< Luka 24 >

1 Da sassafe a ranar farko ta mako, suka zo kabarin, suka kawo kayan kamshi wadda suka shirya.
Mais le premier jour de la semaine, de très grand matin, elles se rendirent au tombeau, portant avec elles les aromates qu'elles avaient préparés.
2 Sai suka samu dutsen a mirgine shi daga kabarin.
Elles s'aperçurent que la pierre avait été éloignée de l'ouverture du sépulcre.
3 Suka shiga ciki, amma ba su sami jikin Ubangiji Yesu ba.
Elles entrèrent et ne trouvèrent pas le corps du Seigneur Jésus.
4 Ya faru kuwa, yayin da suke a rikice game da wannan, ba zato, mutane guda biyu suka tsaya a gabansu da tufafi masu walkiya.
Elles en étaient consternées; mais voilà que deux hommes se présentèrent à elles, vêtus de robes resplendissantes.
5 Sa'adda matan suka sunkuyar da kansu kasa domin tsoro, suka ce wa matan, “Don me kuke neman mai rai ciki matattatu?
Et comme, tout effrayées, elles inclinaient leurs visages vers la terre, ils leur dirent: «Pourquoi cherchez-vous parmi les morts celui qui est vivant?
6 Baya nan, amma ya tashi! Ku tuna fa yadda ya yi maku magana tun sa'adda ya ke Galili,
Il n'est pas ici; tout au contraire, il est ressuscité. Souvenez-vous comment il vous a parlé quand il était encore en Galilée.
7 cewa za a ba da Dan Mutum ga mutane masu zunubi su kuma giciye shi, a rana ta uku, zai tashi kuma”
Il faut, disait-il, que le Fils de l'homme soit livré entre les mains des pécheurs, qu'il soit crucifié et qu'il ressuscite le troisième jour.»
8 Sai matan suka tuna da kalmominsa,
Elles se souvinrent alors de ses paroles.
9 suka koma daga kabarin sai suka gaya wa sha dayan wadannan abubuwan da dukan sauran.
De retour du tombeau, elles annoncèrent tout cela aux onze et à tous les autres.
10 Su Maryamu Magadaliya, Yuwana, Maryamu uwar Yakubu, da sauran matan da ke tare da su suka ba manzanni rohoton wadannan abubuwan.
C'étaient Marie Magdeleine, Jeanne, Marie mère de Jacques, et quelques autres avec elles qui racontèrent cela aux apôtres.
11 Amma manzannin suka dauki maganar kamar ba ta da amfani, kuma ba su bada gaskiya ga matan ba.
Et leurs dires leur firent l'effet d'une absurdité et ils ne les crurent pas.
12 Duk da haka Bitrus ya tashi, sai ya gudu zuwa kabarin, ya sunkuya yana kallon ciki, sai ya gan likaftani linin kadai. Sa'annan Bitrus ya tafi gidansa, yana ta mamakin abinda ya faru.
(Pierre, cependant, se leva et courut au sépulcre. S’étant baissé, il ne vit que des linges qui étaient à terre, puis il retourna chez lui, surpris de ce qui était arrivé.)
13 A ranan nan, sai ga biyu daga cikinsu suna tafiya zuwa wani kauye suna Imawus, wanda nisansa kimanin mil ne daga Urushalima.
Ce même jour, deux d'entre les disciples s'en allaient à un village situé à soixante stades de Jérusalem, nommé Emmaüs,
14 Suna tattaunawa da junansu game da dukan abubuwan da suka faru.
et ils s'entretenaient ensemble de tout ce qui venait de se passer.
15 Sai ya zama da cewa, sa'adda su ke tattaunawa tare da tambayoyi, sai Yesu da kansa ya matsa kusa yana tafiya tare da su.
Tandis qu'ils s'entretenaient ainsi et discutaient, Jésus lui-même s'approcha et se mit à marcher avec eux.
16 Amma idanunsu basu iya ganewa da shi ba.
Mais une force empêchait leurs yeux de le reconnaître.
17 Yesu ya ce masu, “Menene ku ke magana akai sa'adda ku ke tafiya?” Suka tsaya a wurin suna bakin ciki.
«Quelles sont, leur dit-il, ces paroles que vous échangez l'un et l'autre tout en marchant?» Ils étaient pleins de tristesse
18 Daya daga cikinsu, mai suna Kiliyobas, ya amsa masa, “Kai ne kadai mutumin da ke Urushalima wanda bai san abubuwan da suka faru a can a wannan kwanakin ba?”
et l'un d'eux, appelé Cléopas, lui répondit. «Tu es bien seul, lui dit-il, et bien étranger à Jérusalem si tu ne sais pas ce qui y est arrivé ces jours-ci.» —
19 Yesu ya ce masu, “Wadanne abubuwa?” Suka amsa masa, “Abubuwa game da Yesu ba Nazarat, wanda ya ke annabi ne, mai manyan ayuka da kalmomi daga Allah da kuma mutane.
