< Luka 8 >

1 Bayan haka, Yesu da almajiransa goma sha biyu, su ka zagaya cikin birane da kauyuka dabam dabam, suna wa'azi da shelar labari mai dadi game da mulkin Allah,
It happened soon afterward that Jesus began traveling around to different cities and villages, preaching and proclaiming the good news about the kingdom of God. The twelve were with him,
2 mata da yawa wadanda Yesu ya warkar daga aljanu da cututtuka iri iri suna tafiya tare da su. A cikinsu akwai Maryamu wadda a ke ce da ita Magadaliya, wadda ya fitar da aljanu bakwai daga cikinta,
as well as certain women who had been healed of evil spirits and diseases: Mary who was called Magdalene, from whom seven demons had been driven out;
3 da Yuwana matar Kuza wakilin Hirudus, da Suzanatu da kuma wasu mata da yawa. Daga abin hannunsu suka tanada masu.
Joanna, the wife of Chuza, Herod's manager; Susanna; and many others, who, out of their possessions, provided for their needs.
4 Wata rana aka tara taron mutane da yawa, saboda mutane su na zuwa daga birane da yawa domin su ga Yesu. Ya yi magana dasu cikin misali.
While a large crowd of people was gathering, and people were coming to him from town after town, he told a parable:
5 “Wani mai shuka ya tafi domin ya shuka iri. Sa'adda ya ke yafa iri, wadansu iri suka fada a kan hanya. Sai mutane suka tattake su, tsuntsaye kuma suka tsince wadansu suka cinye.
“A farmer went out to sow his seed. As he sowed, some fell beside the road and it was trampled underfoot, and the birds of the sky devoured it.
6 Wadansu kuma suka fada a kan duwatsu inda babu kasa da yawa. Da suka tsaro suka fara girma, sai nan da nan suka bushe saboda babu laima a wurin.
Some fell on the rock, and as soon as it grew up, it withered away, because it had no moisture.
7 Wadansu irin kuma suka fada inda yake da kayayuwa. Tsiretsiren kayayuwan suka fito tare da irin da aka shuka, suka shake su yadda basu iya yin girma ba.
Some fell among thorns, and the thorns grew up together with the seed and choked it.
8 Amma wadansu irin suka fada a kan kasa mai kyau, suka yi girma sosai suka ba da anfani da yawa, har rubi dari.” Bayan da Yesu ya fadi wadannan abubuwan, sai ya yi kira gare su, “Duk mai kunnen ji, bari ya ji.”
But some fell on good soil and produced a crop that was a hundred times greater.” After Jesus had said these things, he called out, “Whoever has ears to hear, let him hear.”
9 Sai almajiran Yesu suka tambaye shi ya gaya ma su ma'anar labarin.
His disciples asked him what this parable meant.
10 ya ce da su, “Ku aka ba dama ku gane boyayyun abubuwa, na mulkin Allah. Amma ga sauran mutane ina yi masu magana cikin misalai, 'Domin ko da sun gani ba za su gane ba, kuma ko da sun ji ba za su fahimta ba.”
He said, “The knowledge of the secrets of the kingdom of God has been given to you, but for others I speak in parables, so that 'seeing they may not see, and hearing they may not understand.'
11 To ga ma'anar misalin. Irin shi ne maganar Allah.
Now this is the meaning of the parable: The seed is the word of God.
12 Irin da ya fada a kan hanya sune mutanen da suka ji maganar Allah amma daga baya sai shedan ya zo ya dauke maganar daga cikin hankulansu, domin kada su bada gaskiya su tsira.
The ones along the path are those who have heard, but then the devil comes and takes away the word from their hearts, so they may not believe and be saved.
13 Sa'annan, wadanda suka fada kan duwatsu sune mutanen da, da zarar sun ji maganar, sukan karbe ta da murna, amma ba su da sauyu; su kan bada gaskiya na dan lokaci kadan kawai, da zaran gwaji ya same su sai su ridda.
The ones on the rock are those who, when they hear the word, receive it with joy. But they have no root; they believe for a while, and in a time of testing they fall away.
14 Irin da suka fada cikin kayayuwa, sune mutanen da suka ji maganar, amma da suka ci gaba da rayuwa, sai suka bari matsalolin rayuwa kamar dukiya da jin dadin rayuwa suka fi karfinsu, sai ya zama ba su iya bada 'ya'yan da suka yi girma ba.
