< کارهای رسولان 16 >

و به دربه و لستره آمد که اینک شاگردی تیموتاوس نام آنجا بود، پسر زن یهودیه مومنه لیکن پدرش یونانی بود. ۱ 1
Bulus ya kai Derbe sa’an nan kuma zuwa Listira, inda wani almajiri mai suna Timoti yake da zama, wanda mahaifiyarsa mutuniyar Yahuda ce kuma mai bi ce, amma mahaifinsa mutumin Hellenawa ne.
که برادران در لستره و ایقونیه بر او شهادت می‌دادند. ۲ 2
’Yan’uwa a Listira da Ikoniyum sun yi magana mai kyau ƙwarai a kansa.
چون پولس خواست او همراه وی بیاید، او راگرفته مختون ساخت، به‌سبب یهودیانی که در آن نواحی بودند زیرا که همه پدرش را می‌شناختندکه یونانی بود. ۳ 3
Bulus ya so ya ɗauke shi a tafiyar, saboda haka ya yi masa kaciya, domin Yahudawan da suke da zama a wurin, don duk sun san cewa mahaifinsa mutumin Hellenawa ne.
و در هر شهری که می‌گشتند، قانونها را که رسولان و کشیشان در اورشلیم حکم فرموده بودند، بدیشان می‌سپردند تا حفظ نمایند. ۴ 4
Yayinda suke tafiya daga gari zuwa gari, suka dinga ba da shawarwarin da manzanni da dattawa a Urushalima suka zartar domin mutane su kiyaye.
پس کلیساها در ایمان استوار می‌شدند و روزبروز در شماره افزوده می‌گشتند. ۵ 5
Saboda haka ikkilisiyoyi suka ginu cikin bangaskiya suka kuma yi girma suka yi ta ƙaruwa kowace rana.
و چون از فریجیه و دیار غلاطیه عبورکردند، روح‌القدس ایشان را از رسانیدن کلام به آسیا منع نمود. ۶ 6
Bulus da abokan tafiyarsa suka zazzaga dukan yankin Firjiya da Galatiya, don Ruhu Mai Tsarki ya hana su yin wa’azi a lardin Asiya.
پس به میسیا آمده، سعی نمودندکه به بطینیا بروند، لیکن روح عیسی ایشان رااجازت نداد. ۷ 7
Da suka isa kan iyakar Misiya, suka yi ƙoƙari su shiga Bitiniya, amma Ruhun Yesu bai yarda musu ba.
و از میسیا گذشته به ترواس رسیدند. ۸ 8
Saboda haka suka ratsa Misiya suka zo Toruwas.
شبی پولس را رویایی رخ نمود که شخصی از اهل مکادونیه ایستاده بود التماس نموده گفت: «به مکادونیه آمده، ما را امداد فرما.» ۹ 9
Da dare Bulus ya ga wahayin wani mutumin Makidoniya yana tsaye yana roƙonsa cewa, “Ka zo Makidoniya ka taimake mu.”
چون این‌رویا را دید، بی‌درنگ عازم سفرمکادونیه شدیم، زیرا به یقین دانستیم که خداوندما را خوانده است تا بشارت بدیشان رسانیم. ۱۰ 10
Bayan Bulus ya ga wahayin, muka shirya nan take mu tashi zuwa Makidoniya, mun tabbata cewa, Allah ya kira mu mu yi musu wa’azin bishara.
پس از ترواس به کشتی نشسته، به راه مستقیم به ساموتراکی رفتیم و روز دیگر به نیاپولیس. ۱۱ 11
Daga Toruwas muka tashi zuwa teku muka kuma shiga jirgin ruwa muka miƙe kai tsaye zuwa Samotiras, kashegari kuma muka nufi Neyafolis.
و از آنجا به فیلپی رفتیم که شهر اول ازسرحد مکادونیه و کلونیه است و در آن شهر‌چندروز توقف نمودیم. ۱۲ 12
Daga can muka tafi Filibbi, wata babbar alkaryar Roma wadda kuma take babban birni a gundumar Makidoniya. Muka zauna a can kwanaki masu yawa.
و در روز سبت از شهربیرون شده و به کنار رودخانه جایی که نماز می گذاردند، نشسته با زنانی که در آنجا جمع می‌شدند سخن راندیم. ۱۳ 13
A Asabbaci, muka fita ƙofar birnin zuwa bakin kogi, inda muke tsammani za mu sami wurin yin addu’a. Muka zauna muka fara yin wa matan da suka taru a can magana.
و زنی لیدیه نام، ارغوان فروش، که از شهر طیاتیرا و خداپرست بود، می‌شنید که خداوند دل او را گشود تا سخنان پولس را بشنود. ۱۴ 14
Ɗaya daga cikin waɗanda suka saurare mu mace ce mai suna Lidiya, mai sayar da yadunan jan garura masu tsada daga birnin Tiyatira, mai yi wa Allah sujada. Ubangiji ya buɗe zuciyarta har ta karɓi saƙon Bulus.
