< حزقیال 7 >

و کلام خداوند بر من نازل شده، گفت: ۱ 1
Maganar Ubangiji ta zo gare ni cewa,
«وتو‌ای پسر انسان (بگو): خداوند یهوه به زمین اسرائیل چنین می‌گوید: انتهایی بر چهارگوشه زمین انتها رسیده است. ۲ 2
“Ɗan mutum, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yake cewa wa ƙasar Isra’ila, “‘Ƙarshe ya zo! Ƙarshe ya zo a kan kusurwoyi huɗu na ƙasar.
الان انتها بر تورسیده است و من خشم خود را بر تو واردآورده‌ام و بر وفق راههایت ترا داوری نموده، تمامی رجاساتت را بر تو خواهم نهاد. ۳ 3
Ƙarshe yanzu yana a kanki. Zan fashe fushina a kanki. Zan shari’anta ki bisa ga halinki in sāka miki kuma saboda dukan ayyukan banƙyamar da kika yi.
و چشم من برتو شفقت نخواهد کرد و رحمت نخواهم فرمود بلکه راههای تو را بر تو خواهم نهاد ورجاسات تو در میانت خواهد بود. پس خواهی دانست که من یهوه هستم.» ۴ 4
Ba zan dube ki da tausayi; ko in ƙyale ki ba. Tabbatacce zan sāka miki saboda halinki da kuma ayyukanki masu banƙyama a cikinki. Sa’an nan za ki san cewa ni ne Ubangiji.’
خداوند یهوه چنین می‌گوید: «بلا هان بلای واحد می‌آید! ۵ 5
“Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Masifa! Masifar da ba a taɓa gani ba tana zuwa.
انتهایی می‌آید، انتهایی می‌آید وبه ضد تو بیدار شده است. هان می‌آید. ۶ 6
Ƙarshe ya zo! Ƙarshe ya zo! Ya farka a kanki. Ga shi, ya zo!
‌ای ساکن زمین اجل تو بر تو می‌آید. وقت معین می‌آید و آن روز نزدیک است. روز هنگامه خواهد شد و نه روز آواز شادمانی بر کوهها. ۷ 7
Ƙaddara ta auko miki, ya ke wadda ke zama cikin ƙasar. Lokaci ya yi, rana ta gabato; akwai fargaba, ba farin ciki ba, a kan duwatsu.
الان عنقریب غضب خود را بر تو خواهم ریخت و خشم خویش را بر تو به اتمام رسانیده، تو را موافق راههایت داوری خواهم نمود و جمیع رجاساتت را بر تو خواهم نهاد. ۸ 8
Ina gab da fasa hasalata a kanki in kuma aukar da fushina a kanki; zan shari’anta ke bisa ga halinki in kuma sāka miki saboda dukan ayyukanki masu banƙyama.
و چشم من شفقت نخواهدکرد و رحمت نخواهم فرمود، بلکه مکافات راههایت را به تو خواهم رسانید و رجاسات تو درمیانت خواهد بود و خواهید دانست که زننده تو من یهوه هستم. ۹ 9
Ba zan dube ki da tausayi ko in ƙyale ke ba; zan sāka miki bisa ga halinki da kuma ayyukan masu banƙyama a cikinki. Sa’an nan za ki san cewa ni ne Ubangiji wanda yake bugunki.
اینک آنروز هان می‌آید! اجل تو بیرون آمده و عصا شکوفه آورده و تکبر، گل کرده است. ۱۰ 10
“‘Ga shi ranar ta zo! Ta iso! Ƙaddararki ta keto, sandar ta yi toho, girman kai ya yi fure!
ظلم عصای شرارت گشته است. ازایشان و از جمعیت ایشان و از ازدحام ایشان چیزی باقی نیست و در میان ایشان حشمتی نمانده است. ۱۱ 11
Rikici ya yi girma ya zama sandar da za a hukunta mugunta; babu wani daga cikin mutanen da za a bari, babu wani dukiyarsu da za a bari, babu wani abin amfani.
وقت می‌آید و آنروز نزدیک است. پس مشتری شادی نکند و فروشنده ماتم نگیرد، زیرا که خشم بر تمامی جمعیت ایشان قرار گرفته است. ۱۲ 12
Lokaci ya yi! Ranar ta gabato! Kada mai saya ya yi farin ciki ko kuwa mai sayarwa ya yi baƙin ciki, gama hasala tana a kan dukan jama’a.
زیرا که فروشندگان اگر‌چه در میان زندگان زنده مانند، به آنچه فروخته باشندنخواهند برگشت، چونکه غضب بر تمامی جمعیت ایشان قرار گرفته است. ایشان نخواهندبرگشت و هیچکس به گناه خویش زندگی خود راتقویت نخواهد داد. ۱۳ 13
Mai sayarwa ba zai mayar da ƙasar da ya sayar tuntuni ba muddin dukansu suna da rai, gama ba za a sauya wahayin da ya shafi dukan jama’a ba. Saboda zunubansu, babu ɗayansu da zai adana ransa.
کرنا را نواخته و همه‌چیزرا مهیا ساخته‌اند، اما کسی به جنگ نمی رود. زیراکه غضب من بر تمامی جمعیت ایشان قرار گرفته است. ۱۴ 14
“‘Ko da yake suna busa ƙaho suna kuma shirya kome, ba wanda zai tafi yaƙi, gama hasalata tana a kan dukan jama’a.
