< ارمیا 33 >

و هنگامی که ارمیا در صحن زندان محبوس بود کلام خداوند بار دیگر براو نازل شده، گفت: ۱ 1
Yayinda Irmiya yana a tsare a sansanin matsara, sai maganar Ubangiji ta zo masa sau na biyu cewa,
«خداوند که این کار رامی کند و خداوند که آن را مصور ساخته، مستحکم می‌سازد و اسم او یهوه است چنین می‌گوید: ۲ 2
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, shi da ya halicci duniya, Ubangiji wanda ya siffanta ta ya kuma kafa ta, Ubangiji ne sunansa.
مرا بخوان و تو را اجابت خواهم نمودو تو را از چیزهای عظیم و مخفی که آنها راندانسته‌ای مخبر خواهم ساخت. ۳ 3
‘Kira gare ni zan kuwa amsa maka in kuma faɗa maka manyan abubuwan da ba a iya kaiwa, da ba ka sani ba.’
زیرا که یهوه خدای اسرائیل درباره خانه های این شهر و درباره خانه های پادشاهان یهودا که در مقابل سنگرها ومنجنیقها منهدم شده است، ۴ 4
Gama ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila yana cewa game da gidaje a wannan birni da fadodin Yahuda da aka rurrushe domin a yi amfani da su a kan mahaurai da kuma takobi
و می‌آیند تا باکلدانیان مقاتله نمایند و آنها را به لاشهای کسانی که من در خشم و غضب خود ایشان را کشتم پرمی کنند. زیرا که روی خود را از این شهر به‌سبب تمامی شرارت ایشان مستور ساخته‌ام. ۵ 5
a yaƙi da Babiloniyawa. ‘Za su cika da gawawwakin mutane waɗanda na kashe da fushina da hasalata. Zan ɓoye fuskata wa wannan birni saboda dukan muguntarsu.
اینک به این شهر عافیت و علاج باز خواهم داد و ایشان راشفا خواهم بخشید و فراوانی سلامتی و امانت رابه ایشان خواهم رسانید. ۶ 6
“‘Duk da haka, zan kawo lafiya da warkarwa gare ta; zan warkar da mutanena in kuma wadata su da salama da zama lafiya.
و اسیران یهودا واسیران اسرائیل را باز آورده، ایشان را مثل اول بناخواهم نمود. ۷ 7
Zan komo da Yahuda da Isra’ila daga bauta zan kuma sāke gina su kamar yadda suke a dā.
و ایشان را از تمامی گناهانی که به من ورزیده‌اند، طاهر خواهم ساخت و تمامی تقصیرهای ایشان را که بدانها بر من گناه ورزیده واز من تجاوز کرده‌اند، خواهم آمرزید. ۸ 8
Zan tsarkake su daga dukan zunubin da suka yi mini zan kuma gafarta musu dukan zunubansu na yin mini tawaye.
و این شهر برای من اسم شادمانی و تسبیح و جلال خواهد بود نزد جمیع امت های زمین که چون آنهاهمه احسانی را که به ایشان نموده باشم بشنوندخواهند ترسید. و به‌سبب تمام این احسان وتمامی سلامتی که من به ایشان رسانیده باشم خواهند لرزید. ۹ 9
Sa’an nan birnin nan za tă sa in zama sananne, farin ciki, yabo da girma a gaban dukan al’ummai a duniya da suka ji abubuwa masu kyau da na yi mata; za su kuma yi mamaki su kuma yi rawan jiki saboda yalwar wadata da salamar da na ba ta.’
خداوند چنین می‌گوید که دراین مکان که شما درباره‌اش می‌گویید که آن ویران و خالی از انسان و بهایم است یعنی در شهرهای یهودا و کوچه های اورشلیم که ویران و خالی ازانسان و ساکنان و بهایم است، ۱۰ 10
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Kuna cewa game da wannan wuri, “Kango ne, babu mutane ko dabbobi.” Duk da haka a cikin garuruwan Yahuda da titunan Urushalima da aka yashe, inda ba mutane ko dabbobi, za a sāke jin
در آنها آوازشادمانی و آواز سرور و آواز داماد و آواز عروس و آواز کسانی که می‌گویند یهوه صبایوت راتسبیح بخوانید زیرا خداوند نیکو است و رحمت او تا ابدالاباد است، بار دیگر شنیده خواهد شد وآواز آنانی که هدایای تشکر به خانه خداوندمی آورند. زیرا خداوند می‌گوید اسیران این زمین را مثل سابق باز خواهم آورد. ۱۱ 11
sowa ta farin ciki da murna, muryoyin amarya da na ango, da muryoyin waɗanda suka kawo hadayun salama a gidan Ubangiji suna cewa, “‘“Ku yi godiya ga Ubangiji Maɗaukaki, gama Ubangiji mai alheri ne; ƙaunarsa za tă dawwama har abada.” Gama zan mayar da wadatar ƙasar kamar yadda suke a dā,’ in ji Ubangiji.
یهوه صبایوت چنین می‌گوید: در اینجایی که ویران و از انسان وبهایم خالی است و در همه شهرهایش بار دیگرمسکن شبانانی که گله‌ها را می‌خوابانند خواهدبود. ۱۲ 12
“Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, ‘A wannan wuri, kango da babu mutane ko dabbobi, cikin dukan garuruwansa za a sāke kasance da wurin kiwo don makiyaya su hutar da garkunansu.
