< خروج 4 >

تصدیق نخواهند کرد، و سخن مرانخواهند شنید، بلکه خواهند گفت یهوه بر توظاهر نشده است.» ۱ 1
Musa ya amsa ya ce, “In ba su gaskata ni ba, suka kuma ce, ‘Ubangiji bai bayyana gare ka ba fa’?”
پس خداوند به وی گفت: «آن چیست در دست تو؟» گفت: «عصا.» ۲ 2
Sai Ubangiji ya ce, “Mene ne wannan a hannunka?” Musa ya amsa ya ce, “Sanda.”
گفت: «آن را بر زمین بینداز.» و چون آن را به زمین انداخت، ماری گردید و موسی از نزدش گریخت. ۳ 3
Sai Ubangiji ya ce, “Jefa shi ƙasa.” Musa ya jefa shi ƙasa, sai sandan ya zama maciji, Musa kuwa ya gudu daga gare shi.
پس خداوند به موسی گفت: «دست خود رادراز کن و دمش را بگیر.» پس دست خود را درازکرده، آن را بگرفت، که در دستش عصا شد. ۴ 4
Sai Ubangiji ya ce masa, “Sa hannunka ka ɗauke shi ta wutsiya.” Sai Musa ya miƙa hannu, ya kama macijin, macijin kuwa ya dawo sanda a hannunsa.
«تاآنکه باور کنند که یهوه خدای پدران ایشان، خدای ابراهیم، خدای اسحاق، و خدای یعقوب، به تو ظاهر شد.» ۵ 5
Ubangiji ya ce, “Wannan zai sa su ba da gaskiya cewa Ubangiji, Allah na kakanninsu, Allah na Ibrahim, Allah na Ishaku, da kuma Allah da Yaƙub, ya bayyana gare ka.”
و خداوند دیگرباره وی راگفت: «دست خود را در گریبان خود بگذار.» چون دست به گریبان خود برد، و آن را بیرون آورد، اینک دست او مثل برف مبروص شد. ۶ 6
Sa’an nan Ubangiji ya ce, “Sa hannunka cikin rigarka.” Sai Musa ya sa hannunsa cikin rigarsa, sa’ad da ya fitar da shi, sai hannun ya a kuturce fari fat, kamar ƙanƙara.
پس گفت: «دست خود را باز به گریبان خود بگذار.» چون دست به گریبان خود باز برد، و آن را بیرون آورد، اینک مثل سایر بدنش باز آمده بود. ۷ 7
Sai Ubangiji ya ce, “Yanzu, mayar da hannunka a rigarka.” Sai Musa ya sa hannunsa cikin rigarsa, da ya fitar da shi, sai hannun ya koma kamar sauran jikinsa.
«وواقع خواهد شد که اگر تو را تصدیق نکنند، وآواز آیت نخستین را نشنوند، همانا آواز آیت دوم را باور خواهند کرد. ۸ 8
Sa’an nan Ubangiji ya ce, “In ba su gaskata ba, ko kuma ba su kula da mu’ujiza ta fari ba, wataƙila su gaskata da ta biyun.
و هر گاه این دو آیت راباور نکردند و سخن تو را نشنیدند، آنگاه از آب نهر گرفته، به خشکی بریز، و آبی که از نهر گرفتی بر روی خشکی به خون مبدل خواهد شد.» ۹ 9
Amma in ba su gaskata mu’ujizan nan biyu ba, ko kuwa ba su saurare ka ba, sai ka ɗibo ruwa daga Nilu, ka zuba a busasshiyar ƙasa. Ruwan da ka ɗebo daga kogin zai zama jini a ƙasar.”
پس موسی به خداوند گفت: «ای خداوند، من مردی فصیح نیستم، نه در سابق و نه از وقتی که به بنده خود سخن گفتی، بلکه بطی الکلام و کندزبان.» ۱۰ 10
Musa ya ce wa Ubangiji, “Ya Ubangiji, ni ban mai iya magana ba ne, ban taɓa iya ba, ko a yanzu ma, bayan ka yi magana da ni, gama ni mai nauyin baki ne, mai nauyin harshe kuma.”
