< پیدایش 25 >

و ابراهیم، دیگر بار، زنی گرفت که قطوره نام داشت. ۱ 1
Ibrahim ya auro wata mace, mai suna Ketura.
و او زمران و یقشان و مدان و مدیان و یشباق و شوحا را برای او زایید. ۲ 2
Ta haifa masa Zimran, Yokshan, Medan, Midiyan, Ishbak da Shuwa.
و یقشان، شبا و ددان را آورد. و بنی ددان، اشوریم و لطوشیم و لامیم بودند. ۳ 3
Yokshan shi ne mahaifin Sheba da Dedan. Zuriyar Dedan su ne mutanen Ashur, da mutanen Letush, da kuma mutanen Lewummin.
و پسران مدیان، عیفا و عیفر و حنوک و ابیداع و الداعه بودند. جمله اینها، اولاد قطوره بودند. ۴ 4
’Ya’yan Midiyan maza su ne, Efa, Efer, Hanok, Abida, da kuma Elda’a. Dukan waɗannan zuriyar Ketura ce.
و ابراهیم تمام مایملک خود را به اسحاق بخشید. ۵ 5
Ibrahim ya bar wa Ishaku kome da ya mallaka.
اما به پسران کنیزانی که ابراهیم داشت، ابراهیم عطایاداد، و ایشان را در حین حیات خود، از نزد پسرخویش اسحاق، به‌جانب مشرق، به زمین شرقی فرستاد. ۶ 6
Amma yayinda Ibrahim yake da rai, ya ba wa’ya’yan ƙwarƙwaransa maza kyautai, ya kuma sallame su daga ɗansa Ishaku zuwa ƙasashen gabas.
این است ایام سالهای عمر ابراهیم، که زندگانی نمود: صد و هفتاد وپنج سال. ۷ 7
Duka-duka, Ibrahim ya yi shekara ɗari da saba’in da biyar.
و ابراهیم جان بداد، و در کمال شیخوخیت، پیر و سیر شده، بمرد. و به قوم خود ملحق شد. ۸ 8
Sa’an nan Ibrahim ya ja numfashinsa na ƙarshe, ya kuma mutu da kyakkyawar tsufa, tsoho da kuma shekaru masu yawa; aka kuma tara shi ga mutanensa.
و پسرانش، اسحاق و اسماعیل، او را در مغاره مکفیله، درصحرای عفرون بن صوحارحتی، در مقابل ممری دفن کردند. ۹ 9
’Ya’yansa maza kuwa Ishaku da Ishmayel suka binne shi cikin kogon Makfela, kusa da Mamre, a cikin filin Efron ɗan Zohar mutumin Hitti,
آن صحرایی که ابراهیم، ازبنی حت، خریده بود. در آنجا ابراهیم و زوجه‌اش ساره مدفون شدند. ۱۰ 10
filin da Ibrahim ya saya daga Hittiyawa. A nan aka binne Ibrahim tare da matarsa Saratu.
و واقع شد بعد از وفات ابراهیم، که خدا پسرش اسحاق را برکت داد، واسحاق نزد بئرلحی رئی ساکن بود. ۱۱ 11
Bayan rasuwar Ibrahim, Allah ya albarkaci ɗansa Ishaku wanda a lokacin yana zama kusa da Beyer-Lahai-Royi.
این است پیدایش اسماعیل بن ابراهیم، که هاجر مصری، کنیز ساره، برای ابراهیم زایید. ۱۲ 12
Waɗannan su ne zuriyar Ishmayel ɗan Ibrahim, wanda Hagar mutuniyar Masar, baranyar Saratu, ta haifa wa Ibrahim.
واین است نامهای پسران اسماعیل، موافق اسمهای ایشان به حسب پیدایش ایشان. نخست زاده اسماعیل، نبایوت، و قیدار و ادبیل ومبسام. ۱۳ 13
Ga jerin sunayen’ya’yan Ishmayel maza bisa ga haihuwarsu, Nebayiwot ɗan farin Ishmayel, Kedar, Adbeyel, Mibsam,
و مشماع و دومه و مسا ۱۴ 14
Mishma, Duma, Massa,
و حدار وتیما و یطور و نافیش و قدمه. ۱۵ 15
Hadad, Tema, Yetur, Nafish da Kedema.
اینانند پسران اسماعیل، و این است نامهای ایشان در بلدان وحله های ایشان، دوازده امیر، حسب قبایل ایشان. ۱۶ 16
Waɗannan su ne’ya’yan Ishmayel maza, waɗanda kuma suke sunayen kabilu goma sha biyu masu mulki bisa ga wuraren zamansu da sansaninsu.
و مدت زندگانی اسماعیل، صد و سی و هفت سال بود، که جان را سپرده، بمرد. و به قوم خودملحق گشت. ۱۷ 17
Duka-duka Ishmayel ya yi shekara ɗari da talatin da bakwai; sai ya ja numfashinsa na ƙarshe, ya kuma mutu, aka kuma tara shi ga mutanensa.
و ایشان از حویله تا شور، که مقابل مصر، به سمت آشور واقع است، ساکن بودند. و نصیب او در مقابل همه برادران او افتاد. ۱۸ 18
Zuriyarsa sun zauna tsakanin Hawila ne da Shur, wanda yake kusa da gabashin iyakar Masar wajen Asshur. Sun yi zaman rikici da dukan sauran’yan’uwansu.