The seeds that fell among the thorns are people who hear the word, but as they go on their way, they are choked by the cares and riches and pleasures of this life, and their fruit does not mature.
15 Amma irin da suka fada a kan kasa mai kyau, wadannan sune mutanen da suka ji maganar, suka karbe ta da gaskiya da zuciya daya, sun rike ta kam-kam, suna jimrewa wurin ba da 'ya'ya.
But the seed that fell on the good soil, these are the ones who, hearing the word with an honest and good heart, hold it securely and bear fruit with patient endurance.
16 Ba mai kunna fitila, ya rufe ta da kasko, ko su sa ta a karkashin gado. Amma sai a sa ta a wurin zaman ta domin duk wanda ya shigo ya iya ganin hasken ta.
No one lights a lamp and covers it with a bowl or puts it under a bed. Rather, he puts it on a lampstand so that everyone who enters may see the light.
17 Babu abin da yake a boye wanda ba za a tone shi ba, ko wani asiri da ba za ya fito fili a san shi ba.
For nothing is hidden that will not be made known, nor is anything secret that will not be known and come into the light.
18 Ku yi hankali da yadda kuke ji, domin duk mai abu, shi za a kara wa, kuma duk mara abu, dan kadan da yake tunani yana da shi ma, za a dauke.”
So listen carefully, for to the one who has, more will be given to him, but the one who does not have, even what he thinks he has will be taken away from him.”
19 Sai mahafiyar Yesu da 'yan'uwansa, su ka zo wurinsa, amma ba su iya zuwa ko kusa da shi ba saboda taron jama'a.
Then his mother and brothers came to him, but they could not get near him because of the crowd.
20 Sai wani ya gaya masa, “Ga mahaifiyarka da 'yan'uwanka, su na tsayuwa a waje, su na son ganin ka.”
He was told, “Your mother and your brothers are standing outside, wanting to see you.”
21 Amma Yesu ya amsa ya ce ma su, “Mahaifiyata da 'yan'uwana sune wadanda suke jin maganar Allah, suke yin biyayya da ita.”
But Jesus answered and said to them, “My mother and my brothers are those who hear the word of God and do it.”
22 Wata rana kuma Yesu ya shiga cikin jirgin ruwa, shi da almajiransa. Ya ce masu, “Ina so mu je dayan ketaren tafkin.” Sai su ka fara tafiya domin su ketare tafkin.
Now one day he got into a boat with his disciples, and he said to them, “Let us go over to the other side of the lake.” They set sail.
23 Amma sa'adda su ke tafiya sai Yesu ya yi barci, sai wata iska mai karfi ta taso cikin tafkin, nan da nan sai jirgin ya fara cika da ruwa, kuma su na cikin hatsari.
But as they sailed he fell asleep. A terrible windstorm came down on the lake, and their boat was filling with water, and they were in danger.
24 Sai almajiran Yesu su ka zo su ka tashe shi daga barci. Suka ce da shi, “Ya Shugaba! Ya Shugaba! Za mu mutu!” Sai ya tashi ya umarci iskar, sai iskar mai hauka da tumbatsar ruwan sun tsaya tsit.
Then Jesus' disciples came over to him and woke him up, saying, “Master! Master! We are about to die!” He awoke and rebuked the wind and the raging of the water, and they ceased, and there was a calm.
25 Daga nan sai ya ce da su, “Ina bangaskiyar ku?” Almajiran suka tsorata suka yi mamakin abin da ya faru nan take. Suka ce wa junansu, “Wanene wannan wanda har zai ba iska da ruwa umarni kuma su yi masa biyayya?”
Then he said to them, “Where is your faith?” and they were afraid. While they were afraid they were also amazed, and they asked one another, “Who then is this, that he commands even the winds and the water, and they obey him?”
26 Suka zo yankin Garasinawa, wanda ke kusa da Gallili.
They sailed to the region of the Gerasenes, which is across the lake from Galilee.
27 Sa'adda Yesu ya sauka kasa, sai wani mutum daga wannan yankin ya tarbe shi. Wannan mutum kuwa yana da aljanu. Mutumin ya dade ba ya sa tufafi, kuma ba ya zama a gida. Maimakon haka, sai a cikin kabarbura ya ke zama.