و خداوند می‌گوید که در شهرهای کوهستان و شهرهای همواری و شهرهای جنوب و در زمین بنیامین و در حوالی اورشلیم وشهرهای یهودا گوسفندان بار دیگر از زیردست شمارندگان خواهند گذشت. ۱۳ 13
A cikin garuruwan ƙasar tudu, garuruwan yammancin gindin dutse da na Negeb, a yankin Benyamin, a cikin ƙauyuka kewayen Urushalima da kuma a cikin garuruwan Yahuda, garkuna za su sāke bi a ƙarƙashin hannun mai ƙidayawa,’ in ji Ubangiji.
اینک خداوندمی گوید: ایامی می‌آید که آن وعده نیکو را که درباره خاندان اسرائیل و خاندان یهودا دادم وفاخواهم نمود. ۱۴ 14
“‘Kwanaki suna zuwa,’ in ji Ubangiji, ‘sa’ad da zan cika alkawarin alheri da na yi wa gidan Isra’ila da kuma gidan Yahuda.
در آن ایام و در آن زمان شاخه عدالت برای داود خواهم رویانید و او انصاف وعدالت را در زمین جاری خواهد ساخت. ۱۵ 15
“‘A waɗannan kwanaki da kuma a wannan lokaci zan tā da Reshe mai adalci daga zuriyar Dawuda; zai yi abin da yake daidai da kuma gaskiya a ƙasar.
درآن ایام یهودا نجات خواهد یافت و اورشلیم به امنیت مسکون خواهد شد و اسمی که به آن نامیده می‌شود این است: یهوه صدقینو. ۱۶ 16
A kwanakin nan zan ceci Yahuda Urushalima kuma za tă zauna lafiya. Sunan da za a kira ta shi ne, Ubangiji Adalcinmu.’
زیرا خداوند چنین می‌گوید که از داود کسی‌که برکرسی خاندان اسرائیل بنشیند کم نخواهد شد. ۱۷ 17
Gama ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Dawuda ba zai taɓa rasa mutumin da zai zauna a gadon sarautar Isra’ila ba,
و از لاویان کهنه کسی‌که قربانی های سوختنی بگذراند و هدایای آردی بسوزاند وذبایح همیشه ذبح نماید از حضور من کم نخواهدشد.» ۱۸ 18
ba kuwa firistoci waɗanda suke Lawiyawa za su rasa mutumin da zai ci gaba da tsaya a gabana don miƙa hadayun ƙonawa, ya ƙona hadayun hatsi ya kuma miƙa sadakoki ba.’”
و کلام خداوند بر ارمیا نازل شده، گفت: ۱۹ 19
Sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
«خداوند چنین می‌گوید: اگر عهد مرا با روز وعهد مرا با شب باطل توانید کرد که روز و شب دروقت خود نشود، ۲۰ 20
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘In ka tā da alkawarina na rana da kuma alkawarina na dare, har dare da rana ba za su ƙara bayyana a ƙayyadaddun lokutansu ba,
آنگاه عهد من با بنده من داودباطل خواهد شد تا برایش پسری که بر کرسی اوسلطنت نماید نباشد و با لاویان کهنه که خادم من می‌باشند. ۲۱ 21
to, sai a tā da alkawarina da Dawuda bawana da alkawarina da Lawiyawan da suke firistoci masu hidima a gabana, Dawuda kuma ba zai ƙara kasance da zuriyar da za tă yi mulki.
چنانکه لشکر آسمان را نتوان شمردو ریگ دریا را قیاس نتوان کرد، همچنان ذریت بنده خود داود و لاویان را که مرا خدمت می‌نمایند زیاده خواهم گردانید.» ۲۲ 22
Zan sa zuriyar Dawuda bawana da kuma Lawiyawan da suke hidima a gabana su yi yawa kamar taurarin sararin sama da kuma yashin bakin tekun da ba a iya ƙidaya.’”
و کلام خداوند بر ارمیا نازل شده، گفت: ۲۳ 23
Sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
«آیا نمی بینی که این قوم چه حرف می‌زنند؟ می‌گویند که خداوند آن دو خاندان را که برگزیده بود ترک نموده است. پس قوم مرا خوارمی شمارند که در نظر ایشان دیگر قومی نباشند. ۲۴ 24
“Ba ka lura ba cewa waɗannan mutane suna cewa, ‘Ubangiji ya ƙi masarautai biyu da ya zaɓa’? Saboda haka suka rena mutanena ba sa ƙara ɗaukansu a matsayin al’umma.
خداوند چنین می‌گوید: اگر عهد من با روز وشب نمی بود و قانون های آسمان و زمین را قرارنمی دادم، ۲۵ 25
Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘In ban kafa alkawarina game da rana da kuma game da dare ba in kuma gyara dokokin sama da duniya ba,
آنگاه نیز ذریت یعقوب ونسل بنده خود داود را ترک می‌نمودم و از ذریت او بر اولادابراهیم و اسحاق و یعقوب حاکمان نمی گرفتم. زیرا که اسیران ایشان را باز خواهم آورد و برایشان ترحم خواهم نمود.» ۲۶ 26
to zan ƙi zuriyar Yaƙub da na Dawuda bawana ba zan kuma zaɓi ɗaya daga cikin’ya’yansa maza ya yi mulki a kan zuriyar Ibrahim, Ishaku da Yaƙub ba. Gama zan mayar da wadatarsu in kuma yi musu jinƙai.’”

< ارمیا 33 >