«Quoi donc?», leur demanda-t-il. Ils lui répondirent: «L'affaire de Jésus de Nazareth qui fut un prophète puissant en oeuvres et en paroles devant Dieu et devant tout le peuple.
20 Da yadda manyan firistoci da masu mulkinmu suka bada shi domin a hukunta shi ga mutuwa a kuma giciye shi.
Les chefs des prêtres et nos magistrats l'ont livré pour le faire condamner à mort et l'ont crucifié.
21 Amma mun yi begen cewa shine wanda za ya yantar da Isra'ila. I, bayan wannan kuma, yanzu kwana uku kenan tunda wadannan abubuwan suka faru.
Nous, nous espérions qu'il était celui qui doit délivrer Israël. Mais, avec tout cela, voici le troisième jour que ces choses sont arrivées!»
22 Amma har'ila yau, wadansu mata da ke tare da mu sun yi mana abin al'ajabi, da suka kasance a kabarin tunda sassafe.
«De plus, certaines femmes qui sont des nôtres nous ont fort effrayés. Elles sont allées de grand matin au tombeau
23 Sa'adda ba su sami jikinsa ba, suka zo, da cewa su ma sun ga wahayin mala'iku wadanda suka ce masu ya na da rai.
et n'y ont pas trouvé son corps; et elles sont venues nous dire qu'elles ont même vu une apparition d'anges. Ces anges leur ont dit qu'il est vivant.
24 Wasu maza wadanda ke tare da mu suka tafi kabarin, suka tarar da shi kamar yadda matan suka fada. Amma ba su ganshi ba.”
Alors quelques-uns des nôtres sont allés au tombeau; ils ont trouvé toutes choses comme les femmes avaient dit; mais, lui, ils ne l'ont pas vu.»
25 Yesu ya ce masu, “Ku mutane masu wauta da marasa ba da gaskiya ga abin da annabawa suka fada!
«Ô insensés! leur dit-il alors, coeurs lents à croire tout ce qu'ont dit les prophètes?
26 Bai zama dole ne Almasihu ya sha wahalan wadannan abubuwan ba, ya kuma shiga cikin daukakarsa?”
Ne fallait-il pas que le Christ souffrît ces choses et entrât dans sa gloire?
27 Sa'annan da farko daga Musa da har zuwa dukan annabawa, Yesu ya fasara masu duka abubuwa da ke game da kansa a dukan littattafai.
Et commençant par Moïse et par tous les Prophètes, il leur expliquait dans toutes les Écritures ce qui le concernait.
28 Da suka yi kusa da kauyen, inda suke tafiya, ko da yake Yesu ya yi kamar zai wuce su.
Ils approchaient du village où ils se rendaient et lui faisait semblant d'aller plus loin.
29 Amma suka tilasta shi, cewa, “Ka zauna da mu, gama yamma ta yi kusa rana kuma ta kusa karewa.” Sai Yesu ya tafi ya zauna da su.
Mais ils le retinrent. «Demeure avec nous, lui dirent-ils, car il se fait tard; le jour est déjà sur son déclin.» entra pour demeurer avec eux.
30 Ya faru cewa, sa'adda ya zauna tare da su domin ya ci abinci, sai ya dauki gurasan, ya albarkace shi, ya kakkarya, sai ya ba su.
Comme ils étaient ensemble à table, il prit le pain, prononça la bénédiction, le rompit et le leur donna.
31 Sa'annan idanunsu suka bude, da suka gane shi, sai ya bace daga garesu,
Leurs yeux s'ouvrirent, et ils le reconnurent, mais lui-même avait disparu de devant eux.
32 Suka ce wa junansu, ashe zuciyarmu ba ta yi kuna a cikinmu ba, sa'adda yake magana da mu a hanya, sa'adda ya bude mana littattafai?”
«N'est-ce pas, se dirent-ils l'un à l'autre, que notre coeur était tout enflammé en nous-mêmes, lorsqu'il nous parlait dans le chemin et qu'il nous ouvrait le sens des Écritures.»