و این است پیدایش اسحاق بن ابراهیم. ابراهیم، اسحاق را آورد. ۱۹ 19
Waɗannan su ne zuriyar Ishaku ɗan Ibrahim. Ibrahim ya haifi Ishaku,
و چون اسحاق چهل ساله شد، رفقه دختر بتوئیل ارامی و خواهر لابان ارامی را، از فدان ارام به زنی گرفت. ۲۰ 20
Ishaku yana da shekara arba’in sa’ad da ya auri Rebeka’yar Betuwel, mutumin Aram, daga Faddan Aram,’yar’uwar Laban mutumin Aram.
و اسحاق برای زوجه خود، چون که نازاد بود، نزد خداونددعا کرد. و خداوند او را مستجاب فرمود. وزوجه‌اش رفقه حامله شد. ۲۱ 21
Ishaku ya yi addu’a ga Ubangiji a madadin matarsa, saboda ba ta haihuwa. Ubangiji ya amsa addu’arsa, matarsa Rebeka kuwa ta yi ciki.
و دو طفل در رحم او منازعت می‌کردند. او گفت: «اگر چنین باشد، من چرا چنین هستم؟» پس رفت تا از خداوندبپرسد. ۲۲ 22
Jariran suka kama kokawa da juna a cikinta, sai ta ce, “Me ya sa wannan yake faruwa da ni?” Saboda haka ta tafi don ta nemi nufin Ubangiji.
خداوند به وی گفت: «دو امت در بطن تو هستند، و دو قوم از رحم تو جدا شوند. وقومی بر قومی تسلط خواهد یافت، و بزرگ، کوچک را بندگی خواهد نمود.» ۲۳ 23
Ubangiji ya ce mata, “Al’ummai biyu suna a cikin mahaifarki mutum biyu da za ki haifa, za su rabu da juna, ɗayan zai fi ɗayan ƙarfi, babban kuma zai bauta wa ƙaramin.”
و چون وقت وضع حملش رسید، اینک توامان در رحم اوبودند. ۲۴ 24
Da lokaci ya yi da za tă haihu, sai ga’yan biyu maza a mahaifarta.
و نخستین، سرخ‌فام بیرون آمد، وتمامی بدنش مانند پوستین، پشمین بود. و او راعیسو نام نهادند. ۲۵ 25
Wanda ya fara fita ja ne, dukan jikinsa kuwa kamar riga mai gashi. Don haka aka sa masa suna Isuwa.
و بعد از آن، برادرش بیرون آمد، و پاشنه عیسو را به‌دست خود گرفته بود. واو را یعقوب نام نهادند. و درحین ولادت ایشان، اسحاق، شصت ساله بود. ۲۶ 26
Bayan wannan, ɗan’uwansa ya fito, da hannunsa yana riƙe da ɗiɗɗigen Isuwa; don haka aka sa masa suna Yaƙub. Ishaku yana da shekara sittin, lokacin da Rebeka ta haife su.
و آن دو پسر، نموکردند، و عیسو صیادی ماهر، و مرد صحرایی بود. و اما یعقوب، مرد ساده دل و چادرنشین. ۲۷ 27
Yaran suka yi girma, Isuwa kuwa ya zama riƙaƙƙen maharbi, mutumin jeji, yayinda Yaƙub, shiru-shiru ne mai son zama a tentuna.
واسحاق، عیسو را دوست داشتی، زیرا که صید اورا می‌خورد. اما رفقه، یعقوب را محبت نمودی. ۲۸ 28
Ishaku, mai son ci naman jeji, ya ƙaunaci Isuwa, amma Rebeka ta ƙaunaci Yaƙub.
روزی یعقوب، آش می‌پخت و عیسو وا مانده، از صحرا آمد. ۲۹ 29
Wata rana sa’ad da Yaƙub yana dafa fate. Isuwa ya shigo daga jeji, da yunwa sosai.
و عیسو به یعقوب گفت: «از این آش ادوم (یعنی سرخ ) مرا بخوران، زیرا که وامانده‌ام.» از این سبب او را ادوم نامیدند. ۳۰ 30
Ya ce wa Yaƙub, “Ina roƙonka, ka ɗan ɗiba mini faten nan! Ina fama da yunwa!” (Shi ya sa aka kira shi Edom.)
یعقوب گفت: «امروز نخست زادگی خود را به من بفروش.» ۳۱ 31
Yaƙub ya amsa ya ce, “Ka fara sayar mini da matsayinka na ɗan fari tukuna.”
عیسو گفت: «اینک من به حالت موت رسیده‌ام، پس مرا از نخست زادگی چه فایده؟» ۳۲ 32
Isuwa ya ce, “Duba, ina gab da mutuwa, me matsayina na ɗan fari zai yi mini?”
یعقوب گفت: «امروز برای من قسم بخور.» پس برای او قسم خورد، و نخست زادگی خود را به یعقوب فروخت. ۳۳ 33
Amma Yaƙub ya ce, “Ka rantse mini tukuna.” Don haka ya rantse masa, ya sayar da matsayinsa na ɗan fari ga Yaƙub.
و یعقوب نان وآش عدس را به عیسو داد، که خورد و نوشید وبرخاسته، برفت. پس عیسو نخست زادگی خود راخوار نمود. ۳۴ 34
Sa’an nan Yaƙub ya ba wa Isuwa burodi da ɗan miyan lansir. Ya ci, ya sha, sa’an nan ya tashi ya tafi. Ta haka Isuwa ya yi banza da matsayinsa na ɗan fari.

< پیدایش 25 >