< Mattiyu 25 >

1 Sa'annan mulkin sama zai zama kamar budurwai goma da suka dauki fitilunsu domin su taryi ango.
“Then the Kingdom of Heaven will be like ten virgins who took their lamps and went out to meet the bridegroom.
2 Biyar daga cikin su masu hikima ne biyar kuma wawaye.
Five of them were foolish, and five were wise.
3 Sa'adda wawayen budurwai suka dauki fitilunsu, ba su dauki karin mai ba.
Those who were foolish, when they took their lamps, took no oil with them,
4 Amma budurwai masu hikimar suka dauki gorar mai tare da fitilunsu.
but the wise took oil in their vessels with their lamps.
5 To da angon ya makara, dukkan su sai suka fara gyangyadi sai barci ya dauke su.
Now while the bridegroom delayed, they all slumbered and slept.
6 Amma da tsakkar dare sai aka yi shela, 'Ga ango ya iso! Ku fito taryensa.
But at midnight there was a cry, ‘Behold! The bridegroom is coming! Come out to meet him!’
7 Sai dukka budurwan nan suka tashi suka gyaggyara fitilunsu.
Then all those virgins arose, and trimmed their lamps.
8 Wawayen su ka ce da masu hikimar, 'Ku sammana kadan daga manku gama fitilunmu su na mutuwa.'
The foolish said to the wise, ‘Give us some of your oil, for our lamps are going out.’
9 “Amma masu hikimar suka ce 'Tun da man ba zai ishe mu tare da ku ba, sai ku je gun ma su sayarwa ku sayo wa kanku.
But the wise answered, saying, ‘What if there isn’t enough for us and you? You go rather to those who sell, and buy for yourselves.’
10 Sa'adda suka tafi sayan man, sai angon ya shigo, kuma wadanda suke a shirye su ka shiga tare da shi bukin auren, sai aka rufe kofar.
While they went away to buy, the bridegroom came, and those who were ready went in with him to the wedding feast, and the door was shut.
11 Bayan dan lokaci kadan sauran budurwan suka dawo suna cewa, 'Mai gida, mai gida, bude mana kofar.'
Afterward the other virgins also came, saying, ‘Lord, Lord, open to us.’
12 Amma ya amsa ya ce, 'A gaskiya ina gaya maku, ni ban san ku ba.'
But he answered, ‘Most certainly I tell you, I don’t know you.’
13 Don haka sai ku lura, don baku san rana ko sa'a ba.
Watch therefore, for you don’t know the day nor the hour in which the Son of Man is coming.
14 Domin yana kama da wani mutum da zai tafi wata kasa. Ya kira barorinsa ya ba su dukiyar sa.
“For it is like a man going into another country, who called his own servants and entrusted his goods to them.
15 Ga wani ya ba shi talanti biyar, ga wani ya ba shi biyu, ga wani kuma ya ba shi talanti daya. kowa an bashi gwargwadon iyawarsa, sai wannan mutum ya yi tafiyar sa
To one he gave five talents, to another two, to another one, to each according to his own ability. Then he went on his journey.
16 nan da nan sai wanda ya karbi talanti biyar ya sa nasa a jari, ya sami ribar wasu talanti biyar.
Immediately he who received the five talents went and traded with them, and made another five talents.
17 Haka ma wanda ya karbi talanti biyu ya sami ribar wasu biyu.
In the same way, he also who got the two gained another two.
18 Amma bawan da ya karbi talanti dayan ya yi tafiyar sa, ya haka rami, ya binne kudin mai gidansa.
But he who received the one talent went away and dug in the earth and hid his lord’s money.
19 To bayan tsawon lokaci sai ubangidan barorin nan ya dawo, domin yayi lissafin kudinsu.
“Now after a long time the lord of those servants came, and settled accounts with them.
20 Bawan da ya karbi talanti biyar, ya kawo nasa da ribar wasu biyar. Yace, 'Maigida, ka bani talanti biyar, gashi na samo ribar karin talanti biyar.'
He who received the five talents came and brought another five talents, saying, ‘Lord, you delivered to me five talents. Behold, I have gained another five talents in addition to them.’
21 Maigidansa yace masa, 'Madalla, bawa na gari mai aminci! Ka yi aminci akan abu kadan. Zan sa ka akan abubuwa masu yawa. Ka shiga cikin farincikin maigidanka.'
“His lord said to him, ‘Well done, good and faithful servant. You have been faithful over a few things, I will set you over many things. Enter into the joy of your lord.’
22 Bawan da ya karbi talanti biyun, ya zo yace, 'Maigida, ka ba ni talanti biyu. Gashi kuwa na sami karin ribar wasu biyun.'
“He also who got the two talents came and said, ‘Lord, you delivered to me two talents. Behold, I have gained another two talents in addition to them.’
23 Ubangidansa yace masa, 'Madalla, kai bawa na gari mai aminci! Ka yi aminci akan abubuwa kadan. Zan saka akan abubuwa masu yawa. Ka shiga cikin farincikin maigidanka.'
“His lord said to him, ‘Well done, good and faithful servant. You have been faithful over a few things. I will set you over many things. Enter into the joy of your lord.’
24 Sai bawan da ya karbi talanti daya ya zo yace, 'Maigida, na san kai mai tsanani ne. Kana girbi inda baka yi shuka ba, kuma kana tattarawa inda ba ka watsa ba.
“He also who had received the one talent came and said, ‘Lord, I knew you that you are a hard man, reaping where you didn’t sow, and gathering where you didn’t scatter.
25 Na ji tsoro, don haka sai na je na boye talantinka a rami. Duba, ga abinda yake naka.'
I was afraid, and went away and hid your talent in the earth. Behold, you have what is yours.’