خداوند گفت: «کیست که زبان به انسان داد، و گنگ و کر و بینا و نابینا را که آفرید؟ آیا نه من که یهوه هستم؟ ۱۱ 11
Ubangiji ya ce masa, “Wa ya ba mutum bakinsa? Wa yake maishe shi kurma ko bebe? Wa yake ba shi gani ko yă makanta shi? Ashe ba Ni Ubangiji ba ne?
پس الان برو و من با زبانت خواهم بود، و هر‌چه باید بگویی تو را خواهم آموخت.» ۱۲ 12
Yanzu tafi, zan taimake ka ka yi magana, zan kuma koya maka abin da za ka faɗa.”
گفت: «استدعا دارم‌ای خداوند که بفرستی به‌دست هر‌که می‌فرستی.» ۱۳ 13
Amma Musa ya ce, “Ya Ubangiji, ina roƙonka, ka nemi wani ka aika.”
آنگاه خشم خداوند بر موسی مشتعل شدو گفت: «آیا برادرت، هارون لاوی را نمی دانم که او فصیح الکلام است؟ و اینک او نیز به استقبال توبیرون می‌آید، و چون تو را ببیند، در دل خود شادخواهد گردید. ۱۴ 14
Sai Ubangiji ya yi fushi da Musa ya ce, “Ɗan’uwanka Haruna Balawe, ba ya nan ne? Na san ya iya magana. Ya riga ya kama hanya don yă sadu da kai, zai kuma yi farin ciki sa’ad da ya gan ka.
و بدو سخن خواهی گفت وکلام را به زبان وی القا خواهی کرد، و من با زبان توو با زبان او خواهم بود، و آنچه باید بکنید شما راخواهم آموخت. ۱۵ 15
Za ka yi masa magana. Ka kuma sa masa maganata a baki; zan kuma taimake ku magana, in koya muku abin da za ku yi.
و او برای تو به قوم سخن خواهد گفت، و او مر تو را به‌جای زبان خواهدبود، و تو او را به‌جای خدا خواهی بود. ۱۶ 16
Zai yi magana da mutane a madadinka, zai zama kamar bakinka, kai kuwa kamar Allah a gare shi.
و این عصا را به‌دست خود بگیر که به آن آیات را ظاهر سازی.» ۱۷ 17
Amma ka ɗauki wannan sanda a hannunka domin yă aikata mu’ujizan.”
پس موسی روانه شده، نزد پدر زن خود، یترون، برگشت و به وی گفت: «بروم و نزد برادران خود که در مصرند برگردم، و ببینم که تا کنون زنده‌اند.» یترون به موسی گفت: «به سلامتی برو.» ۱۸ 18
Sai Musa ya koma wurin Yetro surukinsa, ya ce masa, “Bari in koma wurin mutanena a Masar, in ga ko da mai rai a cikinsu.” Yetro ya ce, “Tafi, ka kuma sauka lafiya.”
و خداوند در مدیان به موسی گفت: «روانه شده به مصر برگرد، زیرا آنانی که در قصد جان توبودند، مرده‌اند.» ۱۹ 19
Ubangiji ya riga ya gaya wa Musa a Midiyan, “Koma Masar, domin dukan mutanen da suke neman su kashe ka sun mutu.”
پس موسی زن خویش وپسران خود را برداشته، ایشان را بر الاغ سوارکرده، به زمین مصر مراجعت نمود، و موسی عصای خدا را به‌دست خود گرفت. ۲۰ 20
Sai Musa ya ɗauki matarsa da’ya’yansa maza, ya sa su a kan jaki, suka kama hanya zuwa Masar. Ya kuma ɗauki sandan Allah a hannunsa.
