< Mattiyu 19 >

1 Sai ya zama sa'adda Yesu ya gama wadannan maganganu, sai ya bar Galili ya zo kan iyakokin Yahudiya, ketaren kogin Urdun.
Et il advint, lorsque Jésus eut terminé ces discours, qu'il s'éloigna de la Galilée et passa dans le territoire de la Judée, par l'autre côté du Jourdain.
2 Taro mai yawa suka bi shi, ya kuma warkar da su a wurin.
Et une foule nombreuse le suivit, et il les guérit en cet endroit.
3 Farisawa suka zo wurinsa, suna gwada shi, suka ce masa, ''Ya hallata bisa ga doka mutum ya saki matarsa don kowanne dalili?''
Et des pharisiens s'approchèrent de lui pour le mettre à l'épreuve, en disant: « Est-il permis de répudier sa femme pour quelque motif que ce soit? »
4 Yesu ya amsa ya ce, ''Baku karanta ba, cewa shi wanda ya yi su tun farko ya yi su miji da mace?
Et il répliqua: « N'avez-vous pas lu que Celui qui les créa à l'origine les fit mâle et femelle,
5 Shi wanda ya yi su kuma ya ce, “Saboda wannan dalilin, mutum zai rabu da mahaifinsa da mahaifiyarsa ya hade da matarsa, su biyun su zama jiki daya?”
et qu'il dit: « à cause de cela l'homme quittera son père et sa mère, et il s'unira étroitement à sa femme, et les deux deviendront une seule chair? »
6 Su ba biyu ba ne kuma, amma jiki daya. Don haka, duk abin da Allah ya hada, kada wani ya raba.''
En sorte qu'ils ne sont plus deux, mais une seule chair. Ainsi donc que ce que Dieu à conjoint, l'homme ne le sépare pas. »
7 Sai suka ce masa, ''To me yasa Musa ya umarcemu mu bada takardar saki, mu kuma kore ta?''
Ils lui disent: « Pourquoi donc Moïse a-t-il commandé de donner un acte de divorce et de la répudier? »
8 Sai ya ce masu, ''Saboda taurin zuciyarku, shi yasa Musa ya yarda maku ku saki matanku, amma da farko ba haka yake ba.
Il leur dit: « C'est à cause de votre dureté de cœur que Moïse vous a permis de répudier vos femmes; mais à l'origine cela ne s'est pas passé ainsi.
9 Ina gaya maku, duk wanda ya saki matarsa in ba saboda zina ba, ya kuma auri wata, yana zina kenan. Wanda kuma ya auri macen da aka saka, yana aikata zina.''
Pour moi, je vous le déclare: celui qui aura répudié sa femme, sauf pour cause d'impudicité, la pousse à commettre un adultère, et celui qui aura épousé une femme répudiée commet un adultère. »
10 Almajiran suka ce wa Yesu, ''Idan haka yake game da mutum da matarsa, ba kyau ayi aure ba.''
Les disciples lui disent: « Si telle est la relation de l'homme avec la la femme, il ne convient pas de se marier. »
11 Amma Yesu yace masu, ''Ba kowa ne zai karbi wannan koyarwa ba, amma sai wadanda an yardar masu su karbe ta.
Mais il leur dit: « Tous n'acquiescent pas à cette parole, mais seulement ceux auxquels cela est accordé;
12 Akwai wadanda aka haife su babanni. Akwai wadanda mutane ne suka maida su babanni. Sa'annan akwai wadanda sun mayar da kansu babanni saboda mulkin sama. Duk wanda zai iya karbar wannan koyarwa, ya karba.''
en effet, il y a des eunuques qui sont sortis tels du ventre de leur mère, et il y a des eunuques qui ont été mutilés par les hommes, et il y a des eunuques qui se sont mutilés eux-mêmes à cause du royaume des cieux. Que celui qui peut acquiescer, acquiesce. »
13 Sai aka kawo masa yara kanana don ya dibiya hannuwansa akansu, yayi masu addu'a, amma almajiran suka kwabe su.
Alors on lui amena de petits enfants, afin qu'il leur imposât les mains et qu'il priât; mais les disciples leur en firent des remontrances.
14 Amma Yesu ya ce masu, ''Ku bar yara kanana, kada ku hana su zuwa wuri na, domin mulkin sama na irinsu ne.''
Or Jésus dit: « Laissez ces petits enfants, et ne les empêchez pas de venir à moi, car c'est à ceux qui leur ressemblent qu'appartient le royaume des cieux. »
15 Ya sa hannuwa akan su, sa'annan ya bar wurin.
Puis, après leur avoir imposé les mains, il partit de là.