26 Amma ubangidansa ya amsa yace, kai mugu malalacin bawa, ka san cewa ni mai girbi ne inda ban shuka ba kuma ina tattarawa inda ban zuba ba.
“But his lord answered him, ‘You wicked and slothful servant. You knew that I reap where I didn’t sow, and gather where I didn’t scatter.
27 To da ba sai ka kai kudina a banki ba, da bayan na dawo da sai in karbi abina da riba.
You ought therefore to have deposited my money with the bankers, and at my coming I should have received back my own with interest.
28 Saboda haka ku kwace talantin daga gare shi ku baiwa mai talanti goman nan.
Take away therefore the talent from him and give it to him who has the ten talents.
29 Gama ga wanda yake da shi za'a kara masa har ma a yalwace za'a kara bashi. Amma ga wanda bashi da komai abinda ke nasa ma za'a kwace.
For to everyone who has will be given, and he will have abundance, but from him who doesn’t have, even that which he has will be taken away.
30 Ku jefa wannan mugun bawan marar amfani, cikin duhu mai zurfi, inda ake kuka da cizon hakora.'
Throw out the unprofitable servant into the outer darkness, where there will be weeping and gnashing of teeth.’
31 Sa'adda Dan mutum zai zo cikin daukakarsa da dukan Mala'iku tare da shi, sa'annan zai zauna kursiyinsa na daukaka.
“But when the Son of Man comes in his glory, and all the holy angels with him, then he will sit on the throne of his glory.
32 A gabansa za'a tattara dukkan al'ummai, zai rarraba mutanen daya'daya, kamar yadda makiyayi yake rarraba tumaki daga awaki.
Before him all the nations will be gathered, and he will separate them one from another, as a shepherd separates the sheep from the goats.
33 Zai sa tumakin a hannunsa na dama, amma awakin a hannunsa na hagu.
He will set the sheep on his right hand, but the goats on the left.
34 Sa'annan sarkin zai ce wa na hannun damarsa, 'Ku zo ku da Ubana ya albarkata, ku gaji mulkin da aka shirya maku kafin a kafa duniya.
Then the King will tell those on his right hand, ‘Come, blessed of my Father, inherit the Kingdom prepared for you from the foundation of the world;
35 Gama na ji yunwa kuka bani abinci; Na ji kishi kuka bani ruwa; Na yi bakunci kun bani masauki;
for I was hungry and you gave me food to eat. I was thirsty and you gave me drink. I was a stranger and you took me in.
36 Na yi huntanci kuka tufasar dani; Na yi ciwo kuka kula dani; Ina kurkuku kuka ziyarceni.'
I was naked and you clothed me. I was sick and you visited me. I was in prison and you came to me.’
37 Sa'annan masu adalcin za su amsa su ce, 'Ubangiji, yaushe muka ganka kana jin yunwa muka baka abinci? Ko kana jin kishi muka baka ruwan sha?
“Then the righteous will answer him, saying, ‘Lord, when did we see you hungry and feed you, or thirsty and give you a drink?
38 Kuma yaushe muka ganka kana bakunci har muka baka masauki? Ko kuma kana huntanci da muka tufatar da kai?
When did we see you as a stranger and take you in, or naked and clothe you?
39 Yaushe kuma muka ganka kana ciwo ko a kurkuku har muka ziyarce ka?'
When did we see you sick or in prison and come to you?’
40 Sa'annan Sarkin zai amsa masu yace, 'Hakika Ina gaya maku, duk abinda kuka yi wa daya mafi kakanta daga cikin 'yan'uwana a nan ni kuka yi wa.'
“The King will answer them, ‘Most certainly I tell you, because you did it to one of the least of these my brothers, you did it to me.’
41 Sa'annan zai cewa wadanda suke hannunsa na hagu, 'Ku rabu da ni, ku la'anannu, ku tafi cikin wutar jahannama da aka shirya wa Shaidan da aljannunsa, (aiōnios g166, questioned)
Then he will say also to those on the left hand, ‘Depart from me, you cursed, into the eternal fire which is prepared for the devil and his angels; (aiōnios g166)
42 domin ina jin yunwa baku bani abinci ba; ina jin kishi ba ku bani ruwa ba;
for I was hungry, and you didn’t give me food to eat; I was thirsty, and you gave me no drink;
43 Ina bakunci amma baku bani masauki ba; ina huntanci, baku tufasar da ni ba; ina ciwo kuma ina kurkuku, baku kula da ni ba.'
I was a stranger, and you didn’t take me in; naked, and you didn’t clothe me; sick, and in prison, and you didn’t visit me.’
44 Sa'annan suma zasu amsa su ce, 'Ubangiji, yaushe muka ganka kana jin yunwa, ko kishin ruwa, ko kana bakunci, ko kana huntanci, ko ciwo, kuma a kurkuku, da bamu yi maka hidima ba?'
“Then they will also answer, saying, ‘Lord, when did we see you hungry, or thirsty, or a stranger, or naked, or sick, or in prison, and didn’t help you?’
45 Sa'annan zai amsa ya ce masu, 'Ina gaya maku hakika abin da baku iya yiwa mafi karanta daga cikin wadannan ba, ba ku yi mani ba.'
“Then he will answer them, saying, ‘Most certainly I tell you, because you didn’t do it to one of the least of these, you didn’t do it to me.’
46 Wadannan kuwa zasu tafi cikin madawwamiyar azaba amma adalai zuwa rai madawwami.” (aiōnios g166)
These will go away into eternal punishment, but the righteous into eternal life.” (aiōnios g166)

< Mattiyu 25 >