و خداوندبه موسی گفت: «چون روانه شده، به مصرمراجعت کردی، آگاه باش که همه علاماتی را که به‌دستت سپرده‌ام به حضور فرعون ظاهر سازی، و من دل او را سخت خواهم ساخت تا قوم را رهانکند. ۲۱ 21
Ubangiji ya ce wa Musa, “Bayan ka koma Masar, ka tabbata ka aikata dukan mu’ujizan da na sa cikin ikonka a gaban Fir’auna. Amma zan taurare zuciyarsa domin kada yă bar mutanen su tafi.
و به فرعون بگو خداوند چنین می‌گوید: اسرائیل، پسر من و نخست زاده من است، ۲۲ 22
Sa’an nan ka gaya wa Fir’auna, ‘Ga abin da Ubangiji ya ce; Isra’ila shi ne ɗan farina,
و به تو می‌گویم پسرم را رها کن تا مرا عبادت نماید، واگر از رها کردنش ابا نمایی، همانا پسر تو، یعنی نخست زاده تو را می‌کشم.» ۲۳ 23
na gaya maka, “Ka bar ɗana yă tafi domin yă yi mini sujada.” Amma ka ƙi ka bari yă tafi, saboda haka zan kashe ɗan farinka.’”
و واقع شد در بین راه که خداوند در منزل بدو برخورده، قصد قتل وی نمود. ۲۴ 24
Ya zama kuwa sa’ad da Musa yake masauki a kan hanya sai Ubangiji ya gamu da shi, ya nema ya kashe shi.
آنگاه صفوره سنگی تیز گرفته، غلفه پسر خود را ختنه کرد و نزد پای وی انداخته، گفت: «تو مرا شوهرخون هستی.» ۲۵ 25
Amma Ziffora ta ɗauki dutsen ƙanƙara mai ci, ta yanke loɓar ɗanta ta taɓa ƙafafun Musa da shi. Ta ce, “Tabbatacce kai angon jini ne a gare ni.”
پس او وی را رها کرد، آنگاه (صفوره ) گفت: «شوهر خون هستی، » به‌سبب ختنه. ۲۶ 26
Sai Ubangiji ya ƙyale shi. (A lokacin ta ce “angon jini,” tana nufin kaciya.)
و خداوند به هارون گفت: «به سوی صحرا به استقبال موسی برو.» پس روانه شد و او را در جبل الله ملاقات کرده، او را بوسید. ۲۷ 27
Ubangiji ya ce wa Haruna, “Tafi cikin hamada ka sadu da Musa.” Sai ya sadu da Musa a dutsen Allah, ya sumbace shi.
وموسی از جمیع کلمات خداوند که او را فرستاده بود، و از همه آیاتی که به وی امر فرموده بود، هارون را خبر داد. ۲۸ 28
Sai Musa ya gaya wa Haruna dukan abin da Ubangiji ya aike yă faɗa, da kuma dukan mu’ujizan da ya umarce shi yă aikata.
پس موسی و هارون رفته، کل مشایخ بنی‌اسرائیل را جمع کردند. ۲۹ 29
Musa da Haruna suka tattara dukan dattawan Isra’ilawa,
وهارون همه سخنانی را که خداوند به موسی فرموده بود، باز‌گفت، و آیات را به نظر قوم ظاهرساخت. ۳۰ 30
sai Haruna ya gaya musu dukan abin da Ubangiji ya ce wa Musa. Ya kuma aikata mu’ujizan a gaban mutanen,
و قوم ایمان آوردند. و چون شنیدندکه خداوند از بنی‌اسرائیل تفقد نموده، و به مصیبت ایشان نظر انداخته است، به روی درافتاده، سجده کردند. ۳۱ 31
sai suka gaskata. Sa’ad da suka ji cewa Ubangiji ya damu da su, ya kuma ga azabarsu, sai suka durƙusa suka yi sujada.

< خروج 4 >