< Markus 14 >

1 Idin Ketarewa da bukin gurasa mara yisti sauran kwana biyu kenan, sai shugabanin firistoci da malaman attaura suka nemi yadda zasu kama Yesu a asirce domin su kashe shi.
erat autem pascha et azyma post biduum et quaerebant summi sacerdotes et scribae quomodo eum dolo tenerent et occiderent
2 Suna cewa amma “Ba a lokacin idin ba, domin kada su haddasa hargitsi a tsakanin mutane”.
dicebant enim non in die festo ne forte tumultus fieret populi
3 Yesu yana Betanya a gidan Saminu kuturu, yana shirin liyafa kenan sai ga wata mace dauke da kwalbar turare mai tamanin kwarai, ta shafa masa a kansa.
et cum esset Bethaniae in domo Simonis leprosi et recumberet venit mulier habens alabastrum unguenti nardi spicati pretiosi et fracto alabastro effudit super caput eius
4 wasu dake tare da Yesu suka husata, suna kwalbarta da cewa
erant autem quidam indigne ferentes intra semet ipsos et dicentes ut quid perditio ista unguenti facta est
5 “Ai wannan turare ne mai tsada, ina laifin a sayar a raba wa talakawa kudin? ina dalilin wannan almubazaranci?
poterat enim unguentum istud veniri plus quam trecentis denariis et dari pauperibus et fremebant in eam
6 Sai Yesu yace masu “Ku kyaleta, don me kuke tsauta mata,
Iesus autem dixit sinite eam quid illi molesti estis bonum opus operata est in me
7 ai Idan kuna da niyyar taimakon talakawa ko matalauta, suna nan tare da ku ko a yaushe amma ni bazan kasance da ku kullum ba.
semper enim pauperes habetis vobiscum et cum volueritis potestis illis benefacere me autem non semper habetis
8 Macen nan tayi aiki nagari domin shirya jikina ga jana'iza.
quod habuit haec fecit praevenit unguere corpus meum in sepulturam
9 hakika, Ina gaya maku, duk inda za'a yi bishara a duniya baza a mance da matan nan da hidimar da ta tayi mini ba.”
amen dico vobis ubicumque praedicatum fuerit evangelium istud in universum mundum et quod fecit haec narrabitur in memoriam eius
10 Da jin haka sai Yahuza Iskariyoti, daya daga cikin manzannin ya ruga zuwa wurin baban firist domin ya bashe shi a garesu,
et Iudas Scariotis unus de duodecim abiit ad summos sacerdotes ut proderet eum illis
11 Da mayan firistoci suka ji haka suka yi murna matuka tare da alkawarin kudi ga Yahuza, shi kuwa sai ya fara neman zarafin da zai mika Yesu a gare su.
qui audientes gavisi sunt et promiserunt ei pecuniam se daturos et quaerebat quomodo illum oportune traderet
12 A ranar farko ta bukin gurasa marar yisti da kuma hadayar ragon Idin ketarewa, almajiransa suka ce masa “Ina zamu shirya liyafar domin idin ketarewa?
et primo die azymorum quando pascha immolabant dicunt ei discipuli quo vis eamus et paremus tibi ut manduces pascha
13 Ya aiki biyu daga cikin almajiransa da cewa “Ku shiga cikin birnin, zaku tarar da wani mutum dauke da tullun ruwa.
et mittit duos ex discipulis suis et dicit eis ite in civitatem et occurret vobis homo laguenam aquae baiulans sequimini eum
14 Duk gidan da ya shiga ku bishi, sai ku cewa mai gidan, malam yace “ina bukatar masauki domin hidimar idin ketarewa tare da almajiraina?”'
et quocumque introierit dicite domino domus quia magister dicit ubi est refectio mea ubi pascha cum discipulis meis manducem
15 Zai kuwa nuna maku babban bene gyararre. Sai ku yi mana shiri a can.”
et ipse vobis demonstrabit cenaculum grande stratum et illic parate nobis
16 Da shigar almajiran cikin birnin, sai kome ya kasance yadda ya fada, su kuwa suka yi shirye shiryen idin ketarewar.
et abierunt discipuli eius et venerunt in civitatem et invenerunt sicut dixerat illis et praeparaverunt pascha
17 Da maraice ta yi, sai ya tare da sha biyun.
vespere autem facto venit cum duodecim
18 Yayin da suke zazzaune a teburin suna cin abincin, sai Yesu ya ce “Hakika ina gaya maku wani da ke ci tare da ni a nan zai bashe ni”.
