< Mattiyu 28 >

1 Da daddare ranar Asabaci, rana ta fari ga mako ta fara gabatowa, Maryamu Magadaliya da daya Maryamun suka zo don su ziyarci kabarin.
Or, sur le tard, le jour du sabbat, au crépuscule du premier jour de la semaine, Marie de Magdala et l’autre Marie vinrent voir le sépulcre.
2 Sai aka yi girgizar kasa mai karfi, saboda mala'ikan Ubangiji ya sauko daga sama ya kuma murgine dutsen ya zauna a kai.
Et voici, il se fit un grand tremblement de terre; car un ange du Seigneur, descendant du ciel, vint et roula la pierre, et s’assit sur elle.
3 Kamanninsa kamar walkiya, tufafinsa kuma fari fat kamar suno.
Et son aspect était comme un éclair, et son vêtement blanc comme la neige.
4 Masu tsaron suka razana don tsoro suka zama kamar matattun mutane.
Et de la frayeur qu’ils en eurent, les gardiens tremblèrent et devinrent comme morts.
5 Mala'ikan ya yi wa matan magana cewa, “Kada ku ji tsoro, nasan kuna neman Yesu wanda aka gicciye.
Et l’ange, répondant, dit aux femmes: Pour vous, n’ayez point de peur; car je sais que vous cherchez Jésus le crucifié;
6 Baya nan, amma ya tashi kamar yadda ya fada. Ku zo ku ga wurin da aka kwantar da shi.
il n’est pas ici; car il est ressuscité, comme il l’avait dit. Venez, voyez le lieu où le Seigneur gisait;
7 Ku hanzarta ku gaya wa almajiransa, 'Ya tashi daga matattu. Duba, ya tafi Galili, can zaku same shi.' Gashi ni kuwa na fada maku.”
et allez promptement, et dites à ses disciples qu’il est ressuscité des morts. Et voici, il s’en va devant vous en Galilée: là vous le verrez; voici, je vous l’ai dit.
8 Matan suka yi hanzari suka bar kabarin da tsoro da murna, suka ruga domin su sanar wa almajiransa.
Et sortant promptement du sépulcre avec crainte et une grande joie, elles coururent l’annoncer à ses disciples.
9 Sai ga Yesu ya tare su, yace masu, “A gaishe ku.” Sai matan suka kama kafar sa, suka kuma yi masa sujada.
Et comme elles allaient pour l’annoncer à ses disciples, voici aussi Jésus vint au-devant d’elles, disant: Je vous salue. Et elles, s’approchant de lui, saisirent ses pieds et lui rendirent hommage.
10 Sai Yesu yace masu, “Kada ku ji tsoro. Ku je ku fada wa 'yan'uwana su je Galili. Can zasu ganni.”
Alors Jésus leur dit: N’ayez point de peur; allez annoncer à mes frères qu’ils aillent en Galilée, et là ils me verront.
11 Sa'adda matan suke tafiya, sai wadansu masu tsaro suka shiga gari suka fada wa Shugabanin Firistoci dukan abin da ya faru.
Et comme elles s’en allaient, voici, quelques hommes de la garde s’en allèrent dans la ville, et rapportèrent aux principaux sacrificateurs toutes les choses qui étaient arrivées.
12 Firistocin suka hadu da dattawa suka tattauna al'amarin, sai suka bada kudi masu yawa ga sojojin
Et s’étant assemblés avec les anciens, ils tinrent conseil et donnèrent une bonne somme d’argent aux soldats,
13 Sukace masu, “Ku gaya wa sauran cewa, “Almajiran Yesu sun zo da daddare sun sace gangar jikinsa lokacin da muke barci.”
disant: Dites: ses disciples sont venus de nuit, et l’ont dérobé pendant que nous dormions;
14 Idan wannan rahoto ya isa wurin gwamna, za mu lallashe shi mu ja hankalinsa mu raba ku da damuwa.”
et si le gouverneur vient à en entendre parler, nous le persuaderons, et nous vous mettrons hors de souci.
15 Sai sojojin suka karbi kudin suka yi abinda aka umarcesu. Wannan rahoto ya bazu a tsakanin Yahudawa, ya ci gaba har zuwa yau.
Et eux, ayant pris l’argent, firent comme ils avaient été enseignés; et cette parole s’est répandue parmi les Juifs jusqu’à aujourd’hui.
16 Amma almajiran sha daya suka tafi Galili, kan dutsen da Yesu ya umarcesu.
Et les onze disciples s’en allèrent en Galilée, sur la montagne où Jésus leur avait ordonné [de se rendre].
17 Da suka gan shi, suka yi masa sujada, amma wadansu suka yi shakka.
Et l’ayant vu, ils lui rendirent hommage; mais quelques-uns doutèrent.
18 Yesu ya zo wurin su ya yi masu magana, yace, “Dukan iko dake sama da kasa an ba ni.
Et Jésus, s’approchant, leur parla, disant: Toute autorité m’a été donnée dans le ciel et sur la terre.
19 Sai kuje ku almajirantar da dukan al'ummai. Kuna yi masu baftisma cikin sunan Uba da na Da da na Ruhu Mai Tsarki.
Allez donc, et faites disciples toutes les nations, les baptisant pour le nom du Père et du Fils et du Saint Esprit,
20 Ku koya masu su kiyaye dukan abin da na umarce ku. Duba, ni kuma kullum ina tare da ku har karshen zamani.” (aiōn g165)
leur enseignant à garder toutes les choses que je vous ai commandées. Et voici, moi je suis avec vous tous les jours, jusqu’à la consommation du siècle. (aiōn g165)

< Mattiyu 28 >