< Matei 18 >

1 Gene mobhago bhaajiganywa gubhaajendelenje a Yeshu, gubhabhushiyenje, “Gani ali jwankulungwa Muupalume gwa Kunnungu?”
A lokacin nan sai almajirai suka zo wurin Yesu suka yi tambaya suka ce, “Wane ne mafi girma a mulkin sama?”
2 A Yeshu gubhanshemile mwana jumo, gubhannjimishe pakati jabhonji,
Sai ya kira ƙaramin yaro ya sa shi yă tsaya a tsakiyarsu.
3 gubhashite, “Kweli ngunakummalanjilanga, nkatendebhukanje nibha malinga bhana, ngu, nkajinjilanga Muupalume gwa Kunnungu.”
Sai ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, in ba kun canja kuka zama kamar ƙananan yara ba, labudda, ba za ku shiga mulkin sama ba.
4 Jojowe akwiinyegaya nibha malinga aju mwanaju, jwenejo shaabhe jwankulungwa Muupalume gwa Kunnungu.
Saboda haka, duk wanda ya ƙasƙantar da kansa kamar wannan yaro, shi ne mafi girma a mulkin sama.
5 Jojowe akumposhela mwana jumo malinga jweneju kwa ligongo lyangu nne, anamboshela nne.
Duk kuma wanda ya karɓi ƙaramin yaro kamar wannan a cikin sunana ya karɓe ni ne.
6 Jojowe shannebhye jumo jwa bhashokonji bhaangulupalinga nne, mbaya akatabhilwe liganga likulungwa nnukoi nileshelwa pa shilindili sha mashi.
“Amma duk wanda ya sa ɗaya daga cikin ƙananan nan da suka gaskata da ni ya yi zunubi, zai fiye masa a rataya babban dutsen niƙa a wuyarsa, a kuma nutsar da shi a zurfin teku.
7 Ole gwenunji bhandu bha pa shilambolyo kwa ligongo lya ilokoli. Ilokoli shiikoposhele, ikabheje ole gwakwe jwene shaikumbuyejo.
Kaiton duniya saboda abubuwan da suke sa mutane su yi zunubi! Dole irin waɗannan abubuwa su zo, sai dai kaiton mutumin da ya zama sanadin kawo su!
8 “Monaga nkono eu lukongono lwenu lunnebhyaga, nnukate na nnjae kwataliya. Mbaya nnjinjile mugumi gwa pitipiti nni gwangali nkono eu lukongono, nngalingana na leshelwa pa moto gwa pitipiti nni na makono na makongono genu ganaabhili. (aiōnios g166)
In hannunka ko ƙafarka yana sa ka zunubi, yanke shi ka yar. Zai fiye maka ka shiga rai da hannu ko ƙafa ɗaya da hannuwa biyu ko ƙafafu biyu da a jefar da kai cikin madawwamiyar wuta da hannuwa biyu ko ƙafafu biyu. (aiōnios g166)
9 Liyo lyenu linnebhyaga, nnikolotole na kulijaa kwataliya. Mbaya nnjinjile mugumi gwa pitipiti nni na shongo, nngalingana leshelwa pa moto gwa ku Jeanamu nni na meyo genu ganaabhili. (Geenna g1067)
In kuma idonka yana sa ka zunubi, ƙwaƙule shi ka yar. Zai fiye maka ka shiga rai da ido ɗaya, da ka shiga jahannama ta wuta da idanunka biyu. (Geenna g1067)
10 “Mwiteiganje! Nnannyegayanje jumo jwa bhashokonjibha. Ngunakummalanjilanga, ashimalaika bhabhonji kunnunguko mobha gowe pubhalinginji tome na Atati bha Kunnungu.
“Ku lura, kada ku rena ɗaya daga cikin waɗannan ƙanana. Gama ina faɗa muku mala’ikunsu a sama kullum suna duban fuskar Ubana da yake cikin sama.
