< Luka 24 >

1 Da sassafe a ranar farko ta mako, suka zo kabarin, suka kawo kayan kamshi wadda suka shirya.
Le jour du sabbat, elles se reposèrent, selon le commandement; mais, le premier jour de la semaine, à l'aube, elles se rendirent au tombeau, portant les aromates qu'elles avaient préparés.
2 Sai suka samu dutsen a mirgine shi daga kabarin.
Elles trouvèrent qu'on avait roulé la pierre loin du sépulcre,
3 Suka shiga ciki, amma ba su sami jikin Ubangiji Yesu ba.
et, étant entrées, elles ne trouvèrent point le corps du Seigneur Jésus.
4 Ya faru kuwa, yayin da suke a rikice game da wannan, ba zato, mutane guda biyu suka tsaya a gabansu da tufafi masu walkiya.
Elles ne savaient qu'en penser, lorsque leur apparurent deux hommes vêtus d'habits d'une éclatante blancheur.
5 Sa'adda matan suka sunkuyar da kansu kasa domin tsoro, suka ce wa matan, “Don me kuke neman mai rai ciki matattatu?
Comme elles étaient saisies de frayeur, et qu'elles baissaient la tête vers la terre, ils leur dirent: «Pourquoi cherchez-vous parmi les morts celui qui est vivant?
6 Baya nan, amma ya tashi! Ku tuna fa yadda ya yi maku magana tun sa'adda ya ke Galili,
Il n'est point ici, mais il est ressuscité. Rappelez- vous la manière dont il vous a parlé, quand, étant encore en Galilée,
7 cewa za a ba da Dan Mutum ga mutane masu zunubi su kuma giciye shi, a rana ta uku, zai tashi kuma”
il vous disait qu'il fallait que le Fils de l'homme fût livré entre les mains des pécheurs, qu'il fût crucifié, et qu'il ressuscitât le troisième jour.»
8 Sai matan suka tuna da kalmominsa,
Alors, elles se ressouvinrent des paroles de Jésus,
9 suka koma daga kabarin sai suka gaya wa sha dayan wadannan abubuwan da dukan sauran.
et, à leur retour du sépulcre, elles rapportèrent toutes ces choses aux Onze et à tous les autres disciples.
10 Su Maryamu Magadaliya, Yuwana, Maryamu uwar Yakubu, da sauran matan da ke tare da su suka ba manzanni rohoton wadannan abubuwan.
Celles qui leur firent ce rapport, étaient Marie Madeleine, Jeanne, Marie, mère de Jacques, et les autres femmes qui étaient avec elles;
11 Amma manzannin suka dauki maganar kamar ba ta da amfani, kuma ba su bada gaskiya ga matan ba.
mais les apôtres ne virent dans ce rapport que des rêveries et ne crurent point ces femmes.
12 Duk da haka Bitrus ya tashi, sai ya gudu zuwa kabarin, ya sunkuya yana kallon ciki, sai ya gan likaftani linin kadai. Sa'annan Bitrus ya tafi gidansa, yana ta mamakin abinda ya faru.
[Toutefois Pierre se leva, courut au sépulcre, et, s'étant baissé, il vit les bandes qui étaient à terre, toutes seules, et s'en retourna chez lui, surpris de ce qui était arrivé.]
13 A ranan nan, sai ga biyu daga cikinsu suna tafiya zuwa wani kauye suna Imawus, wanda nisansa kimanin mil ne daga Urushalima.
Ce même jour, deux disciples allaient dans un village nommé Emmaüs, éloigné de Jérusalem de soixante stades;
14 Suna tattaunawa da junansu game da dukan abubuwan da suka faru.
et ils s'entretenaient de tous ces événements.
15 Sai ya zama da cewa, sa'adda su ke tattaunawa tare da tambayoyi, sai Yesu da kansa ya matsa kusa yana tafiya tare da su.
Pendant qu'ils parlaient et discutaient, Jésus lui-même s'approcha, et fit route avec eux.
16 Amma idanunsu basu iya ganewa da shi ba.
Mais ils avaient comme un bandeau sur les yeux, de sorte qu'ils ne le reconnurent point.
17 Yesu ya ce masu, “Menene ku ke magana akai sa'adda ku ke tafiya?” Suka tsaya a wurin suna bakin ciki.
Il leur dit: «De quoi vous entretenez-vous chemin faisant?... et vous êtes tout tristes.»
18 Daya daga cikinsu, mai suna Kiliyobas, ya amsa masa, “Kai ne kadai mutumin da ke Urushalima wanda bai san abubuwan da suka faru a can a wannan kwanakin ba?”
