< ایّوب 14 >

قلیل الایام و پر از زحمات است. ۱ 1
“Mutum haihuwar mace kwanakinsa kaɗan ne, kuma cike da wahala.
مثل گل می‌روید و بریده می‌شود. و مثل سایه می‌گریزد و نمی ماند. ۲ 2
Yana tasowa kamar fure yana kuma shuɗewa; kamar inuwa, ba ya daɗewa.
و آیا بر چنین شخص چشمان خود را می‌گشایی و مرا با خود به محاکمه می‌آوری؟ ۳ 3
Za ka zura ido a kan irin wannan ne? Za ka kawo shi gaba don ka yi masa shari’a?
کیست که چیز طاهر را ازچیز نجس بیرون آورد؟ هیچکس نیست. ۴ 4
Wane ne zai iya kawo abin da yake da tsarki daga cikin abu marar tsarki? Babu!
چونکه روزهایش مقدر است و شماره ماههایش نزد توست و حدی از برایش گذاشته‌ای که از آن تجاوز نتواند نمود. ۵ 5
An lissafta kwanakin mutum; ka riga ka ɗibar masa watanni, ka yi masa iyaka, ba zai iya wuce iyakar ba.
از او رو بگردان تاآرام گیرد. و مثل مزدور روزهای خود را به انجام رساند. ۶ 6
Saboda haka ka kawar da kanka daga gare shi, ka rabu da shi har sai ya cika lokacinsa kamar mutumin da aka ɗauki hayarsa.
«زیرا برای درخت امیدی است که اگر بریده شود باز خواهد رویید، و رمونهایش نابودنخواهد شد. ۷ 7
“Aƙalla itace yana da bege. In an sare shi, zai sāke tsira, zai tohu da kyau.
اگر‌چه ریشه‌اش در زمین کهنه شود، و تنه آن در خاک بمیرد. ۸ 8
Ko da jijiyoyin itacen sun tsufa a cikin ƙasa kuma kututturensa ya mutu a cikin ƙasa.
لیکن از بوی آب، رمونه می‌کند و مثل نهال نو، شاخه‌ها می‌آورد. ۹ 9
Daga ya ji ƙanshin ruwa zai tohu yă yi tsiro kamar shuka.
اما مرد می‌میرد و فاسد می‌شود و آدمی چون جان را سپارد کجا است؟ ۱۰ 10
Amma mutum yana mutuwa a bizne shi; daga ya ja numfashinsa na ƙarshe, shi ke nan.
چنانکه آبها از دریازایل می‌شود، و نهرها ضایع و خشک می‌گردد. ۱۱ 11
Kamar yadda ruwa yake bushewa a teku ko a gaɓar rafi sai wurin yă bushe,
همچنین انسان می‌خوابد و برنمی خیزد، تانیست شدن آسمانها بیدار نخواهند شد و ازخواب خود برانگیخته نخواهند گردید. ۱۲ 12
haka mutum zai kwanta ba zai tashi ba; har sai duniya ta shuɗe mutane ba za su farka ba, ba za su tashi daga barcinsu ba.
کاش که مرا در هاویه پنهان کنی؛ و تا غضبت فرو نشیند، مرا مستور سازی؛ و برایم زمانی تعیین نمایی تا مرا به یاد آوری. (Sheol h7585) ۱۳ 13
“Da ma za ka ɓoye ni a cikin kabari ka ɓoye ni har sai fushinka ya wuce! In da za ka keɓe mini lokaci sa’an nan ka tuna da ni! (Sheol h7585)
اگر مرد بمیرد باردیگر زنده شود؛ در تمامی روزهای مجاهده خودانتظار خواهم کشید، تا وقت تبدیل من برسد. ۱۴ 14
In mutum ya mutu, ko zai sāke rayuwa? In haka ne zan daure kwanakin da nake shan wahala har su wuce.
تو ندا خواهی کرد و من جواب خواهم داد، و به صنعت دست خود مشتاق خواهی شد. ۱۵ 15
Za ka kira zan kuwa amsa maka; za ka yi marmarin abin da hannunka ya halitta.
اما الان قدمهای مرا می‌شماری و آیا برگناه من پاسبانی نمی کنی؟ ۱۶ 16
Ba shakka a lokacin ne za ka lura da matakaina amma ba za ka kula da zunubaina ba.
معصیت من در کیسه مختوم است. و خطای مرا مسدود ساخته‌ای. ۱۷ 17
Za a daure laifofina a cikin jaka; za ka rufe zunubaina.
به درستی کوهی که می‌افتد فانی می‌شود وصخره از مکانش منتقل می‌گردد. ۱۸ 18
“Amma kamar yadda manyan duwatsu suke fāɗuwa su farfashe su kuma gusa daga wurarensu,
آب سنگهارا می‌ساید، و سیلهایش خاک زمین را می‌برد. همچنین امید انسان را تلف می‌کنی، ۱۹ 19
yadda ruwa yakan zaizaye duwatsu ruwa mai ƙarfi kuma yă kwashe turɓayar ƙasa, haka kake barin mutum ba bege.
بر او تا به ابد غلبه می‌کنی، پس می‌رود. روی او را تغییرمی دهی و او را رها می‌کنی. ۲۰ 20
Ka sha ƙarfinsa gaba ɗaya, sai ya ɓace, ka sauya yanayinsa ka kuma kore shi.
پسرانش به عزت می‌رسند و او نمی داند. یا به ذلت می‌افتند و ایشان را به نظر نمی آورد. ۲۱ 21
Ko an martaba’ya’yansa maza, ba zai sani ba; Ko an wulaƙanta su, ba zai gani ba.
برای خودش فقط جسد اواز درد بی‌تاب می‌شود. و برای خودش جان اوماتم می‌گیرد.» ۲۲ 22
Zafin jikinsa kaɗai yake ji yana kuka wa kansa ne kaɗai.”

< ایّوب 14 >