11 Pabha Mwana juka Mundu ashinkwiya kwaatapulanga bhandu bhaobhilenje.
12 Nkubhonanga bhuli? Mundu akolaga ngondolo makumi kumi, anng'obhaga jumo, shatende bhuli? Anakwiileka ngondolo makumi tisha na tisha ila pa shitumbi, nikwenda kunnoleya aobhile jula.
“Me kuka gani? In wani yana da tumaki ɗari, sai ɗaya daga cikinsu ta ɓace, ba sai yă bar tasa’in da taran a kan tuddai yă je neman guda ɗayan da ta ɓace ba?
13 Kweli ngunakummalanjilanga, ampataga apinga kwinonyela kupunda makumi tisha na tisha yangaobha ila.
In kuwa ya same ta, ina gaya muku gaskiya, zai yi murna saboda ɗayan fiye da tasa’in da taran da ba su ɓace ba.
14 Nneyo peyo, Ainabhenunji bha Kunnungu bhakaapinga aobhe nkali jumo jwa bhashokonjibha.
Haka ma Ubanku da yake cikin sama ba ya so ko ɗaya daga cikin ƙananan nan yă ɓace.
15 “Mpwenu annebhelaga, munjendele nkanneye nninginji mmabhilipe. Ampilikanaga mumpatile mpwenu.
“In ɗan’uwanka ya yi maka laifi, ka je ka nuna masa laifinsa, tsakaninku biyu kaɗai. In ya saurare ka, ka maido da ɗan’uwanka ke nan.
16 Akampilikane, nnjende naka mundu jumo eu bhabhili na mmayene, nkupinga kwa ukong'ondelo gwa bhandu bhabhili eu bhatatu, monaga lipali lilobhe limanyishe nimala.
Amma in bai saurare ka ba, ka je tare da mutum ɗaya ko biyu, domin ‘a tabbatar da kowace magana a bakin shaidu biyu ko uku.’
17 Akaapilikanilanje bhanganyabho, mwaalugulilanje bhandu bha nnikanisha. Na monaga akaapilikanilanje, mumone malinga bhandu bhakakwaamanyanga a Nnungu eu bhakamula koli.
In kuwa ya ƙi yă saurare su, sai ka gaya wa ikkilisiya; in kuma ya ƙi yă saurari ikkilisiya ma, ka yi da shi kamar marar sanin Allah ko mai karɓar haraji.
18 “Kweli ngunakummalanjilanga, shoshowe shishintabhanje pa shilambolyo, shishitabhwe kunnungu, na shoshowe shishinngopolanje pa shilambolyo shishigopolwe kunnungu.
“Gaskiya nake gaya muku, duk abin da kuka daure a duniya, za a daure a sama, duk kuma abin da kuka kunce a duniya, za a kunce shi a sama.
19 Kweli ngunakummalanjilanga kabhili, bhabhili bhenunji pa shilambolyo bhalaganangaga shoshowe sha juga, Atati bhali kunnungu shibhaatendelanje.
“Har wa yau, ina gaya muku cewa in mutum biyu a cikinku a duniya suka yarda su roƙi wani abu, Ubana da yake cikin sama zai yi muku.
20 Pabha popowe pubhaimananga bhandu bhabhlili eu bhatatu kwa ligongo lyangu nne, nne mbali pamo na bhanganyabho.”
Gama inda mutum biyu ko uku suka taru cikin sunana, a can ma ina tare da su.”
21 Kungai a Petili gubhaajendele a Yeshu, gubhaabhushiye, “Bhuli Mmakulungwa, mpwanga anebhele palingwa ninneshelele? Nkali pa shabha?”
Sai Bitrus ya zo wurin Yesu ya yi masa tambaya ya ce, “Ubangiji, sau nawa zan yafe wa ɗan’uwana sa’ad da ya yi mini zunubi? Har sau bakwai?”
22 A Yeshu gubhaajangwile, “Ngaalugula mala shabhape, ikabhe nkali makumi shabha mala shabha.
Yesu amsa ya ce, “Ina gaya maka, ba sau bakwai ba, amma sau saba’in da bakwai.
23 Pabha Upalume gwa Kunnungu unalandana naka mpalume jumo atendile eshabhu ika ntumishi jwakwe.
“Saboda haka, mulkin sama yana kama da wani sarki wanda ya so yă yi ƙididdigar dukiyarsa da take a hannun bayinsa.