و چون او و اهل خانه‌اش تعمید یافتند، خواهش نموده، گفت: «اگر شما رایقین است که به خداوند ایمان آوردم، به خانه من درآمده، بمانید.» و ما را الحاح نمود. ۱۵ 15
Da aka yi mata baftisma tare da iyalin gidanta, sai ta gayyace mu zuwa gidanta. Ta ce, “In kun amince ni mai bi ce cikin Ubangiji, sai ku zo ku sauka a gidana.” Sai ta kuwa rinjaye mu.
و واقع شد که چون ما به محل نمازمی رفتیم، کنیزی که روح تفال داشت و ازغیب گویی منافع بسیار برای آقایان خود پیدامی نمود، به ما برخورد. ۱۶ 16
Wata rana muna tafiya zuwa wurin yin addu’a, sai muka sadu da wata baranya mai ruhun aljani mai duba. Takan samo wa mutanenta kuɗi da yawa, duban da take yi.
و از عقب پولس و ماآمده، ندا کرده، می‌گفت که «این مردمان خدام خدای تعالی می‌باشند که شما را از طریق نجات اعلام می‌نمایند.» ۱۷ 17
Wannan yarinya kuwa ta bi Bulus da kuma sauranmu, tana ihu tana cewa, “Waɗannan mutane bayin Allah Mafi Ɗaukaka ne, suna sanar da ku hanyar ceto.”
و چون این کار را روزهای بسیار می‌کرد، پولس دلتنگ شده، برگشت و به روح گفت: «تو را می‌فرمایم به نام عیسی مسیح ازاین دختر بیرون بیا.» که در ساعت از او بیرون شد. ۱۸ 18
Ta yi ta faɗin haka har kwanaki masu yawa. A ƙarshe Bulus ya damu ƙwarai sai ya juya ya ce wa aljanin, “A cikin sunan Yesu Kiristi na umarce ka, ka rabu da ita!” Nan take aljanin ya rabu da ita.
اما چون آقایانش دیدند که از کسب خودمایوس شدند، پولس و سیلاس را گرفته، در بازارنزد حکام کشیدند. ۱۹ 19
Da iyayengijin baranyar suka ga hanyar samun kuɗinsu ta toshe, sai suka kama Bulus da Sila suka ja su zuwa cikin kasuwa don su fuskanci hukuma.
و ایشان را نزد والیان حاضرساخته، گفتند: «این دو شخص شهر ما را به شورش آورده‌اند و از یهود هستند، ۲۰ 20
Sai suka kawo su a gaban alƙalai suka ce, “Waɗannan Yahudawa ne, suna kuma birkitar mana da gari,
و رسومی را اعلام می‌نمایند که پذیرفتن و به‌جا آوردن آنهابر ما که رومیان هستیم، جایز نیست.» ۲۱ 21
ta wurin koyar da al’adun da ba daidai ba ne mu Romawa mu karɓa ko mu aikata.”
پس خلق بر ایشان هجوم آوردند و والیان جامه های ایشان را کنده، فرمودند ایشان را چوب بزنند. ۲۲ 22
Sai taron suka fāɗa wa Bulus da Sila gaba ɗaya, alƙalan kuwa suka yi umarni a tuɓe su a kuma yi musu dūka.
و چون ایشان را چوب بسیار زدند، به زندان افکندند و داروغه زندان را تاکید فرمودند که ایشان را محکم نگاه دارد. ۲۳ 23
Bayan an yi musu bulala sosai, sai aka jefa su cikin kurkuku, aka umarci mai gadin kurkukun yă tsare su da kyau.
و چون او بدینطورامر یافت، ایشان را به زندان درونی انداخت وپایهای ایشان را در کنده مضبوط کرد. ۲۴ 24
Da karɓan irin umarnan nan, sai ya sa su can cikin ɗakin kurkuku na ciki-ciki, kuma ya ɗaura ƙafafunsu a turu.
اما قریب به نصف شب، پولس و سیلاس دعا کرده، خدا را تسبیح می‌خواندند و زندانیان ایشان را می‌شنیدند. ۲۵ 25
Wajen tsakar dare Bulus da Sila suna addu’a suna rera waƙoƙi ga Allah, sauran’yan kurkuku kuwa suna sauraronsu.
که ناگاه زلزله‌ای عظیم حادث گشت بحدی که بیناد زندان به جنبش درآمد و دفعه همه درها باز شد و زنجیرها از همه فرو ریخت. ۲۶ 26
Ba zato ba tsammani sai aka yi wata babbar girgizar ƙasa har tushen ginin kurkukun ya jijjiga. Nan da nan sai duk ƙofofin kurkukun suka bubbuɗe, sarƙoƙin kowa kuma suka ɓaɓɓalle.
