< حزقیال 35 >

و کلام خداوند بر من نازل شده، گفت: ۱ 1
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
«ای پسر انسان نظر خود را بر کوه سعیر بدار و به ضد آن نبوت نما! ۲ 2
“Ɗan mutum, ka fuskanci Dutsen Seyir; ka yi annabci a kansa
و آن را بگوخداوند یهوه چنین می‌فرماید: اینک‌ای کوه سعیر من به ضد تو هستم. و دست خود را بر تودراز کرده، تو را ویران و محل دهشت خواهم ساخت. ۳ 3
ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da kai, Dutsen Seyir, zan kuma miƙa hannuna gāba da kai in mai da kai kango.
شهرهایت را خراب خواهم نمود تاویران شده، بدانی که من یهوه هستم. ۴ 4
Zan mai da garuruwanka kufai za ka kuma zama kango. Sa’an nan za ka san cewa ni ne Ubangiji.
چونکه عداوت دائمی داشتی و بنی‌اسرائیل را در زمان مصیبت ایشان و هنگام عقوبت آخر به دم شمشیرتسلیم نمودی، ۵ 5
“‘Domin ka riƙe ƙiyayya ta tun dā, ka kuma ba da mutanen Isra’ila domin a kashe su da takobi a lokacin masifarsu, lokacin da adadin horonsu ya cika,
لهذا خداوند یهوه چنین می گوید: به حیات خودم قسم که تو را به خون تسلیم خواهم نمود که خون تو را تعاقب نماید. چون از خون نفرت نداشتی، خون تو را تعاقب خواهد نمود. ۶ 6
saboda haka muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, zan sa a zub da jininka zan kuwa fafare ka. Da yake ba ka ƙi zub da jini ba, zub da jini zai fafare ka.
و کوه سعیر را محل دهشت وویران ساخته، روندگان و آیندگان را از آن منقطع خواهم ساخت. ۷ 7
Zan mai da Dutsen Seyir kango in kuma yanke dukan waɗanda suke shiga da fita a cikinka.
و کوههایش را از کشتگانش مملو می‌کنم که مقتولان شمشیر بر تلها و دره‌ها وهمه وادیهای تو بیفتند. ۸ 8
Zan cika duwatsunka da matattu; waɗanda aka kashe da takobi za su fāɗi a kan tuddanka, da cikin kwarurukanka, da cikin dukan kwazazzabanka.
و تو را خرابه های دائمی می‌سازم که شهرهایت دیگر مسکون نشودو بدانید که من یهوه هستم. ۹ 9
Zan mai da kai kango har abada; ba za a zauna a cikin garuruwanka ba. Sa’an nan za ka san cewa ni ne Ubangiji.
چونکه گفتی این دوامت و این دو زمین از آن من می‌شود و آن را به تصرف خواهیم آورد با آنکه یهوه در آنجا است.» ۱۰ 10
“‘Domin kun ce, “Waɗannan al’ummai biyu da ƙasashe za su zama namu za mu kuma mallake su,” ko da yake Ni Ubangiji ina a can,
بنابراین خداوند یهوه چنین می‌گوید: «به حیات خودم قسم که موافق خشم و حسدی که به ایشان نمودی، از کینه‌ای که با ایشان داشتی با توعمل خواهم نمود. و چون بر تو داوری کرده باشم، خویشتن را بر تو در میان ایشان معروف خواهم گردانید. ۱۱ 11
saboda haka muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, zan sāka maka gwargwadon fushi da kuma kishin da ka nuna a ƙiyayyarsu da ka yi zan kuma sanar da kaina a cikinsu sa’ad da na hukunta ka.
و خواهی دانست که من یهوه تمامی سخنان کفرآمیز را که به ضد کوههای اسرائیل گفته‌ای، شنیده‌ام. چونکه گفتی: خراب گردید و برای خوراک ما داده شد. ۱۲ 12
Sa’an nan za ka san cewa Ni Ubangiji na ji duk abubuwan banzan da ka faɗa a kan duwatsun Isra’ila. Ka ce, “An mai da su kango an kuma ba mu su mu cinye.”
و شما به دهان خود به ضد من تکبر نموده، سخنان خویش را بر من افزودید و من آنها را شنیدم. ۱۳ 13
Ka yi fariya a kaina, ka kuma yi magana a kaina ba gaggautawa, na ji shi sarai.
خداوندیهوه چنین می‌گوید: حینی که تمامی جهان شادی کنند من تو را ویران خواهم ساخت. ۱۴ 14
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa yayinda dukan duniya take farin ciki, zan mai da kai kango.
وچنانکه بر میراث خاندان اسرائیل حینی که ویران شد شادی نمودی، همچنان با تو عمل خواهم نمود. و تو‌ای کوه سعیر و تمام ادوم جمیع ویران خواهید شد. پس خواهند دانست که من یهوه هستم.» ۱۵ 15
Domin ka yi farin ciki sa’ad da gādon gidan Isra’ila ya zama kufai, haka zan yi da kai, ya Dutsen Seyir, kai da dukan Edom. Sa’an nan za ka san cewa ni ne Ubangiji.’”

< حزقیال 35 >