When Jesus stepped on the land, he was met by a certain man from the city who had demons. For a long time he had worn no clothes, and he did not live in a house but among the tombs.
28 Sa'adda ya ga Yesu, mutumin ya yi ihu da karfi, ya rusuna a gabansa da babban murya ya ce, “Me zan yi da kai, Yesu, Dan Allah Madaukaki? Ina rokonka, kada ka ba ni azaba!”
When he saw Jesus, he cried out and fell down before him and he said with a loud voice, “What have you to do with me, Jesus, Son of the Most High God? I beg you, do not torment me.”
29 Domin Yesu ya umarci aljanun su fita daga cikinsa, domin sau da dama aljanun sukan kama shi. Ko an daure mutumin da sarkoki an kuma tsare shi, yakan tsuttsunke su, kazaman ruhohin sukan kora shi cikin jeji.
For Jesus had commanded the unclean spirit to come out of the man. For many times it had seized him, and though he was bound with chains and shackles and kept under guard, he had broken his chains and he would be driven by the demon into the wilderness.
30 Sa'annan Yesu ya tambaye shi, “Yaya sunanka?” Sai ya ba da amsa, “Suna na dubbai.” Ya ce haka ne domin aljanu da yawa sun shiga wannan mutum.
Then Jesus asked him, “What is your name?” and he said, “Legion,” for many demons had entered into him.
31 Aljanun suka yi ta rokon Yesu kada ya ummarce su su shiga cikin rami mai zurfi. (Abyssos g12)
They kept begging him not to send them into the abyss. (Abyssos g12)
32 Akwai babban garken aladu su na kiwo a kan tsauni kusa da wurin. Aljanun suka roki Yesu da ya barsu su shiga cikin aladun, shi kuwa ya yarda masu.
Now a large herd of pigs was there feeding on the hillside. The demons begged him to let them go into them, and he gave them permission.
33 Aljanun suka bar mutumin suka shiga cikin aladun, sai garken aladun suka gangara kwari suka fada cikin tafkin, suka nutse.
So the demons came out of the man and went into the pigs, and the herd rushed down the steep slope into the lake and was drowned.
34 Lokacin da mutanen da su ke kiwon aladun suka ga abin da ya faru, sai suka gudu! Suka ba da rahoton abin da ya faru ga mutanen cikin gari da na wannan kewayen.
When those tending the pigs saw what had happened, they ran off and told about it in the city and countryside.
35 Don haka, mutanen da suka ji haka suka tafi domin su ga abin da ya faru, suka zo wurin da Yesu yake, suka ga mutumin wanda aljanu suka fita daga cikinsa. Suka ga ya na sanye da tufafi, kuma ya na cikin hankalinsa, sai tsoro ya kama su.
So the people went out to see what had happened, and they came to Jesus and found the man from whom the demons had gone out. He was sitting at the feet of Jesus, clothed and in his right mind; and they were afraid.
36 Mutanen da suka ga abin da ya faru, suka gaya wa wadansu yadda aka warkar da mutumin da aljanu suke iko da shi.
Then those who had seen it told them how the man who had been possessed by demons had been healed.
37 Sai dukan mutane wadanda suke cikin yankin Garasinawa da wadanda suke kewaye, suka roki Yesu da ya fita daga cikin yankin kasarsu domin sun ji tsoro kwarai da gaske. Daga nan Yesu da almajiransa suka shiga cikin jirgin ruwa suka koma.
Then all the people of the region of the Gerasenes asked Jesus to depart from them, for they were overwhelmed with great fear. So he got into the boat so they could start back.
38 Mutumin wanda aljanu suka fita daga cikinsa, ya roki Yesu cewa, “Ka barni in tafi tare da kai!” Amma Yesu ya sallame shi cewa,
The man from whom the demons had gone out begged him to let him go with him, but Jesus sent him away, saying,
39 “Ka koma gida ka gaya wa mutanen ka abubuwa masu girma wadanda Allah ya yi maka.” Daga nan sai mutumin ya tafi yana ta gayawa dukan mutanen birnin game da abubuwan da Yesu ya yi masa.
“Return to your home and give a full account of what God has done for you.” The man went on his way, proclaiming throughout the whole city what Jesus had done for him.
40 Sa'adda Yesu ya dawo, mutanen suka marabce shi, gama, dukansu suna jiransa.
Now when Jesus returned, the crowd welcomed him, for they were all expecting him.
