< Lamentazioni 5 >

1 Ricordati, Signore, di quanto ci è accaduto, guarda e considera il nostro obbrobrio.
Ka tuna, ya Ubangiji, abin da ya faru da mu; duba, ka ga kunyar da muka sha.
2 La nostra eredità è passata a stranieri, le nostre case a estranei.
An ba wa baƙi gādonmu, gidajenmu kuma aka ba bare.
3 Orfani siam diventati, senza padre; le nostre madri come vedove.
Mun zama marayu marasa ubanni, uwayenmu kamar gwauraye.
4 L'acqua nostra beviamo per denaro, la nostra legna si acquista a pagamento.
Dole mu sayi ruwan da muke sha; sai mun biya mu sami itace.
5 Con un giogo sul collo siamo perseguitati siamo sfiniti, non c'è per noi riposo.
Masu fafararmu sun kusa kama mu; mun gaji kuma ba dama mu huta.
6 All'Egitto abbiamo teso la mano, all'Assiria per saziarci di pane.
Mun miƙa kanmu ga Masar da Assuriya don mu sami isashen abinci.
7 I nostri padri peccarono e non sono più, noi portiamo la pena delle loro iniquità.
Kakanninmu sun yi zunubi kuma ba sa nan yanzu, mu ne aka bari muna shan hukuncinsu.
8 Schiavi comandano su di noi, non c'è chi ci liberi dalle loro mani.
Bayi suna mulki a kanmu, kuma ba wanda zai’yantar da mu daga hannuwansu.
9 A rischio della nostra vita ci procuriamo il pane davanti alla spada nel deserto.
Muna samun burodi a bakin rayukanmu domin takobin da yake a jeji.
10 La nostra pelle si è fatta bruciante come un forno a causa degli ardori della fame.
Fatar jikinmu ta yi zafi kamar murhu, muna jin zazzaɓi domin yunwa.
11 Han disonorato le donne in Sion, le vergini nelle città di Giuda.
An yi wa mata fyaɗe a cikin Sihiyona, da kuma budurwai a cikin garuruwan Yahuda.
12 I capi sono stati impiccati dalle loro mani, i volti degli anziani non sono stati rispettati.
An rataye’ya’yan sarakuna da hannuwansu; ba a ba wa dattawa girma.
13 I giovani han girato la mola; i ragazzi son caduti sotto il peso della legna.
Samari suna faman yin niƙa; yara kuma suna fama da ƙyar da nauyin kayan itace.
14 Gli anziani hanno disertato la porta, i giovani i loro strumenti a corda.
Dattawan sun bar ƙofar birnin, samari sun daina rera waƙa.
15 La gioia si è spenta nei nostri cuori, si è mutata in lutto la nostra danza.
Farin ciki ya rabu da zuciyarmu; rayuwarmu ta zama makoki.
16 E' caduta la corona dalla nostra testa; guai a noi, perché abbiamo peccato!
Rawani ya fāɗi daga kanmu. Kaiton mu gama mun yi zunubi!
17 Per questo è diventato mesto il nostro cuore, per tali cose si sono annebbiati i nostri occhi:
Domin wannan zuciyarmu ta yi sanyi; domin waɗannan abubuwa idanunmu sun dushe
18 perché il monte di Sion è desolato; le volpi vi scorrazzano.
gama Tudun Sihiyona ya zama kufai, sai diloli ke yawo a wurin.
19 Ma tu, Signore, rimani per sempre, il tuo trono di generazione in generazione.
Ya Ubangiji, kai ne mai iko har abada; kursiyinka ya dawwama cikin dukan zamani.
20 Perché ci vuoi dimenticare per sempre? Ci vuoi abbandonare per lunghi giorni?
Don mene ne kake mantawa da mu koyaushe? Me ya sa ka yashe mu da jimawa?
21 Facci ritornare a te, Signore, e noi ritorneremo; rinnova i nostri giorni come in antico,
Ka sāke jawo mu gare ka, ya Ubangiji, don mu komo; ka sabunta kwanakinmu su zama kamar yadda suke a dā
22 poiché non ci hai rigettati per sempre, nè senza limite sei sdegnato contro di noi.
sai dai in ka ƙi mu gaba ɗaya kana fushi da mu fiye da yadda za a iya aunawa.

< Lamentazioni 5 >