et discumbentibus eis et manducantibus ait Iesus amen dico vobis quia unus ex vobis me tradet qui manducat mecum
19 Sai suka damu suka tambaye shi daya bayan daya suna cewa “Hakika bani bane ko?”
at illi coeperunt contristari et dicere ei singillatim numquid ego
20 Yesu ya amsa masu da cewa “Daya daga cikin sha biyu ne, wanda ke sa hannu tare da ni yanzu cikin tasar”.
qui ait illis unus ex duodecim qui intinguit mecum in catino
21 Dan Mutum zai tafi ne yadda nassi ya umarta game da shi amma kaiton wanda zai bashe shi! “zai, fiye masa, dama ba a haife shi ba”.
et Filius quidem hominis vadit sicut scriptum est de eo vae autem homini illi per quem Filius hominis traditur bonum ei si non esset natus homo ille
22 Lokacin da suke cin abincin, Yesu ya dauki gurasa ya sa albarka, ya gutsuttsura ta, sai ya basu yana cewa “Wannan jikinana ne”.
et manducantibus illis accepit Iesus panem et benedicens fregit et dedit eis et ait sumite hoc est corpus meum
23 Ya kuma dauki koko, yayi godiya, ya basu, su kuwa suka sha daga kokon.
et accepto calice gratias agens dedit eis et biberunt ex illo omnes
24 Ya ce “Wannan jinina ne na alkawari da an zubar ga yawancin mutane”.
et ait illis hic est sanguis meus novi testamenti qui pro multis effunditur
25 Hakika, bazan kara sha daga wannan ruwan inabi ba sai a ranar da zan sha sabo cikin mulkin Allah.”
amen dico vobis quod iam non bibam de genimine vitis usque in diem illum cum illud bibam novum in regno Dei
26 Bayan sun raira wakar yabo ga Allah, sai suka tafi wurin dutsen zaitun.
et hymno dicto exierunt in montem Olivarum
27 Yesu ya ce masu dukkan ku zaku yi tuntube harma ku fadi saboda ni gama rubuce take cewa “Zan buge makiyayin, tumakin kuwa za su watse;
et ait eis Iesus omnes scandalizabimini in nocte ista quia scriptum est percutiam pastorem et dispergentur oves
28 Amma bayan tashina, zai yi gaba in riga ku zuwa Galili.
sed posteaquam resurrexero praecedam vos in Galilaeam
29 Bitrus ya ce masa “ko dukkansu sun fadi, faufau banda ni”.
Petrus autem ait ei et si omnes scandalizati fuerint sed non ego
30 Yesu yace masa “Hakika ina gaya maka, cikin wannan dare kafin carar zakara ta biyu zaka yi musun sani na sau uku”.
et ait illi Iesus amen dico tibi quia tu hodie in nocte hac priusquam bis gallus vocem dederit ter me es negaturus
31 Amma Bitrus ya sake cewa “Koda za'a kasheni tare da kai ba zan yi musun sanin ka ba”. Dukkan su kuwa suka yi wannan Alkawari.
at ille amplius loquebatur et si oportuerit me simul conmori tibi non te negabo similiter autem et omnes dicebant
32 Suka isa wani wuri da ake kira Getsamani, sai Yesu ya ce wa almajiransa “Ku dakata anan domin zan je inyi addu'a”.
et veniunt in praedium cui nomen Gethsemani et ait discipulis suis sedete hic donec orem
33 Sai ya dauki Bitrus, da Yakubu, da Yahaya. Ya fara jin wahala mutuka tare da damuwa kwarai.
et adsumit Petrum et Iacobum et Iohannem secum et coepit pavere et taedere
34 Sai ya ce masu “Raina na shan wahala harma kamar in mutu. Ku dakata a nan, ku zauna a fadake”.
et ait illis tristis est anima mea usque ad mortem sustinete hic et vigilate
35 Da Yesu yayi gaba kadan, sai ya fadi kasa yayi addu'a yana cewa idan mai yiwuwa ne “A dauke masa wannan sa'a daga gare shi.
et cum processisset paululum procidit super terram et orabat ut si fieri posset transiret ab eo hora
36 Ya ce “Ya Abba Uba, kome mai yuwane gare ka, ka dauke mini kokon wahalan nan, duk da haka ba nufina ba sai dai naka”.
et dixit Abba Pater omnia possibilia tibi sunt transfer calicem hunc a me sed non quod ego volo sed quod tu
37 Da komowarsa ya same su suna barci, sai ya ce wa Bitrus, Siman barci kake? Ashe, ba za ka iya zama a fadake ko da sa'a daya ba?