33 Suka tashi a wancan sa'a, sai suka koma Urushalima. Suka sami sha dayan nan tare, da wadanda suke tare da su,
Ils se levèrent à l'heure même, retournèrent à Jérusalem et trouvèrent réunis les onze et ceux qui étaient des leurs;
34 cewa, “Lalle ne Ubangiji ya tashi, ya kuma bayyana ga Siman.”
ceux-ci leur dirent: «Le Seigneur est vraiment ressuscité et il est apparu à Simon.»
35 Sai suka fadi abubuwan da suka faru a hanya, da yadda aka bayyana masu Yesu sa'adda ya kakkarya gurasa.
Quant à eux, ils racontèrent ce qui s'était passé dans le chemin, et comment ils l'avaient reconnu à la fraction du pain.
36 Sa'adda suke fadin wadannan abubuwan, sai Yesu ya tsaya a sakaninsu, sai ya ce masu, “Salama a gareku.”
Pendant qu'ils parlaient, Jésus parut au milieu d'eux et leur dit: «La paix soit avec vous!»
37 Amma suka firgita suna cike da tsoro, suna tsammani sun ga fatalwa.
Troublés, épouvantés, ils croyaient voir un Esprit.
38 Yesu ya ce masu, don me ku ke damuwa? Don me tambayoyi ke tasowa a zuciyarku?
«Pourquoi vous troublez-vous, leur dit-il, et pourquoi ces hésitations qui montent dans vos coeurs?
39 Duba hannayena da kafafuna, cewa nine da kaina. Taba ni ku gani. Gama ruhu ba shi da jiki da kashi, kamar yadda ku ka ga nake da su.”
Voyez mes mains et mes pieds, c'est bien moi. Touchez-moi; regardez-moi; un Esprit n'a ni chair ni os comme vous voyez que j'en ai».
40 Bayan da ya fadi wannan, sai ya nuna masu hannayensa da kafafunsa.
(En leur disant cela, il leur montra ses mains et ses pieds.)
41 Sa'adda suke cike da farin ciki, da mamaki, Yesu ya ce masu, “Kuna da wani abinci?”
Comme dans leur stupéfaction et leur joie ils ne croyaient point encore, il leur demanda: «Avez-vous ici quelque chose à manger?»
42 Sai suka bashi gasasshen kifi.
Ils lui présentèrent un morceau de poisson grillé.
43 Yesu ya karba, ya ci a gabansu.
Il le prit et le mangea devant eux.
44 Sai ya ce masu, “Sa'adda nake tare da ku na gaya maku cewa duka abin da aka rubuta a cikin dokokin Musa da na annabawa da Zabura dole su cika.”
Il ajouta: «Voilà ce que je vous disais quand j'étais encore avec vous et vous parlais. Je vous disais qu'il fallait que fût accompli tout ce qui est écrit de moi dans la Loi de Moïse, dans les Prophètes et dans les Psaumes.»
45 Sai ya bude hankalinsu, saboda su gane littattafai.
Et là-dessus il leur ouvrit l'intelligence pour qu'ils comprissent les Écritures.
46 Ya ce masu, “A rubuce yake, cewa Almasihu za ya sha wuya, zai tashi kuma daga matattu a rana ta uku.
«C'est ainsi, leur dit-il, qu'il est écrit que le Christ souffrira et ressuscitera d'entre les morts le troisième jour,
47 Ku yi wa'azin tuba da gafarar zunubai a cikin sunansa ga dukan al'ummai, ku fara daga Urushalima.
et que la repentance et la rémission des péchés seront prêchées en son nom parmi toutes les nations, à commencer par Jérusalem.
48 Ku shaidu ne ga wadannan abubuwan.
Vous, vous êtes témoins de ces choses.
49 Duba, ina aiko da alkawarin Ubana a kanku. Amma ku jira a birni, sai an suturta ku da iko daga sama.”
Et moi, j'enverrai sur vous ce que mon Père a promis. Vous demeurerez donc dans la ville, jusqu'à ce que vous ayez été revêtus d'une force d'en haut.»
50 Sa'annan Yesu ya tafi tare da su har sai da suka kai kusa da Betanya. Sai ya daga hannunsa ya albarkace su.
Puis il les emmena jusque vers Béthanie et, levant les mains, il les bénit.
51 Ya zama sa'adda yake sa masu albarka, ya bar su sai aka dauke shi zuwa cikin sama.
Et, tandis qu'il les bénissait, il se sépara d'eux et fut élevé au ciel.
52 Sai suka yi masa sujada, suka komo Urushalima da murna mai yawa.
Ils tombèrent en adoration, puis, le coeur plein de joie, ils retournèrent à Jérusalem,
53 Kullayaumin suna cikin haikali, suna albarkatar Allah.
où ils étaient constamment dans le Temple, bénissant Dieu.

< Luka 24 >