< لوقا 15 >

و چون همه باجگیران و گناهکاران به نزدش می‌آمدند تا کلام او را بشنوند، ۱ 1
To sai duk masu karbar haraji da masu zunubi suna ta zuwa wurin Yesu suna sauraronsa.
فریسیان و کاتبان، همهمه‌کنان می‌گفتند: «این شخص، گناهکارن را می‌پذیرد و با ایشان می‌خورد.» ۲ 2
Dukan Farisawa da Marubuta suna ta gunaguni da junansu, cewa, “Wannan mutum yana karbar masu zunubi, har ma tare suke cin abinci.”
پس برای ایشان این مثل را زده، گفت: ۳ 3
Yesu ya fadi wannan misali, ya ce,
«کیست از شما که صد گوسفند داشته باشد و یکی از آنها گم شود که آن نود و نه را درصحرا نگذارد و از عقب آن گمشده نرود تا آن رابیابد؟ ۴ 4
“Idan waninku yana da tumaki dari, sai dayarsu ta bace, wato ba zai bar tasa'in da taran nan a makiyaya, ya bi sawun wadda ta bata gudan nan har sai ya same shi ba?
پس چون آن را یافت به شادی بر دوش خود می‌گذارد، ۵ 5
Idan kuwa ya same ta, sai ya dauke ta a kafadarsa yana farin ciki.
و به خانه آمده، دوستان وهمسایگان را می‌طلبد و بدیشان می‌گوید با من شادی کنید زیرا گوسفند گمشده خود را یافته‌ام. ۶ 6
In ya dawo gida, sai ya kira abokansa da makwabta, yace masu, 'Ku taya ni murna don na samo tunkiyata da ta bata.'
به شما می‌گویم که بر این منوال خوشی درآسمان رخ می‌نماید به‌سبب توبه یک گناهکاربیشتر از برای نود و نه عادل که احتیاج به توبه ندارند. ۷ 7
Ina gaya maku, haka kuma za a yi farin ciki a sama, a kan mai zunubi guda da ya tuba, fiye da kan masu adalci tassa'in da tara wadanda ba su bukatar tuba.
یا کدام زن است که ده درهم داشته باشدهرگاه یک درهم گم شود، چراغی افروخته، خانه را جاروب نکند و به دقت تفحص ننماید تا آن رابیابد؟ ۸ 8
Ko kuwa wacce mace ce, in tana da kudi azurfa guda goma, in ta batar da daya, ba za ta kunna fitila ta share gidan, ta yi ta neman shi har sai ta same shi ba?
و چون یافت دوستان و همسایگان خودرا جمع کرده می‌گوید با من شادی کنید زیرادرهم گمشده را پیدا کرده‌ام. ۹ 9
In kuwa ta same shi sai ta tara kawayenta da makwabtanta, ta ce, 'Ku taya ni farin ciki don na sami kudin nan nawa da ya bace.'
همچنین به شمامی گویم شادی برای فرشتگان خدا روی می‌دهدبه‌سبب یک خطاکار که توبه کند.» ۱۰ 10
Haka nake gaya maku, abin farin ciki ne ga mala'ikun Allah idan mai zunubi guda ya tuba.”
باز‌گفت: «شخصی را دو پسر بود. ۱۱ 11
Sai Yesu ya ce, “Akwai wani mutum mai 'ya'ya biyu maza,
روزی پسر کوچک به پدر خود گفت: ای پدر، رصداموالی که باید به من رسد، به من بده. پس اومایملک خود را بر این دو تقسیم کرد. ۱۲ 12
sai karamin ya ce wa mahaifinsa, 'Baba, bani rabona daga cikin dukiyarka.' Sai mahaifinsa ya raba masu dukiyarsa tsakaninsu.
و چندی نگذشت که آن پسر کهتر، آنچه داشت جمع کرده، به ملکی بعید کوچ کرد و به عیاشی ناهنجار، سرمایه خود را تلف نمود. ۱۳ 13
Bayan 'yan kwanaki kadan, sai karamin dan ya tattara duk mallakarsa, ya kama hanya zuwa wata kasa mai nisa. A can ya batas da kudinsa, yana sayan abubuwan da ba ya bukata, ya kuma batas da kudinsa a wajen masha'a.
و چون تمام راصرف نموده بود، قحطی سخت در آن دیارحادث گشت و او به محتاج شدن شروع کرد. ۱۴ 14
Bayan da ya batas da duk abin da ya ke da shi, sai aka yi babbar yunwa a kasar, sai ya shiga fatara.
پس رفته خود را به یکی از اهل آن ملک پیوست. وی او را به املاک خود فرستاد تاگرازبانی کند. ۱۵ 15
Ya je ya mika kansa domin aiki ga wani dan kasar, sai ya aike shi cikin gonakinsa domin ya rika ba aladu abinci.
و آرزو می‌داشت که شکم خودرا از خرنوبی که خوکان می‌خوردند سیر کند وهیچ‌کس او را چیزی نمی داد. ۱۶ 16
Har yayi marmarin ya ci daga cikin barbashin da aladu suke ci, domin babu wanda yake ba shi wani abu ya ci.
