betani, a tudun da ake kira Dutsen Zaitun, sai ya aiki almajiransa guda biyu, ya ce musu,
گفت: «به آن قریه‌ای که پیش روی شما است بروید و چون داخل آن شدید، کره الاغی بسته خواهید یافت که هیچ‌کس بر آن هرگز سوار نشده. آن را باز کرده بیاورید. ۳۰ 30
“Ku je ƙauyen da yake gaba da ku. Da kuna shiga, za ku tarar da wani ɗan jaki, wadda ba wanda ya taɓa hawa, a daure a wurin. Ku kunce shi ku kawo nan.
و اگر کسی به شما گوید، چرا این راباز می‌کنید، به وی گویید خداوند او را لازم دارد.» ۳۱ 31
In wani ya tambaye ku, ‘Don me kuke kunce shi?’ Ku ce masa, ‘Ubangiji yana bukatarsa.’”
پس فرستادگان رفته آن چنانکه بدیشان گفته بود یافتند. ۳۲ 32
Waɗanda aka aika su yi gaba suka tafi, suka kuwa tarar kamar yadda ya gaya musu.
و چون کره را باز می‌کردند، مالکانش به ایشان گفتند چرا کره را باز می‌کنید؟ ۳۳ 33
Suna cikin kunce ɗan jakin, sai masu ɗan jakin suka ce musu, “Don me kuke kunce shi?”
گفتند خداوند او را لازم دارد. ۳۴ 34
Suka amsa suka ce, “Ubangiji ne na bukatarsa.”
پس او را به نزد عیسی آوردند و رخت خود را بر کره افکنده، عیسی را سوار کردند. ۳۵ 35
Suka kawo shi wurin Yesu. Suka sa rigunarsu a kan ɗan jakin, sa’an nan suka sa Yesu a kai.
و هنگامی که او می‌رفت جامه های خود را در راه می‌گستردند. ۳۶ 36
Yana cikin tafiya, sai mutane suka shimfiɗa rigunarsu a kan hanya.
و چون نزدیک به‌سرازیری کوه زیتون رسید، تمامی شاگردانش شادی کرده، به آوازبلند خدا را حمد گفتن شروع کردند، به‌سبب همه قواتی که از او دیده بودند. ۳۷ 37
Da ya yi kusa da wurin da hanyar ta gangara zuwa Dutsen Zaitun, sai dukan taron almajirai suka fara yabon Allah, da muryoyi masu ƙarfi, da murna, saboda dukan ayyukan banmamaki da suka gani. Suna cewa,
و می‌گفتند مبارک باد آن پادشاهی که می‌آید، به نام خداوند سلامتی در آسمان و جلال در اعلی علیین باد. ۳۸ 38
“Mai albarka ne sarki wanda yake zuwa cikin sunan Ubangiji!” “Salama ta kasance a sama, da ɗaukaka kuma a can cikin sama!”
آنگاه بعضی از فریسیان از آن میان بدو گفتند: «ای استاد شاگردان خود را نهیب نما.» ۳۹ 39
Sai waɗansu Farisiyawa a cikin taron suka ce wa Yesu, “Malam, ka kwaɓi almajiranka!”
او درجواب ایشان گفت: «به شما می‌گویم اگراینها ساکت شوند، هرآینه سنگها به صداآیند.» ۴۰ 40
Ya amsa ya ce, “Ina gaya muku, ko da sun yi shiru, duwatsu za su fara kirari.”
و چون نزدیک شده، شهر را نظاره کرد برآن گریان گشته، ۴۱ 41
Da ya yi kusa da Urushalima, ya kuma ga birnin, sai ya yi kuka a kanta,
گفت: «اگر تو نیز می‌دانستی هم در این زمان خود آنچه باعث سلامتی تومیشد، لاکن الحال از چشمان تو پنهان گشته است. ۴۲ 42
kuma ya ce, “In ke, ko ke ɗin ma, dā ma kin san abin da zai kawo miki salama a wannan rana, amma yanzu an ɓoye shi daga idanunki.
زیرا ایامی بر تو می‌آید که دشمنانت گرد تو سنگرها سازند و تو را احاطه کرده از هرجانب محاصره خواهند نمود. ۴۳ 43
Ranakun za su auko miki, a lokacin da abokan gābanki za su gina bango gāba da ke, su kuma kewaye inda kike, za su kuma tsare kowane gefenki, su sa ke a tsakiya.
و تو را وفرزندانت را در اندرون تو بر خاک خواهند افکندو در تو سنگی بر سنگی نخواهند گذاشت زیرا که ایام تفقد خود را ندانستی.» ۴۴ 44
Za su fyaɗa ke a ƙasa, ke da’ya’yan da suke cikin katanganki. Ba za su bar wani dutse a kan wani ba, saboda ba ki gane da lokacin da Allah zai ziyarce ki ba.”
و چون داخل هیکل شد، کسانی را که درآنجا خرید و فروش می‌کردند، به بیرون نمودن آغاز کرد. ۴۵ 45
Sai ya shiga filin haikali, ya fara korar masu sayar da kaya.
و به ایشان گفت: «مکتوب است که خانه من خانه عبادت است لیکن شما آن را مغاره دزدان ساخته‌اید.» ۴۶ 46
Ya ce musu, “A rubuce, yake cewa, ‘Gidana, zai zama gidan addu’a,’amma ga shi kun mai da shi ‘kogon’yan fashi.’”
و هر روز در هیکل تعلیم می‌داد، اما روسای کهنه و کاتبان و اکابر قوم قصدهلاک نمودن او می‌کردند. ۴۷ 47
Kowace rana, ya yi ta koyarwa a haikalin. Amma manyan firistoci, da malaman dokoki, da shugabannin mutane, suna ƙoƙarin kashe shi.
و نیافتند چه کنندزیرا که تمامی مردم بر او آویخته بودند که از اوبشنوند. ۴۸ 48
Amma ba su sami hanyar yin haka ba, domin kalmominsa sun kama hankalin dukan mutanen.

< لوقا 19 >