et venit et invenit eos dormientes et ait Petro Simon dormis non potuisti una hora vigilare
38 Ku zauna a fadake, kuyi addu'a kada ku fada cikin jaraba. Lalle ruhu na da niyya amma jiki raunana ne.
vigilate et orate ut non intretis in temptationem spiritus quidem promptus caro vero infirma
39 Sai ya sake komawa, yayi addu'a, yana maimaita kalmominsa na farko.
et iterum abiens oravit eundem sermonem dicens
40 Har wa yau kuma ya sake dawowa, ya same su suna barci don barci ya cika masu idanu kwarai, sun kuwa kasa ce masa kome.
et reversus denuo invenit eos dormientes erant enim oculi illorum ingravati et ignorabant quid responderent ei
41 Ya sake komowa karo na uku yace masu “har yanzu barci kuke yi kuna hutawa? Ya isa haka! Lokaci yayi, an bada Dan Mutum ga masu zunubi”.
et venit tertio et ait illis dormite iam et requiescite sufficit venit hora ecce traditur Filius hominis in manus peccatorum
42 Ku tashi mutafi kun ga, ga mai bashe ni nan ya kusato.”
surgite eamus ecce qui me tradit prope est
43 Nan da nan, kafin ya rufe baki sai ga Yahuza, daya daga cikin sha biyun da taron jama'a rike da takkuba da kulake. Manyan firistoci da malaman attaura da shugabanni suka turo su.
et adhuc eo loquente venit Iudas Scarioth unus ex duodecim et cum illo turba cum gladiis et lignis a summis sacerdotibus et a scribis et a senioribus
44 Mai bashe shi din nan ya riga ya kulla da su cewa “Wanda zan yi wa sumba shine mutumin, ku kama shi ku tafi da shi a tsare.
dederat autem traditor eius signum eis dicens quemcumque osculatus fuero ipse est tenete eum et ducite
45 Da isowarsa kuwa, sai ya zo wurin Yesu ya ce “Ya malam!”. Sai ya sumbace shi.
et cum venisset statim accedens ad eum ait rabbi et osculatus est eum
46 Su kuwa suka kama shi, suka tafi da shi.
at illi manus iniecerunt in eum et tenuerunt eum
47 Amma daya daga cikin na tsaye ya zaro takobinsa ya kai wa bawan babban firist sara, ya yanke masa kunne.
unus autem quidam de circumstantibus educens gladium percussit servum summi sacerdotis et amputavit illi auriculam
48 Sai Yesu ya ce “kun fito kamar masu kama yan fashi da takkuba da kulake, domin ku kama ni?
et respondens Iesus ait illis tamquam ad latronem existis cum gladiis et lignis conprehendere me
49 Lokacin da nake koyarwa a Haikali, kowace rana da ku, baku kama ni ba. Amma anyi haka ne domin a cika abinda Nassi ya fada.”
cotidie eram apud vos in templo docens et non me tenuistis sed ut adimpleantur scripturae
50 Daga nan duk wadanda suke tare da Yesu suka yashe shi, suka tsere.
tunc discipuli eius relinquentes eum omnes fugerunt
51 Wani saurayi, daga shi sai mayafi ya bi shi, suka kai masa cafka.
adulescens autem quidam sequebatur illum amictus sindone super nudo et tenuerunt eum
52 Shi kuwa ya bar masu mayafin ya gudu tsirara.
at ille reiecta sindone nudus profugit ab eis
53 Daga nan suka tafi da Yesu wurin babban firist. a can suka tara dattawa duk da manyan firistoci da shugabanni da marubuta, suka taru a wurinsa.
et adduxerunt Iesum ad summum sacerdotem et conveniunt omnes sacerdotes et scribae et seniores
54 Bitrus kuwa ya bi shi daga nesa har cikin gidan babban firist. Ya zauna tare da dogaran Haikalin, yana jin dumin wuta.