شمشیر در بیرون است و وبا و قحط دراندرون. آنکه در صحرا است به شمشیر می‌میرد وآنکه در شهر است قحط و وبا او را هلاک می‌سازد. ۱۵ 15
A waje takobi ne, a ciki annoba ne da yunwa; waɗanda suke fili za su mutu ta wurin takobi, waɗanda kuma suke cikin birni yunwa da annoba za su cinye su.
و رستگاران ایشان فرار می‌کنند ومثل فاخته های دره‌ها بر کوهها می‌باشند. و هرکدام از ایشان به‌سبب گناه خود ناله می‌کنند. ۱۶ 16
Duk waɗanda suka tsira suka tsere za su kasance a cikin duwatsu, suna kuka kamar kurciyoyin kwaruruka, kowanne saboda zunubansa.
همه دستها سست شده و جمیع زانوها مثل آب بیتاب گردیده است. ۱۷ 17
Kowane hannu zai raunana, kowace gwiwa kuma za tă zama marar ƙarfi kamar ruwa.
و پلاس در برمی کنند و وحشت ایشان را می‌پوشاند و بر همه چهره‌ها خجلت و بر جمیع سرها گری می‌باشد. ۱۸ 18
Za su sa tufafin makoki su kuma rufu da fargaba. Fuskokinsu kuma za su rufu da kunya a kuma aske kawunansu.
نقره خود را در کوچه‌ها می‌ریزند و طلای ایشان مثل چیز نجس می‌باشد. نقره و طلای ایشان در روز غضب خداوند ایشان را نتواندرهانید. جانهای خود را سیر نمی کنند و بطنهای خویش را پر نمی سازند زیرا گناه ایشان سنگ مصادم آنها شده است. ۱۹ 19
“‘Za su zubar da azurfarsu a tituna, zinariyarsu kuma za tă zama ƙazantacciyar aba. Azurfarsu da zinariyarsu ba za su iya cetonsu a ranar hasalar Ubangiji ba. Ba za su ƙosar da yunwansu ko su cika cikinsu da shi ba, gama su ne sanadin tuntuɓensu cikin zunubi.
«و او زیبایی زینت خود را در کبریایی قرارداده بود، اما ایشان بتهای مکروهات و رجاسات خویش را در آن ساختند. بنابراین آن را برای ایشان مثل چیز نجس خواهم گردانید. ۲۰ 20
Sun yi fariya kyan kayan adonsu suka kuma yi amfani da su don su yi gumakansu masu banƙyama, da ƙazantattun abubuwa.
و آن رابه‌دست غریبان به تاراج و به شریران جهان به غارت خواهم داد و آن را بی‌عصمت خواهندساخت. ۲۱ 21
Zan ba da su duka kamar ganima ga baƙi da kuma kamar abin da aka washe ga mugayen duniya, za su kuma ƙazantar da su.
و روی خود را از ایشان خواهم برگردانید و مکان مستور مرا بی‌عصمت خواهندنمود و ظالمان داخل آن شده، آن را بی‌عصمت خواهند ساخت. ۲۲ 22
Zan juye fuskata daga gare su, za su kuwa ƙazantar da wurina mai daraja;’yan fashi za su shiga su kuma ƙazantar da shi.
زنجیر را بساز، زیرا که زمین از جرمهای خونریزی پر است و شهر از ظلم مملو. ۲۳ 23
“‘Ka shirya sarƙoƙi, domin ƙasar ta cika da alhakin jini, birnin kuma ya cika da rikici.
و اشرار امت‌ها را خواهم آورد و درخانه های ایشان تصرف خواهند نمود و تکبرزورآوران را زایل خواهم ساخت و آنهامکان های مقدس ایشان را بی‌عصمت خواهندنمود. ۲۴ 24
Zan kawo al’ummai mafi mugunta su mallaki gidajenku; zan kawo ƙarshen fariyar masu ƙarfi, Wurare Masu Tsarkinsu za su ƙazantu.
هلاکت می‌آید و سلامتی را خواهندطلبید، اما یافت نخواهد شد. ۲۵ 25
Sa’ad da wahala ta zo, za su nemi salama, amma ba za su same ta ba.
مصیبت برمصیبت می‌آید و آوازه بر آوازه مسموع می‌شود. رویا از نبی می‌طلبند، اما شریعت از کاهنان ومشورت از مشایخ نابود شده است. ۲۶ 26
Masifa a kan masifa za su zo, jita-jita kuma a kan jita-jita. Za su yi ƙoƙarin samun wahayi daga annabi; koyarwar doka ta wurin firist za tă ɓace, kamar yadda shawarar dattawa za tă ɓace.
پادشاه ماتم می‌گیرد و رئیس به حیرت ملبس می‌شود ودستهای اهل زمین می‌لرزد. و موافق راههای ایشان با ایشان عمل خواهم نمود و بر وفق استحقاق ایشان ایشان را داوری خواهم نمود. پس خواهند دانست که من یهوه هستم؟ ۲۷ 27
Sarki zai yi makoki, yerima zai fid da zuciya, hannuwan mutanen ƙasar kuma za su yi rawa. Zan sāka musu bisa ga ayyukansu, zan kuma hukunta su bisa ga ma’auninsu. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.’”

< حزقیال 7 >