16 Sai wani mutum ya zo wurin Yesu, ya ce, ''Malam, wanne ayyuka nagari ne zan yi domin in sami rai madawwami?'' (aiōnios g166)
Et voici, quelqu'un s'étant approché de lui, dit: « Maître que dois-je faire de bon pour posséder la vie éternelle? » (aiōnios g166)
17 Yesu ya ce masa, ''Me yasa kake tambaya ta game da abin da ke nagari? Daya ne kawai ke nagari, amma idan kana so ka shiga cikin rai, ka kiyaye dokokin.''
Mais il lui dit: « Pourquoi m'interroges-tu sur ce qui est bon? Un seul est Le Bon; mais si tu veux entrer dans la vie, garde les commandements. »
18 Mutumin ya ce masa, ''Wadanne dokokin?'' Yesu ya ce masa, ''Kada kayi kisa, kada kayi zina, kada kayi sata, kada kayi shaidar zur,
Il lui dit: « Lesquels? » Or Jésus dit: « Ceux-ci: tu ne tueras point; tu ne commettras point d'adultère; tu ne déroberas point; tu ne feras point de faux témoignage;
19 ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka, kuma ka kaunaci makwabcinka kamar kanka.''
honore ton père et ta mère; tu aimeras ton prochain comme toi-même. »
20 Saurayin nan ya ce masa, ''Ai na kiyaye duk wadannan. Me nake bukata kuma?''
Le jeune homme lui dit: « J'ai observé toutes ces choses; que me manque-t-il encore? »
21 Yesu ya ce masa, ''Idan kana so ka zama cikakke, ka tafi ka sayar da mallakarka, ka kuma ba matalauta, zaka sami dukiya a sama. Sa'annan ka zo ka biyo ni.''
Jésus lui dit: « Si tu veux être parfait, va, vends tes biens, et donne-les aux pauvres, et tu auras un trésor dans les cieux, puis viens, suis-moi. »
22 Amma da saurayin nan ya ji abin da Yesu ya fada, ya koma da bakin ciki, domin shi mai arziki ne kwarai.
Mais le jeune homme, après avoir entendu ce discours, s'en alla tout triste; car il avait de grandes richesses.
23 Yesu ya ce wa almajiransa, ''Hakika ina gaya maku, zai zama da wuya mai arziki ya shiga mulkin sama.
Or Jésus dit à ses disciples: « En vérité, je vous déclare qu'un riche entrera difficilement dans le royaume des cieux.
24 Ina sake gaya maku, zai fi wa rakumi sauki ya shiga ta kafar allura, da mai arziki ya shiga mulkin Allah.''
Or je vous le déclare encore, il est plus facile qu'un chameau passe par un trou d'aiguille, qu'un riche n'entre dans le royaume de Dieu. »
25 Da almajiran sun ji haka, suka yi mamaki kwarai da gaske, suka ce, ''Wanene zai sami ceto?''
Ce que les disciples ayant ouï, ils étaient dans une grande stupéfaction, et ils disaient: « Qui donc peut être sauvé? »
26 Yesu ya dube su, ya ce, ''A wurin mutane wannan ba zai yiwu ba, amma a wurin Allah, kome mai yiwuwa ne.''
Mais Jésus, ayant fixé sur eux ses regards, dit: « Quant aux hommes cela est impossible, mais quant à Dieu tout est possible. »
27 Sai Bitrus ya amsa ya ce masa, ''Duba, mun bar kome da kome mun bi ka. To me za mu samu?''
Alors Pierre reprenant la parole lui dit: « Voici, pour nous, nous avons tout abandonné, et nous t'avons suivi; qu'avons-nous donc à attendre? »
28 Yesu ya ce masu, ''Hakika ina gaya maku, ku da kuka bi ni, a sabuwar haihuwa, lokacin da Dan Mutum ya zauna a kursiyin daukakarsa, ku ma zaku zauna a kursiyoyi goma sha biyu, kuna shari'anta kabilu goma sha biyu na Isra'ila.
Et Jésus leur dit: « En vérité, je vous déclare que vous qui m'avez suivi, lors du renouvellement, quand le fils de l'homme se sera assis sur le trône de sa gloire, vous aussi vous serez assis sur douze trônes pour juger les douze tribus d'Israël.
29 Duk wanda ya bar gidaje, 'yan'uwa maza, 'yan'uwa mata, mahaifi, mahaifiya, 'ya'ya, ko gonaki, saboda sunana, zai sami ninkin su dari, ya kuma gaji rai madawwami. (aiōnios g166)
Et quiconque a abandonné maisons, ou frères, ou sœurs, ou père, ou mère, ou enfants, ou champs, à cause de mon nom, recevra infiniment davantage, et il héritera la vie éternelle. (aiōnios g166)
30 Amma dayawa dake farko yanzu, za su zama na karshe, dayawa dake karshe kuma, su zama na farko.
Mais plusieurs, quoique des derniers, seront des premiers, et des derniers, quoique des premiers.

< Mattiyu 19 >