Petrus autem a longe secutus est eum usque intro in atrium summi sacerdotis et sedebat cum ministris et calefaciebat se ad ignem
55 Sai, manyan firistoci da duk 'yan majalisa Yahudawa suka nemi shaidar da za a tabbatar a kan Yesu, don su samu su kashe shi. Amma basu samu ba.
summi vero sacerdotes et omne concilium quaerebant adversum Iesum testimonium ut eum morti traderent nec inveniebant
56 Da yawa kuma suka yi masa shaidar Zur (Karya), amma bakin su bai zama daya ba.
multi enim testimonium falsum dicebant adversus eum et convenientia testimonia non erant
57 Sai wadansu kuma suka taso suka yi masa shaidar zur (karya) suka ce.
et quidam surgentes falsum testimonium ferebant adversus eum dicentes
58 “Mun ji ya ce, wai zai rushe haikalin nan da mutane suka gina, ya sake gina wani cikin kwana uku, ba kuwa ginin mutum ba”.
quoniam nos audivimus eum dicentem ego dissolvam templum hoc manufactum et per triduum aliud non manufactum aedificabo
59 Duk da haka, sai shaidar tasu bata zo daya ba.
et non erat conveniens testimonium illorum
60 Sai babban firist ya mike a tsakanin su, ya tambayi Yesu yace “Ba ka da wata amsa game da shaidar da mutanen nan suke yi a kanka?
et exsurgens summus sacerdos in medium interrogavit Iesum dicens non respondes quicquam ad ea quae tibi obiciuntur ab his
61 Amma yayi shiru abinsa, bai ce kome ba. Sai babban firist din ya sake tambayarsa “To, ashe kai ne Allmasihu Dan Madaukaki?
ille autem tacebat et nihil respondit rursum summus sacerdos interrogabat eum et dicit ei tu es Christus Filius Benedicti
62 Yesu ya ce “Nine. Za ku kuwa ga Dan Mutum zaune dama ga mai iko, yana kuma zuwa cikin gajimare”.
Iesus autem dixit illi ego sum et videbitis Filium hominis a dextris sedentem Virtutis et venientem cum nubibus caeli
63 Sai babban firist ya kyakketa tufafinsa yace “Wacce shaida kuma zamu nema?
summus autem sacerdos scindens vestimenta sua ait quid adhuc desideramus testes
64 Kun dai ji sabon da yayi! Me kuka gani? Duk suka yanke masa hukunci akan ya cancanci kisa.
audistis blasphemiam quid vobis videtur qui omnes condemnaverunt eum esse reum mortis
65 Wadansu ma suka fara tottofa masa yau, suka daure masa idanu, suka bubbuge shi suna cewa “Yi annabci” Dogaran kuma suka yi ta marinsa.
et coeperunt quidam conspuere eum et velare faciem eius et colaphis eum caedere et dicere ei prophetiza et ministri alapis eum caedebant
66 Bitrus kuwa na kasa a filin gida, sai wata baranyar babban firist ta zo.
et cum esset Petrus in atrio deorsum venit una ex ancillis summi sacerdotis
67 Da ta ga Bitrus na jin dumi, ta yi masa kallon gaske ta ce “Kaima ai tare kake da banazaren nan Yesu”.
et cum vidisset Petrum calefacientem se aspiciens illum ait et tu cum Iesu Nazareno eras
68 Amma ya musa ya ce “Ni ban ma san abinda kike fada ba balle in fahimta”. Sai ya fito zaure. Sai zakara yayi cara.
at ille negavit dicens neque scio neque novi quid dicas et exiit foras ante atrium et gallus cantavit
69 Sai baranyar ta ganshi, ta sake ce wa wadanda ke tsaitsaye a wurin, “Wannan ma daya daga cikinsu ne”.
rursus autem cum vidisset illum ancilla coepit dicere circumstantibus quia hic ex illis est
70 Amma ya sake musawa, jim kadan sai na tsaitsayen suka ce wa Bitrus “Lalle kai ma dayansu ne don ba Galile ne kai”.
at ille iterum negavit et post pusillum rursus qui adstabant dicebant Petro vere ex illis es nam et Galilaeus es
71 Sai ya fara la'anta kansa yana ta rantsuwa yana ce wa “Ban ma san mutumin nan da kuke fada ba”.
ille autem coepit anathematizare et iurare quia nescio hominem istum quem dicitis
72 Nan da nan sai zakara ya yi cara ta biyu, Bitrus kuwa ya tuna da maganar Yesu a gare shi cewa “Kafin zakara ya yi cara ta biyu, za ka yi musun sani na sau uku”. Da ya tuno haka, sai ya fashe da kuka.
et statim iterum gallus cantavit et recordatus est Petrus verbi quod dixerat ei Iesus priusquam gallus cantet bis ter me negabis et coepit flere

< Markus 14 >