41 Sai ga wani mutum mai suna Yayirus, daya daga cikin shugabannin majami'a, ya zo kusa da Yesu ya rusuna da kansa a kasa. Ya roke shi domin ya zo gidansa,
Behold, a man named Jairus, who was one of the leaders of the synagogue, came and fell down at Jesus' feet, and he begged him to come to his house,
42 saboda diyarsa mai kimanin shekara goma sha biyu ta na bakin mutuwa, kuma ita kadai ce diya a gare shi. Amma sa'adda yake tafiya, taron mutane da yawa suna matsa shi.
because his only daughter, a girl of about twelve years of age, was dying. As Jesus was on his way, the crowds of people pressed together around him.
43 Akwai wata mace a nan wadda take zubar jini har shekara goma sha biyu. Ta kashe kudinta duka a wurin likitoci, domin su warkar da ita amma ba wanda ya iya warkar da ita.
Now a woman was there who had been bleeding for twelve years and had spent all her money, and could not be healed by anyone.
44 Sai ta biyo ta bayan Yesu ta taba habar rigarsa. Nan take sai zubar jinin ya tsaya.
She came behind Jesus and touched the edge of his coat, and immediately her bleeding stopped.
45 Yesu ya ce, “Wanene ya taba ni?” Wadanda suke kewaye da shi, kowa ya ce bai taba shi ba, Bitrus ya ce, “Shugaba, mutane da yawa suna ta taruwa kewaye da kai suna ta matsowa kusa da kai.”
Jesus said, “Who was it who touched me?” When all denied it, Peter said, “Master, the crowds of people are all around you and they are pressing in against you.”
46 Amma Yesu ya ce, “Na sani, wani ya taba ni, domin iko ya fita daga wurina.”
But Jesus said, “Someone did touch me, for I know that power has gone out from me.”
47 Sa'adda matar ta gane cewa ba za ta iya boyewa ba, sai ta zo wurinsa cikin tsoro. Ta durkusa a gaban Yesu, ta fada a gaban dukan jama'a dalilin da ya sa ta taba shi kuma nan da nan ta warke.
When the woman saw that she could not escape notice, she came trembling and fell down before him. In the presence of all the people she declared why she had touched him and how she had been immediately healed.
48 Sai ya ce da ita, “Diya, bangaskiyarki ta warkar da ke. Tafi cikin salama.”
Then he said to her, “Daughter, your faith has made you well. Go in peace.”
49 Yana cikin yin magana, wani daga cikin gidan shugaban majami'ar ya zo, ya ce, “Diyarka ta riga ta mutu, kada ka dami malam.”
While he was still speaking, someone came from the synagogue leader's house, saying, “Your daughter is dead. Do not trouble the teacher any longer.”
50 Amma sa'adda Yesu ya ji haka, sai ya ce da shi, “Kada ka ji tsoro. Ka bada gaskiya za ta rayu.”
But when Jesus heard this, he answered Jairus, “Do not be afraid; only believe, and she will be healed.”
51 Sa'adda ya zo gidan, bai bar kowa ya shiga gidan tare da shi ba sai Bitrus da Yahaya da Yakubu, da mahaifiyar yarinyar da babanta.
When he came to the house, he allowed no one to enter with him, except Peter and John and James, and the father of the child and her mother.
52 Dukan mutane a wurin, suna ta kuka da karfi saboda sun damu da yarinyar ta mutu. Amma Yesu ya ce da su, “Ku dena kuka! Ba mutuwa ta yi ba! Barci ta ke yi kawai!”
Now all were mourning and wailing for her, but he said, “Do not weep; she is not dead but asleep.”
53 Mutanen suka yi ma sa dariyan reni, saboda sun sani yarinyar ta mutu.
But they laughed at him, knowing that she was dead.
54 Amma ya kama hannun ta yayi kira cewa, “Yarinya, na ce ki tashi!”
But he took her by the hand and called out, saying, “Child, get up!”
55 Nan da nan ruhun ta ya dawo jikin ta sai ta tashi. Ya ce masu su ba ta wani abu ta ci.
Her spirit returned, and she rose up immediately. He ordered them to get her something to eat.
56 Iyayenta suka yi mamaki, amma Yesu ya ce da iyayen kada su gaya wa kowa abin da ya faru.
Her parents were astonished, but he ordered them to tell no one what had happened.

< Luka 8 >