اما داروغه بیدار شده، چون درهای زندان را گشوده دید، شمشیر خود راکشیده، خواست خود را بکشد زیرا گمان برد که زندانیان فرار کرده‌اند. ۲۷ 27
Mai gadin kurkukun ya farka daga barci, sa’ad da ya ga ƙofofin kurkukun a buɗe, sai ya zāre takobinsa yana shirin kashe kansa domin ya ɗauka’yan kurkukun sun gudu.
اما پولس به آواز بلندصدا زده، گفت: «خود را ضرری مرسان زیرا که ماهمه در اینجا هستیم.» ۲۸ 28
Amma Bulus ya yi ihu ya ce, “Kada ka yi wa kanka lahani! Dukanmu muna nan!”
پس چراغ طلب نموده، به اندرون جست و لرزان شده، نزد پولس وسیلاس افتاد. ۲۹ 29
Mai gadin kurkukun ya kira a kawo fitilu, ya ruga ciki ya fāɗi yana rawan jiki a gaban Bulus da Sila.
و ایشان را بیرون آورده، گفت: «ای آقایان، مرا چه باید کرد تا نجات یابم؟» ۳۰ 30
Sai ya fito da su waje ya kuma tambaye su ya ce, “Ranku yă daɗe, me zan yi domin in sami ceto?”
گفتند: «به خداوند عیسی مسیح ایمان آور که تو و اهل خانه ات نجات خواهید یافت.» ۳۱ 31
Suka amsa suka ce, “Ka gaskata da Ubangiji Yesu, za ka sami ceto, kai da iyalinka.”
آنگاه کلام خداوند را برای او وتمامی اهل بیتش بیان کردند. ۳۲ 32
Sa’an nan suka yi masa maganar Ubangiji shi da kuma dukan sauran da suke a gidansa.
پس ایشان را برداشته، در همان ساعت شب زخمهای ایشان را شست و خود و همه کسانش فی الفور تعمید یافتند. ۳۳ 33
A wannan sa’a na daren, mai gadin kurkukun ya ɗauke su ya wanke musu raunukansu; nan take aka yi masa baftisma da dukan iyalinsa.
و ایشان را به خانه خود درآورده، خوانی پیش ایشان نهاد و باتمامی عیال خود به خدا ایمان آورده، شادگردیدند. ۳۴ 34
Sai mai gadin kurkukun ya kawo su cikin gidansa ya ba su abinci; ya kuwa cika da murna don yă gaskata da Allah, shi da dukan iyalinsa.
اما چون روز شد، والیان فراشان فرستاده، گفتند: «آن دو شخص را رها نما.» ۳۵ 35
Da gari ya waye, sai alƙalan suka aika ma’aikatansu wajen mai gadin kurkukun da umarni cewa, “Ka saki mutanen nan.”
آنگاه داروغه پولس را از این سخنان آگاهانیدکه «والیان فرستاده‌اند تا رستگار شوید. پس الان بیرون آمده، به سلامتی روانه شوید.» ۳۶ 36
Sai mai gadin kurkukun ya gaya wa Bulus cewa, “Alƙalai sun ba da umarni a sake ku kai da Sila. Yanzu sai ku tafi. Ku sauka lafiya.”
لیکن پولس بدیشان گفت: «ما را که مردمان رومی می‌باشیم، آشکارا و بی‌حجت زده، به زندان انداختند. آیا الان ما را به پنهانی بیرون می‌نمایند؟ نی بلکه خود آمده، ما را بیرون بیاورند. ۳۷ 37
Amma Bulus ya ce wa ma’aikatan, “Sun yi mana dūka a fili ba tare da shari’a ba, ko da yake mu’yan ƙasar Roma ne, suka kuma jefa mu cikin kurkuku. Yanzu suna so su fitar da mu a ɓoye? A’a! Sai dai su zo da kansu su rako mu waje.”
پس فراشان این سخنان را به والیان گفتند و چون شنیدند که رومی هستند بترسیدند ۳۸ 38
Sai ma’aikatan suka faɗa wa alƙalan wannan, da suka ji cewa Bulus da Sila Romawa ne, sai suka ji tsoro.
و آمده، بدیشان التماس نموده، بیرون آوردندو خواهش کردند که از شهر بروند. ۳۹ 39
Sai suka zo don su roƙe su, suka yi musu rakiya daga kurkukun, suna roƙonsu su bar birnin.
آنگاه اززندان بیرون آمده، به خانه لیدیه شتافتند و بابرادران ملاقات نموده و ایشان را نصیحت کرده، روانه شدند. ۴۰ 40
Bayan Bulus da Sila suka fita daga kurkukun, sai suka tafi gidan Lidiya, inda suka sadu da’yan’uwa suka kuma ƙarfafa su. Sa’an nan suka tafi.

< کارهای رسولان 16 >