L'un d'eux, qui s'appelait Cléopas, lui répondit: «Tu es bien le seul dans Jérusalem, qui ne sache pas ce qui s'est passé ces derniers jours.»
19 Yesu ya ce masu, “Wadanne abubuwa?” Suka amsa masa, “Abubuwa game da Yesu ba Nazarat, wanda ya ke annabi ne, mai manyan ayuka da kalmomi daga Allah da kuma mutane.
— «Et quoi?» leur dit-il. Ils lui répondirent: «Ce qui est arrivé à Jésus de Nazareth, qui était un prophète puissant en oeuvres et en paroles, devant Dieu et devant tout le peuple:
20 Da yadda manyan firistoci da masu mulkinmu suka bada shi domin a hukunta shi ga mutuwa a kuma giciye shi.
comment nos principaux sacrificateurs et nos sénateurs l'ont livré pour être condamné à mort, et l'ont crucifié.
21 Amma mun yi begen cewa shine wanda za ya yantar da Isra'ila. I, bayan wannan kuma, yanzu kwana uku kenan tunda wadannan abubuwan suka faru.
Pour nous, nous espérions que ce serait lui qui délivrerait Israël; mais, après tout cela, voici le troisième jour, aujourd'hui, que ces événements se sont passés.
22 Amma har'ila yau, wadansu mata da ke tare da mu sun yi mana abin al'ajabi, da suka kasance a kabarin tunda sassafe.
Il est vrai que des femmes qui sont avec nous, nous ont extraordinairement surpris: elles s'étaient rendues au point du jour au sépulcre,
23 Sa'adda ba su sami jikinsa ba, suka zo, da cewa su ma sun ga wahayin mala'iku wadanda suka ce masu ya na da rai.
et, n'ayant point trouvé son corps, elles sont venues dire que des anges leur sont apparus, et qu'ils le disent vivant.
24 Wasu maza wadanda ke tare da mu suka tafi kabarin, suka tarar da shi kamar yadda matan suka fada. Amma ba su ganshi ba.”
Quelques-uns des nôtres sont allés au sépulcre, ils ont trouvé toutes choses comme les femmes l’avaient annoncé; mais lui, ils ne l’ont pas vu.»
25 Yesu ya ce masu, “Ku mutane masu wauta da marasa ba da gaskiya ga abin da annabawa suka fada!
Alors il leur dit: «Hommes dépourvus de sens, esprits lents à croire tout ce qu'ont dit les prophètes!
26 Bai zama dole ne Almasihu ya sha wahalan wadannan abubuwan ba, ya kuma shiga cikin daukakarsa?”
Ne fallait-il pas que le Messie passât par ces souffrances pour entrer dans sa gloire?»
27 Sa'annan da farko daga Musa da har zuwa dukan annabawa, Yesu ya fasara masu duka abubuwa da ke game da kansa a dukan littattafai.
Puis, commençant par Moïse, et poursuivant par tous les prophètes, il leur expliqua, dans toutes les Ecritures, ce qui le concernait.
28 Da suka yi kusa da kauyen, inda suke tafiya, ko da yake Yesu ya yi kamar zai wuce su.
Cependant ils approchèrent du village où ils se rendaient, et comme l’étranger paraissait vouloir aller plus loin,
29 Amma suka tilasta shi, cewa, “Ka zauna da mu, gama yamma ta yi kusa rana kuma ta kusa karewa.” Sai Yesu ya tafi ya zauna da su.
ils le pressèrent de s'arrêter, disant: «Reste avec nous; car voici le soir, et le jour a déjà baissé; »et il entra dans le village pour rester avec eux.
30 Ya faru cewa, sa'adda ya zauna tare da su domin ya ci abinci, sai ya dauki gurasan, ya albarkace shi, ya kakkarya, sai ya ba su.
Quand il se mit à table avec eux, il prit le pain, et ayant prononcé la bénédiction, il le rompit, et le leur donna:
31 Sa'annan idanunsu suka bude, da suka gane shi, sai ya bace daga garesu,
alors leurs yeux se dessillèrent; ils le reconnurent; mais il disparut de devant leurs yeux.
32 Suka ce wa junansu, ashe zuciyarmu ba ta yi kuna a cikinmu ba, sa'adda yake magana da mu a hanya, sa'adda ya bude mana littattafai?”
Ils se dirent l'un à l'autre: «Notre coeur n'était-il pas tout brûlant au dedans de nous, lorsqu'il nous parlait en chemin, et qu'il nous expliquait les Écritures?»