«آخر به خود آمده، گفت چقدر از مزدوران پدرم نان فراوان دارند و من از گرسنگی هلاک می‌شوم، ۱۷ 17
Amma da hankalinsa ya dawo, ya ce, 'Barorin mahaifina su nawa ne da suke da abinci isasshe, amma ina nan a nan, ina mutuwa sabili da yunwa!
برخاسته نزد پدر خود می‌روم و بدوخواهم گفت‌ای پدر به آسمان و به حضور تو گناه کرده‌ام، ۱۸ 18
Zan tashi, in tafi gun mahaifina, in ce masa, “Baba, na yi wa sama zunubi, na kuma saba maka.
و دیگر شایسته آن نیستم که پسر توخوانده شوم، مرا چون یکی از مزدوران خودبگیر. ۱۹ 19
Ban cancanci a kara kira na danka ba; ka mai da ni kamar daya daga cikin barorinka.'”
در ساعت برخاسته به سوی پدر خودمتوجه شد. اما هنوز دور بود که پدرش او را دیده، ترحم نمود و دوان دوان آمده او را در آغوش خود کشیده، بوسید. ۲۰ 20
Sai ya tashi, ya taho wurin mahaifinsa. Amma tun yana daga nesa, sai mahaifinsa ya hango shi tausayi ya kama shi, ya ruga a guje, ya rungume shi, ya yi ta sumbatar sa.
پسر وی را گفت، ای پدربه آسمان و به حضور تو گناه کرده‌ام و بعد از این لایق آن نیستم که پسر تو خوانده شوم. ۲۱ 21
Dan kuma ya ce masa, 'Baba, na yi wa sama zunubi, na kuma saba maka. Ban isa a kara kira na danka ba.'
لیکن پدر به غلامان خود گفت، جامه بهترین را از خانه آورده بدو بپوشانید و انگشتری بر دستش کنید ونعلین بر پایهایش، ۲۲ 22
Amma mahaifinsa ya ce wa bayinsa, 'Ku yi hamzari ku kawo riga mafi kyau, ku yafa masa. Ku sa masa zobe a hanunsa da takalma a kafafunsa.
و گوساله پرواری را آورده ذبح کنید تا بخوریم و شادی نماییم. ۲۳ 23
Sa'annan a kawo kiwataccen marakin nan, a yanka. Mu yi buki!
زیرا که این پسر من مرده بود، زنده گردید و گم شده بود، یافت شد. پس به شادی کردن شروع نمودند. ۲۴ 24
Gama da na ya mutu a da, amma yanzu yana a raye. Ya bata a da, amma a yanzu an same shi.' Sai suka fara liyafa.
اما پسر بزرگ او در مزرعه بود. چون آمده نزدیک به خانه رسید، صدای ساز و رقص راشنید. ۲۵ 25
A wannan lokacin, babban dansa yana gona. Da ya kai kusa da gida, ya ji ana kade-kade da raye-raye.
پس یکی از نوکران خود را طلبیده پرسید این چیست؟ ۲۶ 26
Sai ya kira wani bawan gidan, ya tambayi manufar wadannan abubuwa.
به وی عرض کرد برادرت آمده و پدرت گوساله پرواری را ذبح کرده است زیرا که او را صحیح باز‌یافت. ۲۷ 27
Bawan ya ce masa, 'Dan'uwanka ne ya dawo gida, mahaifinka kuma ya yanka kiwataccen marakin nan, saboda ya dawo gida lafiya.'
ولی او خشم نموده نخواست به خانه درآید تا پدرش بیرون آمده به او التماس نمود. ۲۸ 28
Amma dan'uwan ya yi fushi, ya ki ya shiga ciki, mahaifinsa kuwa ya fito, ya roke shi.
اما او در جواب پدرخود گفت، اینک سالها است که من خدمت توکرده‌ام و هرگز از حکم تو تجاوز نورزیده و هرگزبزغاله‌ای به من ندادی تا با دوستان خود شادی کنم. ۲۹ 29
Amma babban dan ya amsa wa ubansa ya ce, 'Duba, duk yawan shekarun nan da nake bauta maka, ban taba karya umarnin ka ba, duk da haka ba ka taba bani ko dan taure da zan yi shagali tare da abokaina ba,
لیکن چون این پسرت آمد که دولت تو رابا فاحشه‌ها تلف کرده است، برای او گوساله پرواری را ذبح کردی. ۳۰ 30
amma da dan nan naka ya zo wanda ya fallasar da dukiyarka a kan karuwai, ka yanka masa kiwataccen marakin nan.
او وی را گفت، ای فرزند تو همیشه با من هستی و آنچه از آن من است، مال تو است. ۳۱ 31
Sai mahaifin ya ce masa, 'Dana, ai kullum kana tare da ni, duk abin da yake nawa naka ne.
ولی می‌بایست شادمانی کرد و مسرور شد زیرا که این برادر تو مرده بود، زنده گشت و گم شده بود، یافت گردید.» ۳۲ 32
Amma, daidai ne a yi murna da farinciki, don dan'uwan nan naka da ya mutu, amma yanzu yana da rai, da ya bata, amma yanzu an same shi.'”

< لوقا 15 >