24 Eshabhu ikatandubheje, gubhapeleshelwe mundu jumo alongwaga ligambo mmbiya yaigwinji.
Da ya fara ƙididdigar, sai aka kawo masa wani wanda yake bin bashin talenti dubu goma.
25 Jwene mundujo akakweteje shindu sha lipa, bhakulungwa bhakwe gubhaamulishe aushwe jwenejo na akagwe na ashibhanagwe na indu yowe yaakwete, nkupinga lipila ligambo lila.
Da yake bai iya biya ba, sai maigida ya umarta a sayar da shi da matarsa da yaransa da kuma duk abin da yake da shi, a biya bashin.
26 Bhai, ntumishi jula gwabhatindibhalile, nigwashite, ‘Nnindile shininnipe ligambo lyenu lyowe.’
“Bawan ya durƙusa a gabansa. Ya yi roƙo ya ce, ‘Ka yi mini haƙuri, zan biya ka ƙaf.’
27 Bhakulungwa bhala gubhammonele shiya ntumishi jula, gubhanneshelele ligambo lila, gubhanneshile aijabhulile.
Maigidan bawan ya ji tausayinsa, ya yafe masa bashin, ya kuma sake shi.
28 “Ntumishi jula gwajabhwile, gwanng'imene ntumishi nnjakwe annongaga ligambo lya mmbiya makumi kumi. Gubhankamwile, nikunkida pa nngulo alinkuti, ‘Unipe inguulonga!’
“Amma da wannan bawa ya fita, sai ya gamu da wani abokin bautarsa wanda yake binsa bashin dinari ɗari. Sai ya cafke shi, ya shaƙe shi a wuya yana cewa, ‘Biya ni abin da nake binka!’
29 Ntumishi nnjakwe jula akuntindibhalilaga nikunshondelesheya, alinkuti ‘Nninde shininnipe yowe’.
“Wannan abokin bautarsa ya durƙusa ya roƙe shi, ‘Ka yi mini haƙuri, zan biya ka.’
30 Ikabheje jwanngakunda, gwapite kuntabha kuligelesha mpaka pushalipe ligambo lyowe.
“Amma ya ƙi. A maimako, sai ya je ya sa aka jefa shi a kurkuku, har yă biya bashin.
31 “Bhai, bhatumishi ajakwenji bhakaibhonanjeje itendeshe gubhainginikenje kwa kaje, nigubhapite kwatashiyanga bhakulungwa bhabhonji gakoposhele.
Sa’ad da sauran bayin suka ga abin da ya faru, abin ya ɓata musu rai ƙwarai, sai suka tafi suka faɗa wa maigidansu dukan abin da ya faru.
32 Bhakulungwa bhala gubhanshemile ntumishi jula, gubhammalanjlile, ‘Ugwe ujwanyata ntima! Gwashinkunyuga nikuleshelele, gunikuleshelele ligambo lyako lyowe.
“Sai maigidan ya kira wannan bawa. Ya ce, ‘Kai mugun bawa, na yafe duk bashin da nake binka domin ka roƙe ni.
33 Bhuli, ikapinjikweje ugwe kummonnela shiya ntumishi nnjako malinga shinikubhonele shiya nne?’
Ashe, bai kamata kai ma ka ji tausayin abokin bautarka yadda na yi maka ba?’
34 “Bhai, bhakulungwa bhala gubhatumbele kaje, nigubhampeleshe akapotekwe mpaka pushalipe ligambo lyowe.
Cikin fushi, maigidan ya miƙa shi ga ma’aikatan kurkuku su gwada masa azaba, har yă biya dukan bashin da ake binsa.
35 A Yeshu gubhashite, Atati bhali kunnungu shibhantendelanje nneyo peyo monaga mundu akanneshelele mpwakwe mpaka muntima.”
“Haka Ubana da yake cikin sama zai yi da kowannenku, in ba ku yafe wa’yan’uwanku daga zuciyarku ba.”

< Matei 18 >