33 Suka tashi a wancan sa'a, sai suka koma Urushalima. Suka sami sha dayan nan tare, da wadanda suke tare da su,
Et, se levant à l'heure même, ils retournèrent à Jérusalem. Ils trouvèrent réunis les Onze et leurs compagnons,
34 cewa, “Lalle ne Ubangiji ya tashi, ya kuma bayyana ga Siman.”
qui leur dirent: «Le Seigneur est réellement ressuscité, et il est apparu à Simon.»
35 Sai suka fadi abubuwan da suka faru a hanya, da yadda aka bayyana masu Yesu sa'adda ya kakkarya gurasa.
Ils racontèrent à leur tour, ce qui leur était arrivé en chemin, et comment ils l'avaient reconnu au moment où il avait rompu le pain.
36 Sa'adda suke fadin wadannan abubuwan, sai Yesu ya tsaya a sakaninsu, sai ya ce masu, “Salama a gareku.”
Pendant qu'ils s'entretenaient ainsi, lui-même parut au milieu d'eux.
37 Amma suka firgita suna cike da tsoro, suna tsammani sun ga fatalwa.
Frappés de stupeur et d'effroi, ils crurent voir un esprit;
38 Yesu ya ce masu, don me ku ke damuwa? Don me tambayoyi ke tasowa a zuciyarku?
et Jésus leur dit: «Pourquoi êtes-vous troublés? Pourquoi vous faites-vous des idées folles?
39 Duba hannayena da kafafuna, cewa nine da kaina. Taba ni ku gani. Gama ruhu ba shi da jiki da kashi, kamar yadda ku ka ga nake da su.”
Voyez mes mains et mes pieds: c'est bien moi. Palpez-moi, et considérez qu'un esprit n'a ni chair ni os, comme vous voyez que j'en ai.»
40 Bayan da ya fadi wannan, sai ya nuna masu hannayensa da kafafunsa.
[Après avoir ainsi parlé, il leur montra ses mains et ses pieds.]
41 Sa'adda suke cike da farin ciki, da mamaki, Yesu ya ce masu, “Kuna da wani abinci?”
Comme la joie les rendait encore incrédules, et qu'ils ne revenaient pas de leur surprise, il leur dit: «Avez-vous ici quelque chose à manger?»
42 Sai suka bashi gasasshen kifi.
Ils lui présentèrent un morceau de poisson rôti et un rayon de miel.
43 Yesu ya karba, ya ci a gabansu.
Il les prit, et les mangea devant eux.
44 Sai ya ce masu, “Sa'adda nake tare da ku na gaya maku cewa duka abin da aka rubuta a cikin dokokin Musa da na annabawa da Zabura dole su cika.”
Puis il leur, dit: «C'est là ce que je vous annonçais quand j'étais encore avec vous; je vous disais qu'il fallait que s'accomplit tout ce qui est écrit de moi dans la Loi de Moïse, dans les Prophètes et dans les Psaumes.»
45 Sai ya bude hankalinsu, saboda su gane littattafai.
Alors il leur ouvrit l'esprit, afin qu'ils entendissent les Ecritures.
46 Ya ce masu, “A rubuce yake, cewa Almasihu za ya sha wuya, zai tashi kuma daga matattu a rana ta uku.
Et il leur dit: «C'est ainsi qu'il est écrit que le Messie souffrirait, et qu'il ressusciterait des morts le troisième jour,
47 Ku yi wa'azin tuba da gafarar zunubai a cikin sunansa ga dukan al'ummai, ku fara daga Urushalima.
et qu'on prêcherait en son nom la repentance et le pardon des péchés à toutes les nations, en commençant par Jérusalem.
48 Ku shaidu ne ga wadannan abubuwan.
Vous êtes témoins de ces faits.
49 Duba, ina aiko da alkawarin Ubana a kanku. Amma ku jira a birni, sai an suturta ku da iko daga sama.”
Maintenant, je vais vous envoyer ce que mon Père vous a promis; pour vous, demeurez tranquillement dans la ville, jusqu'à ce que vous soyez revêtus d'une puissance qui vient d'en haut.»
50 Sa'annan Yesu ya tafi tare da su har sai da suka kai kusa da Betanya. Sai ya daga hannunsa ya albarkace su.
Il les emmena hors de la ville, jusqu’à Béthanie; et, élevant les mains, il les bénit.
51 Ya zama sa'adda yake sa masu albarka, ya bar su sai aka dauke shi zuwa cikin sama.
Pendant qu'il les bénissait, il se sépara d'eux.
52 Sai suka yi masa sujada, suka komo Urushalima da murna mai yawa.
Pour eux, ils s'en retournèrent à Jérusalem, pleins d'une grande joie;
53 Kullayaumin suna cikin haikali, suna albarkatar Allah.
et ils étaient continuellement dans le temple, louant et bénissant Dieu.

< Luka 24 >