< استر 7 >

پس پادشاه و هامان نزد استر ملکه به ضیافت حاضر شدند. ۱ 1
Saboda haka sarki da Haman suka tafi cin abinci wurin sarauniya Esta.
و پادشاه در روزدوم نیز در مجلس شراب به استر گفت: «ای استرملکه، مسول تو چیست که به تو داده خواهد شد ودرخواست تو کدام؟ اگر‌چه نصف مملکت باشدبجا آورده خواهد شد.» ۲ 2
Yayinda suke shan ruwan inabi a rana ta biyun nan, sai sarki ya sāke tambaya, “Sarauniya Esta, me kike so? Za a ba ki. Mene ne roƙonki? Ko da rabin masarautata ne, za a ba ki.”
استر ملکه جواب داد و گفت: «ای پادشاه، اگر در نظر تو التفات یافته باشم و اگر پادشاه راپسند آید، جان من به مسول من و قوم من به درخواست من، به من بخشیده شود. ۳ 3
Sai Sarauniya Esta ta amsa ta ce, “In na sami tagomashi a wurinka, ya sarki, in kuma mai girma ya yarda, a bar ni da raina, wannan shi ne roƙona. Ka kuma sa kada a kashe mutanena, wannan ita ce bukata.
زیرا که من و قومم فروخته شده‌ایم که هلاک و نابود و تلف شویم و اگر به غلامی و کنیزی فروخته می‌شدیم، سکوت می‌نمودم با آنکه مصیبت ما نسبت به ضرر پادشاه هیچ است.» ۴ 4
Gama an sayar da ni da mutanena don a hallaka, a karkashe mu, a kuma ƙi mu. Da a ce an sayar da mu kamar bayi maza da mata ne, da na yi shiru, domin wannan zai zama abin da bai taka kara ya karye ba, har da za a dami sarki a kai.”
آنگاه اخشورش پادشاه، استر ملکه راخطاب کرده، گفت: «آن کیست و کجا است که جسارت نموده است تا چنین عمل نماید؟» ۵ 5
Sarki Zerzes ya tambayi Sarauniya Esta ya ce, “Wane ne shi? Ina mutumin da ya yi ƙarfin halin yin wannan karambani?”
استر گفت: «عدو و دشمن، همین هامان شریراست.» آنگاه هامان در حضور پادشاه و ملکه به لرزه درآمد. ۶ 6
Esta ta ce, “Maƙiyi da abokin gāban, shi ne wannan mugun Haman.” Sai Haman ya tsorota a gaban sarki da sarauniya.
و پادشاه غضبناک شده، از مجلس شراب برخاسته، به باغ قصر رفت. و چون هامان دید که بلا از جانب پادشاه برایش مهیا است برپا شد تانزد استر ملکه برای جان خود تضرع نماید. ۷ 7
Sarki ya tashi cikin fushi, ya bar ruwan inabinsa, ya fita zuwa cikin lambun fada. Amma da Haman ya gane cewa sarki ya riga ya yanke shawara a kan ƙaddararsa, ya dakata domin yă roƙi sarauniya Esta saboda ransa.
وچون پادشاه از باغ قصر به‌جای مجلس شراب برگشت، هامان بر بستری که استر بر آن می‌بودافتاده بود، پس پادشاه گفت: «آیا ملکه را نیز به حضور من در خانه بی‌عصمت می‌کند؟» سخن هنوز بر زبان پادشاه می‌بود که روی هامان راپوشانیدند. ۸ 8
Sarki yana dawowa daga lambun fada zuwa babban zauren liyafan ke nan, sai ga Haman ya fāɗi a kan shimfiɗar da Esta take zaune. Sarki ya tā da murya da ƙarfi ya ce, “Har ma zai ci mutuncin sarauniya yayinda take tare da ni a cikin gida?” Sarki bai ma rufe baki ba, sai bayin sarki suka rufe fuskar Haman.
آنگاه حربونا، یکی ازخواجه‌سرایانی که در حضور پادشاه می‌بودند، گفت: «اینک دار پنجاه ذراعی نیز که هامان آن رابه جهت مردخای که آن سخن نیکو را برای پادشاه گفته است مهیا نموده، در خانه هامان حاضر است.» پادشاه فرمود که «او را بر آن مصلوب سازید.» ۹ 9
Sai Harbona, ɗaya daga cikin bābānni masu yi wa sarki hidima ya ce, “Akwai wurin rataye mai laifi da tsayinsa ya kai ƙafa saba’in da biyar yana nan tsaye kusa da gidan Haman. Ya gyara shi ne domin a rataye Mordekai, wanda ya yi cece sarki wanda ya tone makircin masu niyya su hallaka sarki.” Sai sarki ya ce, “Ku rataye shi a kansa!”
پس هامان را بر داری که برای مردخای مهیا کرده بود، مصلوب ساختند و غضب پادشاه فرو نشست. ۱۰ 10
Saboda haka suka rataye Haman a kan wurin rataye mai laifin da shi Haman ya shirya saboda Mordekai. Sa’an nan sarki ya huce.

< استر 7 >